Jameel Online Media Tv

Jameel Online Media Tv Trusted News | Islamic | Education | Entertainment | Sports | More

🚨 GWARZUWAR HIZB 60 DAGA ƘASAR GHANA.•Wannan itace Allah ya bata nasarar samun lamba ta ɗaya a haddan HIZB 60 a Musabaqa...
24/08/2026

🚨 GWARZUWAR HIZB 60 DAGA ƘASAR GHANA.

•Wannan itace Allah ya bata nasarar samun lamba ta ɗaya a haddan HIZB 60 a Musabaqar Duniya da aka gudanar a ƙasar Saudiyya kuma 'yar Ghana ce.

•Allah ya yiwa yankin Afrika baiwar Al-Qur'ani, ta yadda suke iya zuwa cikin larabawan da aka saukar da Al-Qur'ani da yaren su amma kuma su iya samun nasara akan su tare da taimakon Ubangiji.

•Ɗazu na ɗan bi ta kan wani rubutu da wani juyayye mai ƙaramin fahimta yayi akan yadda 'yan Nigeria da 'yan Afrika suke samun nasara a Musabaqar Duniya, yana nuna cewar ana basu ne don a ƙarfafe su amma ba wai don ƙoƙarin su yakai ba.

•To kunga shi wannan ba'a kallon sa ballantana a saurari maganar sa, domin Al-Qur'ani an saukar dashi ne kawai da harshen Larabci amma ba larabawa bane kaɗai aka saukarwa dashi ba, saboda haka kowa zai iya koyon sa kuma ya ƙware acikin sa koda ko ba balarabe bane, haka kuma za'a iya samun balaraben da bazai iya karantawa ba duk da cewar da yaren nasu aka saukar dashi.

Allah ya ƙara mana Ni'imar Al-Qur'ani kuma yasa yayi mana jagora zuwa Aljannah Amin.

🚨SHINE NA BIYAR A MATAKIN TAFSIR NA DUNIYA GABA DAYA.•Goni Muhammad ya samu daraja ta BIYAR a Musabaqar Duniya ta aka ga...
21/08/2026

🚨SHINE NA BIYAR A MATAKIN TAFSIR NA DUNIYA GABA DAYA.

•Goni Muhammad ya samu daraja ta BIYAR a Musabaqar Duniya ta aka gabatar a kasar Saudiyya a matakin Hibz 60 da Tafsir.

•Yau ina cikin farin ciki marar misaltuwa, nasarar wadannan bayin Allah ba tasu bace su kadai, nasara ce da ta shafe duk wani dan Nigeria.

Allah ya karawa rayuwar su da tamu Albarka Amin.

20/08/2026

Shout out to my newest followers! Excited to have you onboard! Bilkisu Muhammad, Muhammad Bello, Aliyu Suleiman, Ibrahim Bello Ibrahim, Yunussa Haruna, Harira Nasiru, Muhermmad Sernee Muhermmad, Oummoul Khaeree

Gombawa Diban Fari!Gwarazaa Yaya Da ƘanwaYan Gida daya da s**a yi fice a Musabaƙar karatun Alqur'ani a matakin Duniya ga...
20/08/2026

Gombawa Diban Fari!

Gwarazaa Yaya Da Ƙanwa

Yan Gida daya da s**a yi fice a Musabaƙar karatun Alqur'ani a matakin Duniya gaba daya yan asalin jihar Gombe. Daga makarantar Abubakar Siddiq Islamiyya School Gombe.

A shekarar 2023 Hajara Ibrahim daga Jihar Gombe ta wakilci Najeriya a Musabaƙar karatun Alƙur’ani mai girma ta mata da aka gudanar a ƙasar Jordan, inda ƙasashe kusan 40 s**a fafata, kuma ta samu matsayi na daya.

A lokacin ta samu kyautar Naira miliyan 5. Da Tallafin karatu (Scholarship)

Da Kyautar Naira miliyan 5 ga makarantar da ta yi karatu, Abubakar Siddiq Islamiyya School Gombe. Da Kujerar aikin Hajji daga National Hajj Commission.

Yau kuma an wayi gari, ƙanwarta Maryam itama ta lashe gasar Al-Qur'ani mai girma ta Duniya karo na 46 a Masarautar Saudiyya ta shekarar 2026.

A sashen Tafsiri na mata, inda ta samu kyautar Riyal 300,000 na Saudiyya, wanda ya yi daidai da kimanin ₦120,000,000 (Naira Miliyan 120) a kuɗin Najeriya.

Abin da ya fi burgewa shi ne, a fannin karatun boko ma ba a bar su a baya ba.

Hajara Ibrahim Ɗan’Azumi, ta karanci Botany, kuma ta kammala karatunta.

Maryam Ibrahim Ɗan’Azumi, tana shekara ta ƙarshe (Final Year) a fannin Education Physics.

Mutum idan ya sami Alqur'ani ba abinda zai gagara in sha Allah matuƙar aka kyautata niyya.

Barakallahu feekum

Alhamdulillah, Madallah da wannan zuri'a Allah ya ƙarama karatu Albarka.

Nigeria Munfi kowa yin Nasara 🇳🇬🌎✊| category Guda Daya Sune Sukayi Nasara 🇳🇬🔥 Hizb 60 (tafsiri) gwani Muhammad ASIL 5th ...
20/08/2026

Nigeria Munfi kowa yin Nasara 🇳🇬🌎✊| category Guda Daya Sune Sukayi Nasara 🇳🇬🔥 Hizb 60 (tafsiri) gwani Muhammad ASIL 5th position 🏆 gwana Maryam Ibrahim dan azumi 1st position 🏆 , Wannan Category Shine Babban Category Cikin Musabaqar Baki daya Kuma Cikinsa Aka Samu Gwarzuwa Tayo Na daya Kuma cikinsa Aka Samu gwarzo Wanda Yayi Na biyar ALHAMDULILLAH 👏 Yan Nigeria 🇳🇬 Allah Ya Bamu Baiwa Muyi Amfani Da Baiwarmu Domin kawoma Nigeria 🇳🇬 Ci gaba Allah Ya Kawo Mana Ƙarshen Matsalolin Kasarmu 🤲🤲😥

14/08/2026
Alhmadulh Hafiz Imran Musa Kenn Daga kasar saudiya tare Da Sheikh Yasser Al-Dosari.Allah yayi ma rayuwa Albarka 🤲
11/08/2026

Alhmadulh
Hafiz Imran Musa Kenn
Daga kasar saudiya tare Da Sheikh Yasser Al-Dosari.

Allah yayi ma rayuwa Albarka 🤲

11/08/2026

Shout out to my newest followers! Excited to have you onboard! Adam Abdullahi Muhammad, Mujahiddeen Mustapha Adam, Hafeez Polchi

11/08/2026

Allah Ka Tabbatar Mana Da Nasara 🤲

A Gobe ne in sha Allah Gwarzuwa Maryam Ibrahim Dan Azumi Zata tafi kasar Saudiyya domin wakiltar Kasarmu Nigeria a Gasar...
05/08/2026

A Gobe ne in sha Allah Gwarzuwa Maryam Ibrahim Dan Azumi Zata tafi kasar Saudiyya domin wakiltar Kasarmu Nigeria a Gasar Musabaqar Alqur'ani ta Duniya bangaren mata.

Wannan Musabaqar za'a gudanar da ita ne a cikin garin Makka cikin Masallacin Harami kuma wannan shine karo na farko da za'a fara gudanar da wannan Musabaqar ta bangaren mata.

Muna buqatar yan uwa ku saka ta a addu'ah Ubangiji ya tabbatar mata da nasara 🙏🙏

Address

Gombe

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Jameel Online Media Tv posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Shortcuts

Share

Category