Ck TV

Ck TV CK Media Service – Labarai na Gaskiya, Don Jama’a.

Birtaniya ta amince da Falasɗinu a matsayin ƙasa mai ‘yanciFiraministan Birtaniya, Keir Starmer, ya tabbatar da amincewa...
21/09/2025

Birtaniya ta amince da Falasɗinu a matsayin ƙasa mai ‘yanci

Firaministan Birtaniya, Keir Starmer, ya tabbatar da amincewar ƙasarsa da Falasɗinu a matsayin ƙasa mai cin gashin kai daga yau Lahadi.

Me ya sa wannan ya zama tarihi?
Birtaniya (United Kingdom) ba England kaɗai bace. Ƙasa ce da ta haɗu da ƙasashe huɗu: England, Scotland, Wales da Northern Ireland.
Matakin yana nufin duka ƙasar UK ta ɗauki wannan matsaya, ba England kaɗai ba.

Starmer ya ce wannan ba goyon bayan Hamas ba ne, illa dai ƙoƙari na farfado da tsarin zaman lafiya na ƙasashe biyu.

Hon. Abubakar Usman Gora ya bayyana cewa, al’ummar Jihar Zamfara ba su da wani zabi mafi cancanta da ya dace da shugaban...
21/09/2025

Hon. Abubakar Usman Gora ya bayyana cewa, al’ummar Jihar Zamfara ba su da wani zabi mafi cancanta da ya dace da shugabanci a shekarar 2027, face Sanata Kabiru Garba Marafa.

Ya ce Marafa ya dade yana tsayawa tsayin daka wajen kare muradun talakawa, tare da nuna kwarewa da cancanta a harkokin shugabanci. Gora ya kara da cewa, lokaci ya yi da mutanen Zamfara za su hada kai domin tabbatar da nasarar Marafa a matsayin gwamnan jihar a zaben 2027.

Me zaku ce?

Jami’ar European-American University (EAU) ta nesanta kanta daga ikirarin cewa ta karrama fitaccen mawakin siyasa, Dauda...
21/09/2025

Jami’ar European-American University (EAU) ta nesanta kanta daga ikirarin cewa ta karrama fitaccen mawakin siyasa, Dauda Kahutu Rarara, da digirin girmamawa.

A wata sanarwa da jami’ar ta wallafa a shafinta na yanar gizo, ta bayyana lamarin a matsayin damfara da aka shirya ba tare da saninta ko amincewarta ba.

“Jami’ar ba ta da hannu a wannan abu, ba mu ba da izinin gudanar da wannan biki ba, kuma ba mu amince da sunayen da aka ce mun bai wa digiri ba,” in ji jami’ar.

Sanarwar ta kara da cewa jami’ar ba za ta lamunci amfani da sunanta wajen damfarar jama’a ba, tare da gargadin mutane da su rika tantance sahihancin bayanai kafin daukar su da muhimmanci.

Wannan na zuwa ne bayan yaɗuwar rahotannin cewa Rarara ya samu digirin girmamawa na Doctorate daga jami’ar, lamarin da yanzu ta bayyana a matsayin karya.

MUHAWARA; Wane dan Siyasa ne ya cancanci Wannan lakabi a Nigeria??
21/09/2025

MUHAWARA; Wane dan Siyasa ne ya cancanci Wannan lakabi a Nigeria??

Ansake zaman sasancin da Yan bindiga a jahar katsina domin samar da zama lafiya.Sai dai al'umma na tofa albarkacin bakin...
20/09/2025

Ansake zaman sasancin da Yan bindiga a jahar katsina domin samar da zama lafiya.

Sai dai al'umma na tofa albarkacin bakinsu ganin yanda ake barin Yan ta'addan da akayi sasanci dasu su koma daji da Makamansu!

Me kuke ganin ya dace ayi domin kawo karshen matsalar tsaro??

Shugaban ƙungiyar, Abdulmalik sai'du maibiredi ya ce wannan mota za ta taimaka wajen sauƙaƙa jigilar aiki, bin diddigin ...
20/09/2025

Shugaban ƙungiyar, Abdulmalik sai'du maibiredi ya ce wannan mota za ta taimaka wajen sauƙaƙa jigilar aiki, bin diddigin abubuwan da ke faruwa da kuma isar da labarai cikin lokaci ga al’umma.

Ya gode wa mambobin ƙungiyar bisa haɗin kai da jajircewar da ya kai ga cimma wannan nasara.

A wani rahoton bincike da Omoyele Sowore ya gudanar Ya bayyana cewa gidajen da tsohon gwamnan Rivers kuma Ministan Abuja...
20/09/2025

A wani rahoton bincike da Omoyele Sowore ya gudanar Ya bayyana cewa gidajen da tsohon gwamnan Rivers kuma Ministan Abuja, Nyesom Wike, ya mallaka a Amurka sun kai darajar Naira biliyan 3.
An saya gidajen ne da sunan matar sa da ’ya’yansa, lamarin da ya tayar da tambaya: daga ina aka samo kuɗin?

European-American University (EAU) ta karrama fitaccen mawakin siyasa na Najeriya, Dauda Kahutu Rarara, da digirin girma...
20/09/2025

European-American University (EAU) ta karrama fitaccen mawakin siyasa na Najeriya, Dauda Kahutu Rarara, da digirin girmamawa na Doctorate (Dr.) a matsayin yabo da girmamawa bisa rawar da ya taka a fagen waka da al’adu.

Me zaku Ce?
Shin Rarara ya cancanci Wannan karramawa??

Ficewar tasa ta biyo bayan matakin da jagoransa, Sanata Kabir Garba Marafa (CON) ya dauka na barin APC a kwanakin baya, ...
20/09/2025

Ficewar tasa ta biyo bayan matakin da jagoransa, Sanata Kabir Garba Marafa (CON) ya dauka na barin APC a kwanakin baya, saboda gazawar gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu wajen cika alƙawuran yakin neman zabe.

Wannan mataki ya ƙara jefa siyasar Zamfara cikin sabon salo, kasancewar Marafa da mabiyansa na daga cikin manyan jiga-jigan da ke da tasiri a jam’iyyar APC tun kafuwarta a jihar.

Wannan bayani ya fito ne daga bakin Alhaji Surajo Garba Maikatako, Shugaban Majalisar Ƙoli ta Ƙungiyar Sanata Marafa, a ...
20/09/2025

Wannan bayani ya fito ne daga bakin Alhaji Surajo Garba Maikatako, Shugaban Majalisar Ƙoli ta Ƙungiyar Sanata Marafa, a cikin wata sanarwa da ya rabawa manema labarai a Gusau, yau Juma’a.

Maikatako ya ce, ficewar Sanata Marafa daga APC ya dawo da martaba da karɓuwar siyasar tsohon Sanatan, inda ya jaddada cewa hakan alheri ne wajen tsara sabuwar tafiya a harkokin siyasa.

Ya kuma tuna da furucin da Marafa ya yi a baya, inda ya bayyana da ƙarfi cewa za su cire kasa da ƙuri’u miliyan ɗaya daga ƙididdigar da Shugaba Tinubu zai samu a zaɓe mai zuwa.

Address

Tudun Wada Gusau
Gusau
GUS234

Telephone

+2349124457735

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Ck TV posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Ck TV:

Share