Zamfara Online Daily News

Zamfara Online Daily News Zamfara online daily news is new company And also it establish the company to provide us realible news all over the country.

And we are working very hard to avoid the fake news.

DA DUMI DUMI: 2027 Ta Musamman ce Yan Nigeriya, Shugaban ƙasa Bola Tinubu ya bayyana cewa ya fidda Manufofinsa guda 8 wa...
06/07/2025

DA DUMI DUMI: 2027 Ta Musamman ce Yan Nigeriya, Shugaban ƙasa Bola Tinubu ya bayyana cewa ya fidda Manufofinsa guda 8 wanda zai yiwa yan Nigeria idan S**a Sake Zaɓarshi a karo na biyu ya zama shugaban ƙasa a kakar Zaɓe ta 2027

Shugaban ƙasar Nageriya, Asiwaju Bola Ahmed Tinubu ya fidda manufofi ko ƙudirori guda 8 waɗanda ya ke son cimmawa a gwamnatinsa.

Jaridar Wakiliya ta rawaito manufofin guda takwas, ga su nan k**ar haka:

1. Wadata ƙasa da Abinci (Food Security).
2. Kawo ƙarshen Talauci (Ending Poverty).
3. Samar da ayyukan yi da bunƙasa tattalin arziƙi (Eonomic Growth and Job Creation).
4. Bawa ƴan ƙasa damar samun jarin dogaro da kai (Access To Capital).

5. Kyautata tsaron ƙasa (Improving Security).
6. Kyautata sha'anin kasuwanci (Improving The Playing Field on which people and particularly companies operate).
7. Tabbatar da bin doka da ƙa'ida (Rule of Law).
8. Yaƙi da rashawa da cin-hanci (Fighting Corruption

Kana Son Duba Sahihan Labarai Shigo Jaridar 👉 Zamfara Online daily News.👈 Yanzu Yi Following Karku Bari Komai Ya Wuceku...

Jarumi Adam A. Zango Yayi Haɗarin Mota Akan Hanyar Kano Zuwa KadunaDaga Abubakar Shehu DokokiFitaccen Jarumin Masana'ant...
09/06/2025

Jarumi Adam A. Zango Yayi Haɗarin Mota Akan Hanyar Kano Zuwa Kaduna

Daga Abubakar Shehu Dokoki

Fitaccen Jarumin Masana'antar shirya Fina-finai ta Kannywood Adam A. Zango, ya gamu da haɗarin mota akan hanyarsu daga Kaduna Zuwa Kano, wanda hakan ya tada hankalin dayawa daga cikin Masoyansa, dakuma mabiyan Jarumin.

Bayyanar saƙon nuna godiya daga Adam A. Zango bisa addu'o'i da ake masa da kuma fatan alkairi, k**ar yadda ya bayyana a shafinsa na Facebook, hakan ya sanyaya zuciyar da yawa daga cikin masoya Jarumin.

ANYI MUMUNAN HADARIHatsarin Mota ya laƙume rayukan Mutane 16 'Yan asalin Shinkafi ta jahar Zamfara.Wasu matafiya 'yan as...
28/05/2025

ANYI MUMUNAN HADARI

Hatsarin Mota ya laƙume rayukan Mutane 16 'Yan asalin Shinkafi ta jahar Zamfara.

Wasu matafiya 'yan asalin karamar hukumar mulkin Shinkafi sun gamu da hatsarin mota bayan da S**a taso daga Ore kudancin Najeriya Zuwa Shinkafi ta Jahar Zamfara.

Mutane goma Sha shida (16) Sun rigamu gidan Gaskiya ta sanadiyyar Hatsarin motar daya faru da Safiya Jiya lahadi, motar Kirar Homa, ta shige Cikin motar Kamfanin Dangote Kuma Duka motocin S**a k**a da wuta.

Bayanai sun tabbatar da Cewa Yarinya daya kawai ta fita a cikin Karamar motar Inda yanzu Haka take karbar magani a wata Assibiti.

Daga Muktar Elduniya Shinkafi.

YANZU-YANZU: An Ga Hamdiyya Amma A Cikin Mayuwayacin HaliLabarai sun ishe mu cewa Hamdiyya na babban asibitin Bakura jih...
21/05/2025

YANZU-YANZU: An Ga Hamdiyya Amma A Cikin Mayuwayacin Hali

Labarai sun ishe mu cewa Hamdiyya na babban asibitin Bakura jihar Zamfara.

Tana cikin mawuyacin hali. Amma akwai jami’an tsaro a tare da ita. Ya tabbata sace ta aka yi.

Alhamdulillah ala kulli halin., k**ar yadda Lauyanta, Barista Abba Hikima ya bayyana a daren nan.

Daga Rashida Bala Suleja

INNA LILLAHI WA'INNA ILAIJI RAJI'UN: Ta Ràśù Tana Kan Yi Wa Kàsa HìđimaAllah Ya yi ma kawarmu rasuwa sanadiyyar gajeruwa...
26/04/2025

INNA LILLAHI WA'INNA ILAIJI RAJI'UN: Ta Ràśù Tana Kan Yi Wa Kàsa Hìđima

Allah Ya yi ma kawarmu rasuwa sanadiyyar gajeruwar ràśhin lafiya a asibitin Sokoto.

Tare muke yi wa kasa hidima (services) yanzu haka da ita a Sokoto, sai dai Allah bai nufa za mu kare da ita ba.

Duk wanda ke ganina a NYSC Permanent Orientation Camp, Sokoto, yana ganinmu tare da wannan baiwar Allah.

Allah Ya gafarta mata.

Daga Murjanatu Diri

INNALILLAHI WA'INNA ILAIHIR RAJI'UN Allah Ya Yiwa Matashi Usama Mustapha Lanas Ràśùwa Yau A Garin Madina, Matashin Dan A...
11/04/2025

INNALILLAHI WA'INNA ILAIHIR RAJI'UN

Allah Ya Yiwa Matashi Usama Mustapha Lanas Ràśùwa Yau A Garin Madina, Matashin Dan Asalin Jihar Sokoto Ne Kuma Yana Karatu A Kasar Indiya Daga Chan Yaje Aikin Umrah Bana.

Allah ya Gafarta Masa Amin.

https://temu.com/u/W67FcWsWwB3P2d

Dakarun Sojoji Na Musamman Sun K**a 'Yan Ta'adda Yayin Da Suke Kokarin Dasa Bam A Zamfara..Dakarun musamman na Operation...
28/03/2025

Dakarun Sojoji Na Musamman Sun K**a 'Yan Ta'adda Yayin Da Suke Kokarin Dasa Bam A Zamfara..

Dakarun musamman na Operation FANSAN YANMA sun k**a wasu ‘yan ta’adda da suke yunkurin tayar da bama-bamai a wata hanya mai mahimmanci a dajin Gando da ke karamar hukumar Anka a jihar Zamfara.

Wata majiya ta shaida cewa dakarun da ke aiki a karkashin Operation TSAFTA DAJI III Phase 3, sun kai harin kwantan bauna a lokacin da s**a ci karo da wasu gungun ‘yan ta’adda da suke ajiye bama-bamai.

Da ganin dakarun da ke tahowa, ‘yan ta’addan sun gudu zuwa cikin dajin karkashin duhu, inda s**a yi watsi da ababen fashewa da kayan aikinsu.

Kayayyakin da aka kwato sun hada da: Babur daya, jerikan lita 25 guda uku cike da kayan aikin IED, igiyar sapper mai tsawon mita 300, abun fashewar wutar lantarki DET 33 daya da farat daya da ake amfani da su wajen dasa abubuwan fashewa.

Rundunar sojin Najeriya na ci gaba da kai farmaki kan ‘yan ta’adda da masu aikata miyagun laifuka a jihar Zamfara, inda rundunar Operation FANSAN YANMA da Operation TSAFTA DAJI III s**a kai hari a maboyar ‘yan ta’adda a fadin Anka, Bagega, da Bukkuyum.


Daga  Auwal Sani GamboAzumin bara daya wuce, duk wayewar gari sai dan isihu ya kashe mutum, tun farkon fara azumi yakan ...
27/03/2025

Daga Auwal Sani Gambo

Azumin bara daya wuce, duk wayewar gari sai dan isihu ya kashe mutum, tun farkon fara azumi yakan kashe mutum fiye da daya harma yake ikirarin cewa hakan shine matsayin azuminshi.

Dan isihu Yellow yakawo mumunar hari agarin tsafe, yakai sau 2 da safe da kuma dare, wanda yayi sanadiyar mutuwar shugaban askarawa na tsafe LG da sauran yan sakai, hadida wasu daga cikin jami'an tsaro, kari da dadi kusan kullum yana tare hanyar tsafe zuwa yankara yakai sau 1 zuwa 7 a rana.

Dan isihu Yellow kane ne ga ga fitaccen dan bindiga ADO ALERO wanda gwamnati katsina ta bada kwangilar kawoshi araye ko amace da kyautar 5 Million. Kaf din danginsu barayine hatta da babansu Midille, suna zaune a garin YANKUZO, dabarsu na munhaye.

Yau dubunshi tacika, Allah ya isar mana, yakara nauyin kasa, matsiyachi!

Ÿàn Bìñđiga Śùñ Ķàśĥè Matashiya Zarah Yar Asalin Jihar Sokoto Wacce S**ayi Ĝàŕķùŵà Da Ita Tsawon Wata Hudu Bayan Sun Kàŕ...
26/02/2025

Ÿàn Bìñđiga Śùñ Ķàśĥè Matashiya Zarah Yar Asalin Jihar Sokoto Wacce S**ayi Ĝàŕķùŵà Da Ita Tsawon Wata Hudu Bayan Sun Kàŕɓi Kuɗin Fàñśà A Hannun Yan Uwanta.

Ubangiji Allah ya ĵìķàñta da rahma Amin.

Daga Usama Lawal Rabah.

ABIN AL'AJABI: Bayaɲ Aure Da Sati Biyu, Amarya Ta Ráșu Ranar Talata, Baban Ango Ya Râșu Jiya Juma'a, Inda Shi Kuma Ango ...
16/02/2025

ABIN AL'AJABI: Bayaɲ Aure Da Sati Biyu, Amarya Ta Ráșu Ranar Talata, Baban Ango Ya Râșu Jiya Juma'a, Inda Shi Kuma Ango Ya Râșu Yau Asabar

Ikon Allah kenan. Allah Ya gafarta masu.

Daga Ameenu Dauda Pawa

Gwamnan jihar Zamfara Dauda Lawan ya haramta duk wani nau'in taron siyasa a fadin jihar
15/02/2025

Gwamnan jihar Zamfara Dauda Lawan ya haramta duk wani nau'in taron siyasa a fadin jihar

Matawalle ya motsa siyasar jam'iyyar APC a jihar Zamfara ya ma yaba da irin yunkurin da Shugaba Tinubu ke yi na kyautata...
23/12/2024

Matawalle ya motsa siyasar jam'iyyar APC a jihar Zamfara ya ma yaba da irin yunkurin da Shugaba Tinubu ke yi na kyautata rayuwar Zamfarawa

Ministan kasa a ma'aikatar tsaron Nijeriya kuma tsohon gwamnan jihar Zamfara, Dr. Bello Matawalle, ya jaddada mubaya'arsa ga jam'iyyar APC, yayin da ya yaba wa 'ya'yan jam'iyyar bisa jajircewar da suke nunawa a kodayaushe.

A ziyarar kwanaki shida da ya kai jihar Zamfara, Dr Matawalle ya tarbi magoya bayansa a gidansa da ke Gusau, inda ya sanar da bayar da gudunmawar miliyoyin nairori domin karfafa jam’iyyar APC da sauran kungiyoyin kawayenta a jihar.

Ya bayyana gudummawar a matsayin wani bangare na kokarin karfafa tsarin jam’iyyar da kuma tabbatar da ci gaba da samun nasara.

Bugu da kari, Matawalle ya bayyana cewa shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya bayar da gudunmuwa shinkafa mai tarin yawa domin raba wa magoya bayan jam’iyyar APC a fadin jihar Zamfara.

Ya ce an kafa kwamitin da zai sa ido kan yadda ake rabon kayayyakin yadda ya k**ata, ya kara da jaddada goyon bayan shugaban kasa da jiga-jigan jam’iyyar.

Tsohon gwamnan ya jaddada bukatar hadin kai a tsakanin ‘ya’yan jam’iyyar APC, inda ya yi alkawarin ganawa akai-akai da magoya bayansa domin samar da tattaunawa da ci gaba.

Ya kuma bayyana hadin kansa da Sanata Abdul’aziz Yari Abubakar wajen ciyar da ajandar jam’iyyar gaba.

Matawalle ya gode wa shugaban kasa Tinubu kan yadda ya ba da fifiko ga ababen more rayuwa a jihar Zamfara, musamman yadda za a gina titin Zaria-Funtua-Gusau- Sokoto, wanda ya ce tuni aka fara aikin.

Dangane da batun tsaro, Dr. Matawalle ya tabbatar wa mazauna jihar Zamfara kudirin Gwamnatin Tarayya na kawo karshen ‘yan ta'adda.

Ya bayyana cewa, shugaba Tinubu ya amince da sayo kayan aikin soja na zamani, da s**a hada da manyan motocin yaki da jiragen yaki, wadanda tuni s**a iso. Wadannan matakan, in ji shi, suna nuna kwakkwaran kudurin gwamnatin tarayya na maido da zaman lafiya a yankin.

Ziyarar ta Matawalle dai ta kara karfafa alakarsa da al’umma

Address

Gangaren Mai Gemu Tudun Wada Gusau
Gusau

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Zamfara Online Daily News posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Zamfara Online Daily News:

Share