
06/07/2025
DA DUMI DUMI: 2027 Ta Musamman ce Yan Nigeriya, Shugaban ƙasa Bola Tinubu ya bayyana cewa ya fidda Manufofinsa guda 8 wanda zai yiwa yan Nigeria idan S**a Sake Zaɓarshi a karo na biyu ya zama shugaban ƙasa a kakar Zaɓe ta 2027
Shugaban ƙasar Nageriya, Asiwaju Bola Ahmed Tinubu ya fidda manufofi ko ƙudirori guda 8 waɗanda ya ke son cimmawa a gwamnatinsa.
Jaridar Wakiliya ta rawaito manufofin guda takwas, ga su nan k**ar haka:
1. Wadata ƙasa da Abinci (Food Security).
2. Kawo ƙarshen Talauci (Ending Poverty).
3. Samar da ayyukan yi da bunƙasa tattalin arziƙi (Eonomic Growth and Job Creation).
4. Bawa ƴan ƙasa damar samun jarin dogaro da kai (Access To Capital).
5. Kyautata tsaron ƙasa (Improving Security).
6. Kyautata sha'anin kasuwanci (Improving The Playing Field on which people and particularly companies operate).
7. Tabbatar da bin doka da ƙa'ida (Rule of Law).
8. Yaƙi da rashawa da cin-hanci (Fighting Corruption
Kana Son Duba Sahihan Labarai Shigo Jaridar 👉 Zamfara Online daily News.👈 Yanzu Yi Following Karku Bari Komai Ya Wuceku...