Dan kullum online TV

Dan kullum online TV *Shirye muke a ko yaushe domin kawowa masu kallonmu ingantattun shirye - shirye dangane da rayuwa

05/05/2026

Ina Al'ummar Kananan hukumomin Zurmi da Shinkafi ga naku Hon Ahmad A Abubakar ( Dan malikin zurmi)

Mai neman tsayawa takarar kujerar dan majalisar mai wakiltar Kananan hukumomin Zurmi da Shinkafi

Daukar Nauyi:- comrd Mubarak Muhammad Ya'u

SubhanallahWannan bawan Allah sunansa Tukur Aliyu wanda aka fi sani da Jikan Ayi, jiya ya baro Legas ya dawo gida Jikams...
05/05/2026

Subhanallah

Wannan bawan Allah sunansa Tukur Aliyu wanda aka fi sani da Jikan Ayi, jiya ya baro Legas ya dawo gida Jikamshi, yau yana cikin wadanda yan bindiga s**a kashe a harin da s**a kawo garin

Ku roka masa Allah Ya karɓi shahadarsa, Allah Ya gafarta masa

Buhari Zubairu Jikamshi

Ranar ’Yancin ’Yan Jarida ta Duniya: Gwamnatin Nijeriya ta nemi haɗin gwiwa don yaƙi da yaɗa labaran ƙaryaGwamnatin Tara...
04/05/2026

Ranar ’Yancin ’Yan Jarida ta Duniya: Gwamnatin Nijeriya ta nemi haɗin gwiwa don yaƙi da yaɗa labaran ƙarya

Gwamnatin Tarayyar Nijeriya ta buƙaci a ƙara haɗin gwiwa tsakanin kafafen yaɗa labarai, hukumomin gwamnati da sauran masu ruwa da tsaki domin magance barazanar yaɗa labaran ƙarya.

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, shi ne ya bayyana hakan a ranar Litinin a Abuja yayin bikin Ranar ’Yancin ’Yan Jarida ta Duniya ta shekarar 2026 da aka gudanar a Radio House.

Ya ce: “Wannan gwamnati ta ba da fifiko ga haɗin gwiwa da masu ruwa da tsaki a kafafen yaɗa labarai da kuma abokan hulɗa na ƙasa da ƙasa domin inganta aikin jarida mai inganci da kuma yaƙi da yaɗa labaran ƙarya.”

Ya bayyana ’yancin ’yan jarida a matsayin muhimmin haƙƙi da kundin tsarin mulki ya tanada, yana mai tabbatar da cewa gwamnati za ta ci gaba da samar da yanayi mai kyau da zai bai wa kafafen yaɗa labarai damar gudanar da aikin su cikin ’yanci, tsaro da gaskiya.

“Gwamnatin Tarayya ta amince da ’yancin ’yan jarida, kuma za ta ci gaba da samar da yanayin da zai bai wa kafafen yaɗa labarai damar yin aikin su cikin ’yanci, tsaro da gaskiya,” inji shi.

Ministan ya ƙara da cewa Gwamnatin Tarayya ta ɗauki matakai na ƙarfafa gaskiya da samun bayanai ta hanyar cigaba da hulɗa da kafafen yaɗa labarai, aiwatar da dokar ’Yancin Samun Bayanai, da kuma saka hannun jari a hanyoyin sadarwa na jama’a.

Ya kuma bayyana haɗin gwiwar Nijeriya da UNESCO wajen kafa Cibiyar Ilimin Kafofin Watsa Labarai da Bayanai ta Duniya (IMILI) a Abuja a matsayin wani muhimmin mataki na ƙarfafa ilimin kafafen yaɗa labarai da bayanai da kuma inganta sadarwa mai kyau a wannan zamani na dijital.

Ministan ya buƙaci ’yan jarida da su ci gaba da kiyaye ƙwarewa da ƙa’idojin aiki, yana mai jaddada cewa dole ne ’yancin aikin jarida ya tafi tare da ɗaukar nauyin da ya rataye a wuyan jama'a.

“Ainihin gwajin ’yancin ’yan jarida ba wai a cikin furucin mu yake ba, a cikin ayyukan mu yake, yadda ’yan jarida ke gudanar da aikin su cikin tsaro, yadda ake yaɗa bayanai cikin gaskiya, da kuma yadda jama’a suke amfani da su yadda ya kamata,” inji shi.

A nata jawabin maraba, Babbar Sakatariyar Ma’aikatar Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Dakta Binyerem Ukaire, ta bayyana taron a matsayin wata dama ta ƙarfafa haɗin gwiwa da inganta wayar da kan jama’a.

Ta yi kira da a ƙara haɗin kai tsakanin hukumomi domin magance ƙalubalen yaɗa labaran ƙarya, musamman la’akari da yadda kafafen sadarwa na zamani suke ƙara yaɗuwa.

Gwamnatin Tarayya ta sake jaddada aniyar ta ta ci gaba da aiki tare da masu ruwa da tsaki domin gina tsarin bayanai mai ƙarfi da zai tallafa wa dimokiraɗiyya, haɗin kan ƙasa da cigaba mai ɗorewa.

Taron ya samu halartar Sufeto Janar na ’Yan Sanda, wanda jami’in hulɗa da jama’a na rundunar, DCP Anthony Okon Placid, ya wakilta; da Darakta-Janar na DSS, wanda Daraktan Tsare-Tsare, M.O. Chukwuka, ya wakilta; da Babban Sakataren Hukumar Kula da Aikin Jarida ta Nijeriya, Dakta Dilli Ezughah; da kuma Shugabar Ofishin UNESCO a Abuja, wadda Shugabar Sashen Sadarwa da Bayanai, Ms Yachat Nuhu, ta wakilta.

Hajji 2026: An fara tantance maniyyatan Kebbi rukunin farko, gabanin tashinsu zuwa Saudiyya.
04/05/2026

Hajji 2026: An fara tantance maniyyatan Kebbi rukunin farko, gabanin tashinsu zuwa Saudiyya.

04/05/2026

Mai neman tsayawa takarar kujerar dan majalisa mai wakiltar Gusau ta daya (1)

Hon Umar Mahmud (Mainan Damba) Tare da tareda tawagarsa jim kadan bayan maida fom dinsa na tsayawa takara a shekara ta 2027

Takarar 2027: Jam’iyyar APC ta tsawaita lokacin sayar da fom tare da gyara jadawalin tantance ƴan takaraA wata sanarwa d...
04/05/2026

Takarar 2027: Jam’iyyar APC ta tsawaita lokacin sayar da fom tare da gyara jadawalin tantance ƴan takara

A wata sanarwa da Sakataren Yada Labarai na ƙasa, Felix Morka, ya fitar a yau Litinin, jam’iyyar APC mai mulki a ƙasa ta bayyana cewa an ƙara wa’adin sayar da fom ɗin na-gani-ina-so da na takara zuwa ƙarfe 12 na dare na ranar Laraba, 6 ga watan Mayu, 2026.

Haka kuma, an ɗage ranar ƙarshe ta miƙa cikakkun fom zuwa ƙarfe 12 na dare na ranar Alhamis, 7 ga watan Mayu, 2026.

APC ta kuma ce za a gudanar da tantance ‘yan takara daga ranar Juma’a, 8 ga watan Mayu, zuwa Talata, 12 ga watan Mayu, 2026, yayin da za a fitar da jerin waɗanda s**a tsallake tantancewa a ranar Laraba, 13 ga watan Mayu, 2026.

Game da kuɗin fom, jam’iyyar ta tabbatar da cewa Fom ɗin takarar shugaban ƙasa ya kai Naira miliyan 100, Na gwamna Naira miliyan 50, ‘Yan Majalisar Tarayya Naira miliyan 10, ‘Yan Majalisar Dattawa Naira miliyan 20, ‘Yan Majalisar Jiha Naira miliyan 6.

Tun da farko, APC ta tsara fara sayar da fom daga 25 ga Afrilu zuwa 2 ga watan Mayu, 2026, amma aka fara aikin da jinkiri na kwanaki uku, lamarin da ya sa aka sake tsara jadawalin.

04/05/2026

FASHIN BAQI DANGANE DA TURURUWAR SAYEN FORM NA ‘YAN TA KARKARI A KOWANE FANNI NA JAHAR ZAMFARA

TARE DA COMRD SAIFULLAHI HASSAN

Hon Anas Muhammad Dan Amanar kasar hausa Wane fata zakuyi masa?
04/05/2026

Hon Anas Muhammad Dan Amanar kasar hausa

Wane fata zakuyi masa?

Gwamnatin Tarayya ta kaddamar da jigilar maniyyata 50,000 na aikin Hajjin 2026 a Abuja● Ku Kasance Masu Kyawun Hali Don ...
03/05/2026

Gwamnatin Tarayya ta kaddamar da jigilar maniyyata 50,000 na aikin Hajjin 2026 a Abuja

● Ku Kasance Masu Kyawun Hali Don Kare Kimar Nijeriya — Shettima

Daga Aliyu Samba

​Mataimakin Shugaban Kasa, Sanata Kashim Shettima, ya yi kira ga maniyyata aikin Hajjin shekarar 2026 da su kiyaye dabi’u na gari wadanda za su fito da martabar Nijeriya fili, sannan su kasance jakadu nagari ga kasarsu yayin gudanar da ibada a kasa mai tsarki.

​Shettima ya bayyana maniyyata a matsayin wakilan Nijeriya a idon duniya, inda ya bukace su da su nuna kyakkyawar dabi’a ta hanyar bin dokoki da oda na kasar Saudiyya.

​Mataimakin Shugaban Kasar ya bayyana hakan ne a ranar Lahadi, yayin da yake kaddamar da jigilar maniyyata ta farko na shekarar 2026 a Filin Jirgin Sama na kasa da kasa na Nnamdi Azikiwe da ke Abuja. Ya nanata cewa gwamnati ta jajirce wajen tabbatar da tsaro, tsari, da jin dadin dukkan mahajjata.

​“Ku jakadun Nijeriya ne. Kuna dauke da hoton kasarmu da mutuncin al’ummarmu. Halayenku su nuna tarbiya, tawali’u, hakuri, da gaskiya,” in ji shi.

​An fara jigilar ne da mahajjata kusan 500 daga Jihar Kogi zuwa kasar Saudiyya, yayin da jimillar maniyyata 50,000 ne ake sa ran za su gudanar da aikin Hajjin na bana daga Nijeriya.

​Da yake jawabi a wurin taron, Shettima ya bayyana cewa aikin Hajji wata tabbatacciyar yarjejeniya ce tsakanin gwamnatin Nijeriya da ’yan kasa, inda ya ce ya zama wajibi kan gwamnati ta sauke nauyin kula da su, su kuma maniyyata su kare mutuncin kasar.

​Ya kara da cewa: “Aikinmu ne mu tabbatar kowane maniyyaci ya yi wannan tafiya ba tare da wata wahala ko fargaba ba. Nasarar wannan aikin ba ta dogara ne kawai kan yawan jiragen da s**a tashi ba, a’a, tana ga jin dadin mahajjatanmu da kuma kauce wa duk wata nakasu da za a iya kauce mata.”

​A nasa jawabin, Gwamnan Jihar Kogi, Ahmed Usman Ododo, ya bayyana aikin Hajji a matsayin wata dama ta musamman da ke bukatar sadaukarwa ga Allah. Ya bukaci maniyyata da su ci gaba da addu’o’i ga Nijeriya, musamman kan zaman lafiya da ci gaban tattalin arziki.

​Haka zalika, ya nemi a taya Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu da Mataimakinsa Shettima da addu’a yayin da suke kokarin gyara kasar nan ta hanyar manufofinsu na "Sabunta Fata" (Renewed Hope).

​Shugaban Hukumar Jin Dadin Alhazzai ta Kasa (NAHCON), Ismail Abba Yusuf, ya tabbatar wa masu ruwa da tsaki cewa hukumar tana nan kan bakarta na tabbatar da jin dadin ’yan Nijeriya. Ya bayyana cewa hukumar tana fuskantar garambawul karkashin gwamnatin Shugaba Tinubu don tabbatar da gaskiya da kuma sauya fasalin aikin Hajji a kasar.

​Taron ya samu halartar Karamar Ministar Abuja, Dr. Mariya Mahmoud Bunkure, da wakilin Ministan Sufurin Jiragen Sama, Festus Keyamo, wadanda duka s**a jaddada kudurin gwamnati na ganin an kwashe mahajjata lafiya an kuma dawo da su lafiya.

Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un Allah yayiwa mahaifin abokin aikin mu Umar Muhammad T/kazai rasuwa Daraktan sashen la...
03/05/2026

Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un Allah yayiwa mahaifin abokin aikin mu Umar Muhammad T/kazai rasuwa Daraktan sashen labarai da al'amurran yau da kullum na Gamji tv da Radio Allah ya jikan shi da rahama Amin.

03/05/2026

Yanda akeyin aikin Hajji a aikace tare Malam Jamilu Ahmad Gusau

03/05/2026

BAYANIN AYUKKAN HAJJI A CIKIN KWANUKAN MINA

Tareda: Imam Sani Mai Albasa

Address

Gusau

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Dan kullum online TV posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Dan kullum online TV:

Share

Category