Nαzαrin Mαi Hαnkαli

Nαzαrin Mαi Hαnkαli Allah SWT yana cewa: Shin kuna tunanin Mun halicce ku Dan Wasa? Sannan Baza ku dawo garemu ba😭💔🥺

🛑 In kina soyayya da mai aure kuma kina so ki gane ya dace ki aure shi ko bai dace ba jarraba wannan:Ki kira shi kamar 1...
23/09/2025

🛑 In kina soyayya da mai aure kuma kina so ki gane ya dace ki aure shi ko bai dace ba jarraba wannan:

Ki kira shi kamar 11pm in y ɗauka a gaban matarsa ko shakka babu b mijin aure bane, kamar yadda ya yi mata kema wata rana zai yi miki fiye. Ko fita daga harkarsa kawai.

In yaƙi ɗauka, sai da safe ya kiraki toh ki sani yana son matarsa ko yana shakkarta. Zaki sha wahala a irin wannan gidan, fita daga sabgarsa ita tafi alheri.

In kuwa ya ce miki bai koma gida ba ki dasa ayar tambaya akansa, tabbas baya bawa matarsa lokaci kuma kema haka zai miki. Ki guje shi.

In kuwa ya shiga banɗaki sannan ya kiraki ko kuma ya fito waje ya kiraki toh wannan mayaudari ne, ki gaggauta raba hanya da shi.

Ai kinji dai ko🚶

KISAN DA WAYE ZAKI YI SOYAYYA Idan har zakiyi soyayya qawata yana da kyau ace yau kinsan da wanda zakiyi soyayya.saboda ...
20/09/2025

KISAN DA WAYE ZAKI YI SOYAYYA

Idan har zakiyi soyayya qawata yana da kyau ace yau kinsan da wanda zakiyi soyayya.

saboda mazan shaho sunyi yawa,wani ko kadan bashida burin auranki kawai dai zaizo yabata miki lokaci ne.idan kuma kika hadu da mungun namiji zaisan duk wani hanyar dazai bi domin yaga yarabaki da masoyinki na Asali.
yayi ta miki dadin bakin sa,har sai ya tabbatar baki da kowa sai shi.to a lokacinne zai bijiro miki danashi salon nacin amana ya gudu ya barki ko kuma ya kirkiro miki karyar cewa,a gida iyayenshi sun hadashi da wata 'yar uwarsa don ya aure ta,shikuma baya sonta.karya dai kala_kala zai shirya miki.

wani marar kunyar ma ,cemiki zaiyi kijira shi idan ya aure ta zai dawo ya aure ki,idan aka samu marar sanin ciwon kanta wanda batada wayo,sai ta amince mishi zata zauna jiran sa.
Haba Qawata! sai kace shi kadai ne namiji?
tun kafin lokaci yakara kure miki yana da kyau kisan abinda yake miki ciwo,kuma lallai Qawata

''KI SAN DA WAYE ZAKI YI SOYAYYA''

Qawata abinda zaki lura dashi,duk saurayin dake matukar kaunarki tsakaninsa da Allah,kuma yake da burin auranki,shi bazai wani tsaya dogon soyayya a waje ba.burinsa ya aure ki don kuyi Asalin ingantacciyar soyayya mai tsafta dakuma kamala.saboda burinsa kenan daman ya aure ki kuma ya aure ki.

amma qawata wani sai dai kawai yayi ta cikaki da surutu ya barki a matsayin 'yar tayashi hira da kuma surutu,shi bai fito ya aure ki ba,kuma bai bari wani ya fito ya aure ki ba.zakiga akwai wanda zai fito yana da niyyan auranki,amma sai ya dauke miki hankali .

karshe shi bai aure ki ba,wancan kuma ya tafi,sai kuma daga baya kidawo kinayin Danasani.

yar uwata ki kula da wanda zakiyi soyayya dashi.

▪ki samu nagartaccen namiji ,mai addini da tsoron Allah ,mai kula da hakkinki wanda idan har kin aure shi bazaki tabayin nadama ba,wanda kina da yakinin cewa zai damu da duk wani damuwarki,sannan zai kula da duk wasu al'amuranki,zai ji tausayinki,zai kuma tallafamiki da harma 'yan uwanki zasuji dadin tarayyarki dashi.
▪ki samu namiji mai Aji,mai kuma zuciya da son taimakawa,kisan cewa duk namijin da zai zamu yana da aji,yana kula dake zai zamu mai kwarjini a gun kowa ma,har ma kawayenki bazasu sami damar raina miki miji ba,saboda akwai mazan dako kadan basu da aji,idan sunga kawar matarsu suyi ta rawar jiki akan su,wannan yakan janyo matsala a tsakanin su,kuma hakan nasawa kawayen nata su raina shi domin baya da kamun kai.
▪Tundaga lokacin dayake nemanki zaki fara karantan yanayin halayyansa kafin kishiga ciki ki lura da yanayin sa.
▪yana da kyau ki tantance shin wannan soyayya na gaskiya yake minne,ko kuma sha'awata yake yi?
▪karki kuskura don kuna soyayya da mutum ya zama har kina buda baki gun tambayarsa kudi ko makamantar su,kul !Qawata karma kifara wannan rokun saboda kina zubarwa kanki Qima ne a gunsa.
▪Qawata ki lura da takun soyayya,kar dadin soyayya ya kaiki ya baro har ki nemi mallaka mishi kanki ki kula qawata karki fara wannan babban kuskuren.


©️ Nusaiba Tasiu Abdulrahim

KAR KI YARDA A SAKI A HANYAR DA BATA DACE BA🧕1️⃣9️⃣👉Sau da yawa akwai wasu mutanan dasu burin su shine,saka mutum gurbat...
20/09/2025

KAR KI YARDA A SAKI A HANYAR DA BATA DACE BA🧕

1️⃣9️⃣

👉Sau da yawa akwai wasu mutanan dasu burin su shine,saka mutum gurbatacciyar hanya,basa da burin daya wuce sai ganin mutum yana shiga wata hanya daban, saboda hakan ki kula da irin wadannan mutanan,kar ki yarda kina tarayya dasu.

👉 Kar ki yarda ace don kina da matsala a kawo miki shawaran cewa bin bokaye da wasu mashirka,ki san cewa daga lokacin da kika fara bin mutanan dasu daman can halakakku ne,kema kin zama halakakkiya kuma idan kika mutu a wannan hanyar wuta zaki shiga.
Ki sani wadannan bokayen babu abinda zasu miki sai ma su cire miki imani a zuciyar ki.
Kar ki bi rudin shaidan wajan saka kan ki a hanyar hallaka.

👉 Idan matsala k**e dashi babu wanda ya dace ki tunkara face ubangijin ki,shi kadai ne zai yaye miki ya kuma miki maganin wannan matsalar take saboda hakan ki rike ubangiji,kar ki zama mai sab'a mishi.

👉 Duk wanda zai nuna miki hanyar lalacewa ki kyale wannnan mutumin.

👉 Kar a zuga ki a saki wani hanya daban,ki daure ki yaki shaidan a cikin zuciyar ki.

👉 Kar ma kina kula irin wadannan mutanan wanda su basu da burin daya wuce ganin sun saka mutum wata hanya daban.

👉 Ki tsarkake zuciyar ki ki zama mutuniyar kirki a duk inda k**e.

👉 Kar ki bi hudubar mutanan banza.

👉 Kiji tsoron Allah

👉 Ki tsarkake zuciyar ki idan zuciya ta gyaru zata hanaki aikata abubuwa marar sa kyau.

©️ Nusaiba Tasiu Abdulrahim

20/09/2025

Rayuwa gwaji ce wanda ba'a gwada shi ba bazai ga sakamako ba.

Big shout out to my new rising fans! Sunusi Abbas, Aisha Alhassan, Nusaibah Salisu Abdulfatah, Jamilu Dan Gaske, Bilkisu...
19/09/2025

Big shout out to my new rising fans! Sunusi Abbas, Aisha Alhassan, Nusaibah Salisu Abdulfatah, Jamilu Dan Gaske, Bilkisu Lawal Aminu, Hussaini Zubairu LG, Legends Ay, Hafnah Usman, Ummi Lawal, Mubarak Musa Magajee, Imran Bello, Abduljalil Dahiru, Abdulmajid Prince Dembo, Saloju Muham, Dâbûwà Dàwàkí, Rukayya Nasir, Hassan Gee, Souley Issoufss, Usman Girma, Mousthopher Bn Yahya, Hafsert Usman, Abdoul Cash, Shamwil Adam, Aminu M Muhammed, Jibreel Nuxeelert, Musa Abu Rahmat, Aliyu Abubakar, Salisu Ahmad, Umar Muhammad Bello, Abou-bakr Herrouna Salyhu, Comrd Aleeyu Haidar, Lawal Usman Yero, Abbas Musa, Rash Key Heart, Dda Ibrahim, Nazifi Abdullahi, Umar Musa Yakub, Ummu Abdurrahman, Bilyaminu Abdulhamid, Usman Muhammad, Auwal Hero, Bab Son

19/09/2025

Wai da gaske ne 🛑 SAURAYI : idan yana da kudi yafi wahalar samun Mata?

In dai kai yaron wani ne a kasuwa, to ka karanta wannan rubutun cikin natsuwa:1- Dole ka riƙa girmama mai gidanka, da mu...
19/09/2025

In dai kai yaron wani ne a kasuwa, to ka karanta wannan rubutun cikin natsuwa:

1- Dole ka riƙa girmama mai gidanka, da mutunta shi da karrama shi, da ba shi matsayinsa na mai gida, koda ka girme shi a shekaru. Matuƙar kana son ci gaba, to dole ka girmama wanda yake gaba da kai. Bahaushe na cewa "yaro ba ya raina manya ya yi ƙarko" wannan gaskiya ne, kuma wannan magana tana shiga kusan kowanne babi na mu'amala; kasuwanci ko karatu ko addini da sauran sabgogi na zamantakewa.

2- Kada ka yi wani abu da zai riƙa jefa zargi cikin zuciyar mai gidanka game da kai, domin daga lokacin da mai gidanka ya rasa natsuwa da kai, ya fara tuhuma da zarginka jin daɗin zamanka da shi ya zo ƙarshe.

3- Kada ka bayyana wa mai gidanka kaifin basirarsa da ƙololuwar kwarewarka da iya magana dss, kada ka riƙa fin mai gidanka iya wanka da kwalliya da kashe kuɗi da makamantansu, domin zai fara jin kamar ka ɗauki hanyar yi masa juyin mulki. Shi ya sa mai littafin 48 Laws of Power, ya buɗe littafin da "Never outshine your master" don haka koda ka fi shi baiwa, to kada ka bayyana masa, ka sanya a tunaninsa ya riƙa jin sama yake da kai.

4- Kada ka taɓa zama ƙarƙashin mai gidanka ba tare da kana da shirin tsayuwa da ƙafarka ba, duk irin gata da kyautatawa da yake maka, ya zama kai ma kana da hadafin zama mai gidan kanka.

5- Galibin iyayen gida ba su son yaronsu na amana ya ɓalle daga gare su, dole ka san wannan sosai. Musamman yaro mai amana, wanda ya san sirrin kasuwancin mai gidansa. Shi ya sa wasu masu gidan da gangan suke daƙile ci gaban yaransu domin kada su girma su yi fukafukai, su fire su bar su, wasu mara sa imanin har da asiri suke turke yaransu.

6- Kada ka sake ka bari mai gidanka ya san shirinka na tsayuwa da ƙafarka, domin daga lokacin da ya sani, wani zai fara canja maka, ko kuma ƙoƙarin daƙile ka.

7- Kada ka ɓalle daga mai gidanka sai ka tabbata ka kai matsayin da za ka iya tsayuwa da ƙafarka, kada ka yi gaggawa, kuma ka yi haƙuri, ka bi komai a sannu, domin rashin iya tsayuwa da ƙafa bayan ɓallewar zai sanya ka yi biyu babu.

8- Daga lokacin da ka bayyana wa mai gidanka shirin ɓallewa to ka sani daga lokacin ya cire ka a fakaice, koda ba ka ɓalle ba, zai sauya maka, kuma ba zai ƙara bari ka san sirrin abubuwan da ake yi ba.

9- Idan ka riga ka ɓalle, to ba za ka sake dawowa ba, koda ka yi rashin nasara (Allah Ya tsare) kada ka dawo, ka nemi wani wajen kawai, ya zama tsakaninku mutunci ne da girmamawa kawai, domin idan ka dawo koda ya karɓe ka ba zai saki jiki da kai ba.

10- Idan za ka rabu da mai gidanka, duk da cewa ba zai so ku rabu ba, ka yi iya ƙoƙarinka ka ga kun rabu lafiya, ka yi haƙuri da duk abubuwan da za a riƙa faɗa, don ka rabu da mai gidanka da nufin tsayawa da ƙafarka ba ka yi wa kowa laifi ba, ba ka yi butulci ba. Kowa yana da haƙƙin ya cim ma burinsa na rayuwa. Don ka yi abin da kake ganin maslaha ne ga rayuwarka kuma ba ka taɓa haƙƙin kowa ba, kada ka ji a ranka ka yi laifin komai.
Allah Ya ba mu sa'a.
© Isa Sadi

Idan kuna ƙaunar juna da gaske, to ku girmama wanda kuke ƙaunar ta hanyar yin aure.  Kuma wanda bai da ikon yin aure a y...
19/09/2025

Idan kuna ƙaunar juna da gaske, to ku girmama wanda kuke ƙaunar ta hanyar yin aure.
Kuma wanda bai da ikon yin aure a yanzu, to ya nemi taimakon Allah, ya yi haƙuri, kada ya buɗe wa kansa ƙofar saɓo, sa'an nan ya jingina laifinsa da "halin rayuwa" ko "ƙaddara".
Kada ya jawo wa kansa karyewar zuciya ko damuwa, sa'an nan ya riƙa zargin an yaudare shi.
Wanda ya ƙulla soyayya bai shirya aure ba, shi ne ya yaudari kansa; wadda ta ƙulla soyayya da wanda bai shirya aure ba, ita ce ta yaudari kanta.
Domin lokacin da ya samu hali, zai iya canja hali, ya nemi wata ya aura ba ita ba. Ko kuma ita ta auri wanda ya shirya, ta jefar da shi da soyayyarsa.
Dayawan mutanen da suke kuka an yaudare su, su ne s**a yaudari kansu, idan aka yi binciken ƙeƙe da ƙeƙe.
Dukkan wata mu’amala ko hulɗa tsakanin namiji da mace waɗanda ba ma’aurata ba ne, kuma ba cikin sahihiyar hanyar neman aure ba ce, wannan alaƙa ba ta haifar da komai sai raɗaɗi da ciwo a ƙarshe.
© Isa sidi

🛑 FALALAR ISTIGFARI DA SALATIN ANNABI(Tsira da aminci su tabbata a gare shi)Daga Abu Zarr ( Allah ya yarda dashi) cewa :...
19/09/2025

🛑 FALALAR ISTIGFARI DA SALATIN ANNABI

(Tsira da aminci su tabbata a gare shi)
Daga Abu Zarr ( Allah ya yarda dashi) cewa : Allah ta'ala yace: ya ku 'ya'yan Adam dukkaninku masu sabo ne sai wanda na yafewa saboda haka ku nemi shiriya ta sai na gafarta muku. Kuma dukkaninku mabukata ne sai wanda na arzurta, saboda haka ku roke ni sai na baku. Kuma dukkaninku batattu ne sai wanda na shiryar saboda haka ku nemi shiriya ta sai na shiriaya da ku.

Duk wanda ya nemi gafara ta kuma ya san cewa ni mai gafara ne kuma ya san cewa ni mai iko ne akan na gafarta masa, zan gafarta masa kuma ba zan damu ba
Muslim, Tirmizhi, Ibn Majah da Baihaki s**a fitar da shi15

2. Daga Abu sa'id Alkhudri (Allah ya yarda dashi) cewa Annabi (Tsira da Amincin su tabbata a gare shi ) yace: Iblis yace: na rantse da girman ka ba zan gushe ba ina halakar da bayinka matukar rayukansu suna jikinsu. Sai Allah yace; na rantse da girma na da buwayata ba zan gushe ba ina gafarta musu matukar sun nemi gafarata
Ahmad da Hakim ne s**a rawaito shi

3. Daga: Dan Abbas ( Allah ya yarda dashi) cewa Annabi ( Tsira da Aminci su tabbata a gare shi) yace: Duk wanda ya lizimci Istigfara, Allah zai sa masa budi a cikin kowanne bakin ciki, da kuma mafita a cikin kowanne kunci, sannan zai arzurta shi ta wajen da ba ya tsammani
Abu Da'ud, nisai da ibn majah s**a rawaito

4. Daga: Ummu Asmat Al-Ausiyyat ( Allah ya yarda da ita) tace : Manzon Allah ( tsira da Aminci su tabbata gare shi) yace: babu wani musulmi da zai aikata wani zunubi face sai mala'ika ya saurare shi tsawon awa ( hour) uku, idan ya nemi gafara to ba za a rubuta masa zunubin ba, kuma Allah ba zai masa azaba ba ranar kiyama.
Hakim ya fitar dashi a cikin mustadrak, kuma yace: ingantaccen sanadi ne.

Ya Allah ka bamu ikon yawaita istigfari da salatin Annabi.

Ka gafarta muna zunuban mu.

©️ Nusaiba Tasiu Abdulrahim

19/09/2025

Aure na daga dalilan dake kawar da ciwon hauka, kamar yadda gaurantaka na daga dalilan kamuwa da ciwon hauka
نهاية المطلب ١٢/٤٣

19/09/2025

Idan aka girmama namiji aka kiyaye masa abinda yakeso da kuma yake ki, yakan ba da tukwuicin kansa gabadaya da zuciya

Bayan ta shiga ganin likita, sai ta ce, in babu damuwa ina so ka yiwa mijina izini ya shigo...!!Likita ya ce, kar ki sam...
19/09/2025

Bayan ta shiga ganin likita, sai ta ce, in babu damuwa ina so ka yiwa mijina izini ya shigo...!!

Likita ya ce, kar ki samu damuwa, ni ƙwararren likita ne, kuma na yi rantsuwa ba zan ci amanar aikina ba.

Ta ce, ba nan ne matsalar ba, akwai Malaman jinya (Nurses) kyawawa da suke kai komo a asibitin nan, kuma na bar mijina a waje.

Dr. In ka rantse ba zaka ci amanar aikinka ba, ni fa mijina bai rantse ba zai ci amanata ba.....!!!!

Sukairaj Hafiz Imam.

Address

Unguwar Nassarawa
Gusau
632101

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Nαzαrin Mαi Hαnkαli posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Nαzαrin Mαi Hαnkαli:

Share