Fara'a tv

Fara'a tv A tuntubemu 08133376020/08164949696
(1)

Fara'a Tv tasha ce dake karkashin Kamfanin Fara'a Media Services Ltd da ke kawo muku ingantattun labarai daga kowace kusurwa a faɗin duniya ba tare da nuna wariya ko banbancin addini ko kabilanci ba. Faraa TV Na Maraba Da Ku, Ku Ci Gaba Da Kasancewa Da Mu A Kowane Lokaci Domin Sanin Halin Da Kasa Ke Ciki Da Wasu Sassa Daban-daban Na Duniya, Mun Gode

Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa LabaraiMinistan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai...
12/09/2025

Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya bayyana Etsu Nupe, Mai Martaba Alhaji Yahaya Abubakar, a matsayin ginshiƙi na zaman lafiya da haɗin kai a Nijeriya, wanda ya sadaukar da rayuwar sa wajen bunƙasa masarautar Nupe, Jihar Neja, da ƙasa gaba ɗaya.

A cikin saƙon taya murna na zagayowar ranar haihuwar sa ta 73 da kuma cika shekara 22 a kan karagar mulki, Ministan, wanda shi ne Kakakin Nupe, ya ce: “Etsu Nupe mutum ne mai jajircewa wajen tabbatar da zaman lafiya da haɗin kai, wanda a cikin shekaru 22 da s**a gabata ya jagoranci ƙasar Nupe zuwa cigaba da bunƙasar da ba a taɓa ganin irin ta ba.”

Idris ya jaddada rawar da Sarkin Mai Daraja ta Ɗaya ya taka wajen ƙarfafa haɗin kan Nijeriya, tun daga gudunmawar sa a rundunar sojin ƙasa har ya kai matsayin Birgediya Janar, zuwa irin gudunmawar da yake bayarwa a matsayin Shugaban Kwamitin Tsara Ayyuka na Majalisar Sarakunan Gargajiya ta Nijeriya.

Ya ƙara da cewa: “Don haka taya ɗaya daga cikin shugabannin Nijeriya mafiya sauƙin kai, masu karamci da jarumtaka, murnar zagayowar ranar haihuwar sa, da roƙon Allah ya ci gaba da yi masa jagora a babban nauyin shugabanci na ƙasar Nupe da jama’ar ta, ya kuma ƙara masa ƙarfi don ci gaba da aiki wajen tabbatar da zaman lafiya, haɗin kai, da cigaban Nijeriya.”

Gwamnatin Tarayya ta fara rabon kayan noma kyauta ga manoma a Jihar NejaGwamnatin Tarayya ta fara rabon kayan noma kyaut...
12/09/2025

Gwamnatin Tarayya ta fara rabon kayan noma kyauta ga manoma a Jihar Neja

Gwamnatin Tarayya ta fara rabon kayan noma kyauta ga kananan manoma a Jihar Neja domin karfafa noman ko wane lokaci na shekara da kuma bunkasa samar da abinci.

Karamin Ministan Noma da samar da Abinci, Dakta Aliyu Sabi Abdullahi, ya ce wannan shiri wani bangare ne na manufofin gwamnatin Bola Ahmed Tinubu na tabbatar da wadatar abinci da kuma tsaron abinci a Najeriya.

Kayan da ake rabawa sun hada da taki, magungunan kashe kwari, iri, sinadaran bunkasa amfanin gona, injinan feshi da sauran kayayyakin da za su taimaka wa manoma. Za a ci gaba da raba irin wadannan kayan a jihohi 36 da kuma Babban Birnin Tarayya.

Ministan ya jinjinawa Gwamnan Jihar Neja, Muhammad Umaru Bago, bisa nasarorin da jihar ta samu a fannin noma, lamarin da ya ce ya sanya ta zama abin koyi wajen aiwatar da shirye-shiryen gwamnati.

Shi ma Gwamna Bago ya gode wa Shugaba Tinubu bisa tallafin da ya bayar, yana mai cewa shirin zai karfafa gwiwar manoma kuma ya ba su damar dogaro da kansu. Ya kuma bayyana cewa Jihar Neja ta samu damar fitar da irin gyaɗa (sesame seeds) na dalar Amurka miliyan 2.2 zuwa kasashen waje, tare da shirin dawo da Bankin Tattalin Arzikin Kananan Manoma (Cooperative Bank) da Naira biliyan 2 domin rage radadin rancen da ke da ruwa mai yawa.

Gwamna Uba Sani ya kaddamar da titunan Rigasa da Zango a KadunaGwamnan Jihar Kaduna, Sanata Uba Sani, ya kaddamar da aik...
12/09/2025

Gwamna Uba Sani ya kaddamar da titunan Rigasa da Zango a Kaduna

Gwamnan Jihar Kaduna, Sanata Uba Sani, ya kaddamar da aikin sabunta titunan Rigasa a Karamar Hukumar Igabi da kuma Zango Road a Kaduna South, a wani mataki na cike gibi da ɗorewar rashin kula da manyan wuraren da masu karamin karfi ke rayuwa.

Rigasa, wanda ɗaya ce daga cikin gundumomi mafi girma da yawan jama’a a Najeriya, da Zango, inda ake da muhimman cibiyoyi k**ar kasuwar shanun Zango, makarantar Sheikh Abubakar Gumi da School of Health Technology, sun shafe shekaru masu yawa suna fama da matsalar hanyoyi marasa kyau.

A cewar Gwamna Uba Sani, wannan aikin ba wai shimfiɗa kwalta kaɗai ba ne, illa dai wani babban mataki na buɗe hanyoyin tattalin arziki, ƙirƙirar guraben ayyukan yi da kuma mayar da martani ga jajircewar jama’a waɗanda s**a ci gaba da taka muhimmiyar rawa a ci gaban Kaduna duk da kalubalen da s**a fuskanta.

Ya bayyana cewa sabbin hanyoyin na daga cikin shirin sake fasalin muhimman gine-gine na jiharsa, inda a matakin farko aka ƙaddamar da tituna 85 mai tsawon kilomita 785, daga cikinsu an kammala 44, sauran kuma suna dab da kammaluwa. A mataki na biyu kuma, an ƙara tituna da gadaje 50 da s**a kai tsawon kilomita 550.

Gwamnan ya tabbatar da cewa kamfanin CCECC zai kammala aikin cikin watanni takwas, tare da jaddada cewa hakan zai bai wa al’umma damar fara cin moriyar sabbin hanyoyin cikin kankanin lokaci. Ya kuma yi kira ga shugabannin al’umma, mazauna yankuna, ‘yan kwangila da masu tsara manufofi da su ɗauki aikin a matsayin na su, su kiyaye shi kuma su tabbatar da ya amfanar da al’ummar da ke gaba.

Sanata Uba Sani ya nanata kudirin gwamnatinsa na kasancewa mai mayar da hankali kan talakawa, ci gaba da tabbatar da adalci da daidaito, tare da gina Kaduna da kowa zai amfana da ci gaban ta.

IGP Egbetokun: Tsaron iyaka na buƙatar amfani da fasahar zamani da haɗin kai tsakanin hukumomi.Sufeto Janar na ‘Yan Sand...
12/09/2025

IGP Egbetokun: Tsaron iyaka na buƙatar amfani da fasahar zamani da haɗin kai tsakanin hukumomi.

Sufeto Janar na ‘Yan Sanda, IGP Kayode Egbetokun, ya umarci kwamandojin rundunar 'Border Patrol' a fadin ƙasa da su ƙara kaimi wajen tabbatar da tsaro a iyakokin Najeriya, yana mai jaddada cewa su ne garkuwa ta farko da ke kare ƙasa daga barazanar tsaro daga waje.

A wata sanarwa da mai magana da yawun rundunar, CSP Benjamin Hundeyin, ya fitar, Egbetokun ya yi wannan bayani ne yayin taron kwamandojin da aka gudanar a Hedikwatar ‘Yan Sanda, dake Abuja a ranar Juma’a.

IGP Egbetokun ya bayyana cewa girman iyakokin Najeriya da kuma hanyoyin ruwa da ke haɗa ƙasar da 'Gulf of Guinea' suna buƙatar tsauraran matakai na musamman. Ya yaba da irin rawar da rundunar ke takawa wajen yaƙi da laifukan ƙetare iyaka, amma ya bukaci a rungumi sabbin dabaru na zamani.

“Ba za mu iya yaƙar laifukan ƙarni na 21 da kayan aiki na ƙarni na 20 ba. Dole mu rungumi fasahar zamani – k**ar na’urorin sa ido, drones, na’urorin tantance bayanai, da nazarin bayanai a ainihin lokaci,” in ji shi.

Ya kuma jaddada cewa leƙen asiri, haɗin kai tsakanin hukumomi, da kuma amincewar jama’a su ne ginshiƙai na tsaron iyaka mai inganci. IGP Egbetokun ya tabbatar da cewa walwalar jami’ai da kwamandoji za ta ci gaba da kasancewa babban abin da zasu baiwa muhimmanci.

Dakarun Operation FANSAN YANMA tare da jami’an ƴan sanda da ƙungiyoyin sa-kai sun yi nasarar fatattakar ’yan bindiga da ...
12/09/2025

Dakarun Operation FANSAN YANMA tare da jami’an ƴan sanda da ƙungiyoyin sa-kai sun yi nasarar fatattakar ’yan bindiga da s**a yi yunkurin kai hari a Matazu, dake Jihar Katsina.

Rahotanni sun ce maharan sun afka unguwar Yar Makera da misalin ƙarfe 9:50 na dare a ranar Alhamis. Sai dai jami’an tsaro da mazauna yankin s**a yi gaggawar mayar da martani, s**a shiga musayar wuta da ’yan bindigar, lamarin da ya tilasta musu janyewa.

Wani mazaunin yankin, Aliyu Hassan, mai shekaru 70, ya rasa ransa yayin harin, yayin da wani mutum mai suna Mustapha Ado, mai shekaru 35, ya samu munanan raunuka kuma yana karɓar magani a asibiti.

An tabbatar da cewa dakarun tsaro yanzu haka suna aikin tantance wa da zakulo ’yan bindigar da s**a tsere cikin dazuka.

Wani jami’in ɗan sanda a Jihar Filato, Inspector Lasare Jeremiah, ya rasa ransa bayan wani da ake zargi ya yi masa sharr...
12/09/2025

Wani jami’in ɗan sanda a Jihar Filato, Inspector Lasare Jeremiah, ya rasa ransa bayan wani da ake zargi ya yi masa sharri cewa shi barawo ne, abin da ya jawo jama’a s**a yi masa dukan kawo wuka.

Kakakin rundunar, DSP Alabo Alfred, ya ce lamarin ya faru ne a ranar Laraba, 10 ga Satumba, a ƙauyen Nyakala, Ƙaramar Hukumar Bassa.

Ya bayyana cewa marigayin, wanda ke aiki a Sashen Binciken Manyan Laifuka (CID), tare da wani abokin aikinsa, sun je cafke wani da ake nema bisa laifuka, mai suna Audu Abdullahi, wanda ake zargi da addabar al’umma a yankin.

Lokacin da aka tare shi, Abdullahi ya yi ƙarar karya cewa jami’an da s**a k**a shi barayi ne, abin da ya jawo jama’a s**a afka wa ɗan sandan da duka.

Bayan daga bisani aka fahimci gaskiya, jama’ar s**a kuma juya wa wanda ake zargin. An garzaya da su asibiti, inda Inspector Jeremiah ya rasu, yayin da Abdullahi ya mutu daga baya a Asibitin Koyarwa ta Jami’ar Jos.

DSP Alfred ya tabbatar da cewa an fara bincike kan lamarin, yayin da Kwamishinan ƴan sanda na jihar, Emmanuel Olugbemiga Adesina, ya yi kira ga jama’a da su guji ɗaukar doka a hannunsu.

Tinubu Ya Kaddamar da Shirin RenewHER Don Inganta Lafiyar Mata Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya ƙaddamar da wani sabon...
12/09/2025

Tinubu Ya Kaddamar da Shirin RenewHER Don Inganta Lafiyar Mata

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya ƙaddamar da wani sabon shiri mai suna RenewHER da nufin rage mace-macen uwa da kuma inganta lafiyar mata a Najeriya.

Shugaban ƙasar, wanda Mataimakinsa Kashim Shettima ya wakilta a wajen bikin ƙaddamarwar da aka gudanar a Fadar Shugaban Ƙasa, Abuja, ya bayyana cewa shirin zai zama ginshiƙin tabbatar da ci gaban al’umma.

Ya ce: “Babu babban gwajin halin ƙasa fiye da yadda take kula da matanta. Lafiyar uwa ita ce zuciyar kowane iyali kuma ita ce sahihin ma’aunin jin daɗin ƙasa.”

A cewar shugaban ƙasar, shirin RenewHER zai kafa ofishi na musamman na shugaban ƙasa kan lafiyar mata, tare da haɗin gwiwar Ma’aikatar Lafiya, Ma’aikatar Harkokin Mata, ofishin tsare-tsaren lafiya na jihohi (SWAp), da kuma ƙungiyar matan gwamnonin Najeriya.

Haka kuma, an ƙirƙiri National Women’s Health Digital Hub, cibiyar zamani da za ta yi amfani da fasahar AI wajen yaɗa bayanai kan lafiyar uwa, lafiyar matasa, rigakafin cututtuka da kuma ƙarfafa aikin jinya.

Matar gwamnan Kwara kuma shugabar ƙungiyar matan gwamnonin ƙasa, Farfesa Olufolake AbdulRazaq, ta ce RenewHER ya nuna jajircewar gwamnatin Tinubu wajen ba da dama ga mata, tare da tabbatar da cewa dukkan jihohi za su mara baya ga shirin.

A nata jawabin, mai ba da shawara ta musamman ga shugaban ƙasa kan lafiyar mata, Dr. Adanna Steinacker, ta bayyana cewa RenewHER ya samo asali ne daga hangen nesa na shugaban ƙasa wajen ɗaukar lafiyar mata a matsayin muhimmin fifiko na ƙasa.

Haka nan, wakiliyar mata ta majalisar dinkin duniya a Najeriya, Ms. Beatrice Eyong, ta yi maraba da shirin, tana mai cewa shi ne karo na farko da gwamnatin Najeriya ta ɗauki lafiyar mata a matakin koli, tare da tabbatar da cewa MDD za ta yi aiki da gwamnati wajen bunƙasa damar samun kulawa ga mata a ƙasar.

Taron ya samu halartar shugaban ma’aikatan fadar shugaban ƙasa, Femi Gbajabiamila, wasu matan gwamnonin jihohi, jakadun ƙasashen waje da sauran manyan baki.

Kungiyar rajin tabbatar da shugabanci na gari a jihar Zamfara, Zamfara Good Governance Forum, ta nuna ɓacin rai da damuw...
12/09/2025

Kungiyar rajin tabbatar da shugabanci na gari a jihar Zamfara, Zamfara Good Governance Forum, ta nuna ɓacin rai da damuwa kan yajin aikin da ma’aikatan jinya karkashin kungiyar National Association of Nurses and Midwives (NAS) s**a tsunduma a jihar.

A cikin wata sanarwa da sakataren kungiyar, Kabiru Ibrahim Gusau, ya sanya wa hannu, an danganta lamarin kai tsaye da rikon sakainar kashi da Gwamna Dauda Lawal Dare yake yi wa bangaren kiwon lafiya.

Kungiyar ta bayyana rashin jin daɗi kan yadda aka ware malaman jinya daga sabon tsarin albashi da aka amince da shi, wanda aka aiwatar ga likitoci kawai, duk da roƙo da gargaɗin da aka sha yi daga bangaren jinya.

Ta yi gargaɗin cewa wannan wariya ba wai kawai take mutuncin malaman jinya da sauran ma’aikatan lafiya ba, har ma tana jefa lafiyar dubban jama’a cikin haɗari, musamman a daidai lokacin da jihar ke fama da annobar kwalara.

“Shirin gwamnatin na fifita likitoci kawai babbar shaida ce ta amfani da mulki cikin son rai da rashin gaskiya. Malaman jinya su ne ginshiƙin tsarin kiwon lafiya, raina su kuwa illa ce kai tsaye ga rayukan jama’a,” in ji Gusau.

Ya ƙara da cewa halin ko-in-kula na gwamnatin jihar na iya haifar da mummunan tasiri ga harkar kiwon lafiya baki ɗaya. Gusau ya ce idan annobar kwalara ta ƙara k**ari kuma rayuka s**a salwanta sak**akon yajin aikin, alhakin zai rataya ne a wuyan Gwamna Dauda Lawal Dare.

Kungiyar ta bukaci gwamnan da ya gaggauta tsoma baki ta hanyar umartar Ma’aikatar Lafiya da ta gyara tsarin albashin cikin adalci, tare da haɗa malaman jinya cikin biyan watan Satumba.

“Lokacin bayar da hujja ya wuce. Jama’ar jihar Zamfara ba za su iya jure rugujewar tsarin kiwon lafiya a daidai lokacin da aka fi buƙatarsa ba. Idan ba a ɗauki mataki cikin gaggawa ba, tarihi zai tuna da Gwamna Lawal a matsayin wanda ya yi watsi da lafiyar jama’arsa,” in ji Kabiru Ibrahim Gusau.

Gwamnatin Tinubu Za ta Gaggauta Bayar da Lamunin Naira Biliyan 250 Ga ManomaMataimakin Shugaban Ƙasa, Sanata Kashim Shet...
11/09/2025

Gwamnatin Tinubu Za ta Gaggauta Bayar da Lamunin Naira Biliyan 250 Ga Manoma

Mataimakin Shugaban Ƙasa, Sanata Kashim Shettima, ya umarci Hukumar Kula da Samar da Abinci ta Fadar Shugaban Ƙasa (PFSCU) da ta gaggauta sakin lamunin Naira biliyan 250 ga ƙananan manoma a faɗin ƙasar.

Wannan umarni ya biyo bayan amincewar Shugaba Bola Ahmed Tinubu da shirin bayar da bashin, domin ƙarfafa noman rani a tsakiyar damuna da kuma tabbatar da ci gaba da samar da isasshen abinci ga yan Najeriya.

Shettima ya yi gargaɗi ga hukumar PFSCU da ta tabbatar kudaden sun isa ga manoman da s**a cancanta ba tare da jinkiri ba, yana mai nanata cewa gwamnati ba za ta lamunci sakaci ko gazawa ba. A cewarsa, "Shirin gwamnatin Shugaba Tinubu na bayar da lamunin bai zo don a ajiye kuɗi ba, sai don al’umma su amfana cikin lokaci."

Mataimakin Shugaban Ƙasar ya yaba wa jajircewar Shugaba Tinubu wajen tallafa wa hukumar domin inganta tsare-tsaren samar da abinci, musamman ta fuskar sauƙaƙe hanyoyin samun taki da kafa asusun tallafin Shugaban Ƙasa. Ya ƙara da cewa, idan ma’aikatun gwamnati, hukumomi da masana’antu masu zaman kansu s**a haɗa kai, wannan shiri zai samar da ci gaban tattalin arziki cikin gaggawa.

Taron ya samu halartar gwamnoni da sauran masu ruwa da tsaki, inda s**a nuna goyon bayan su ga matakin gwamnatin, tare da tabbatar da cewa za su ba da dukkan haɗin kai wajen tabbatar da tsarin rabon lamunin ya gudana cikin gaskiya da nagarta.

An yi gargaɗi ga matafiya kan amfani da hanyar da ta haɗa Shinkafi a Jihar Zamfara da kuma isa zuwa Sabon Birni a Jihar ...
11/09/2025

An yi gargaɗi ga matafiya kan amfani da hanyar da ta haɗa Shinkafi a Jihar Zamfara da kuma isa zuwa Sabon Birni a Jihar Sakkwato, bayan ruwan sama ya ruguza sassan hanyar.

Rahotanni sun bayyana cewa lalacewar hanyar ta jawo tsaiko ga masu zirga-zirga, tare da haifar da haɗarin lalacewar motocin matafiya da kuma jinkirin isa zuwa Sabon Birni.

Hukumomi sun bukaci matafiya su yi taka-tsantsan, tare da la’akari da amfani da wasu hanyoyin na daban.

11/09/2025

Dr. Sani Abdullahi Shinkafi ya bayyana fannoni biyu a mulkin Tinubu: abin yabawa da abin fallasa.

Hotuna: An Hangi Sheikh Ibrahim Zakzaky a Taron Majalisar Ƙoli ta Majma'u Taqarib bainal Mazahibul IslamiyyahJagoran ƙun...
11/09/2025

Hotuna: An Hangi Sheikh Ibrahim Zakzaky a Taron Majalisar Ƙoli ta Majma'u Taqarib bainal Mazahibul Islamiyyah

Jagoran ƙungiyar Shi’a na Afirka, Sheikh Ibrahim Zakzaky, an hange shi a wajen zaman majalisar ƙoli ta Majma'u Taqarib bainal Mazahibul Islamiyyah, bayan kammala taron ƙasa da ƙasa na haɗin kan Musulmi karo na 39 a birnin Tehran. Rahotanni sun bayyana cewa, Membobin majalisar sun gudanar da zaman bita na musamman domin tattaunawa kan hanyoyin ƙarfafa fahimtar juna da haɗin kai a tsakanin Musulmi.

📸 Szakzakyoffice

Address

Government House Gusau
Gusau
3337

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Fara'a tv posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Fara'a tv:

Share

Category