09/07/2026
'Gani Ya Kori Ji': Aikin sake gina t**in Abuja–Kaduna ya kai kashi 85 cikin 100
Tawagar 'yan jarida da ke rangadin manyan ayyukan gwamnatin tarayya a Arewacin Najeriya ƙarƙashin shirin 'Gani Ya Kori Ji' ta ziyarci aikin sake gina babbar hanyar Abuja–Kaduna, inda aka bayyana cewa an kammala kusan kashi 85 cikin 100 na aikin.
Rangadin na gudana ne tare da Babban Mai Taimakawa Shugaban Ƙasa kan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Malam Abdulaziz Abdulaziz. Kafin isa wurin aikin, tawagar ta kai ziyara Kaduna Western Bypass da kuma tashar Green Ville CNG da ke jihar Kaduna.
Jami'an da ke kula da aikin sun yi wa tawagar bayani kan yadda ake tafiyar da aikin, inda s**a ce ana ci gaba da aiwatar da shi cikin sauri tare da kiyaye ƙa'idojin inganci.
Sun bayyana cewa ana sake gina t**in ne da kankare mai ƙarfi (reinforced concrete pavement) maimakon kwalta, domin ƙara masa ɗorewa, rage saurin lalacewa da kuma tsawaita rayuwar hanyar.
A cewarsu, da zarar an kammala aikin, ana sa ran zai rage lokacin tafiya tsakanin Abuja da Kaduna, ya sauƙaƙa cunkoson ababen hawa, ya inganta tsaron matafiya, tare da ƙara bunƙasa harkokin kasuwanci da jigilar kayayyaki a yankunan da t**in ya ratsa.
Da yake jawabi bayan rangadin, Malam Abdulaziz Abdulaziz ya bayyana t**in Abuja–Kaduna a matsayin ɗaya daga cikin muhimman hanyoyin sufuri a Najeriya, yana mai cewa gwamnatin tarayya ta ba aikin fifiko saboda muhimmancinsa ga tattalin arziki da haɗa sassan ƙasar.
Ya ce manufar shirin 'Gani Ya Kori Ji' ita ce bai wa 'yan jarida damar ganin ci gaban ayyukan gwamnati da idonsu, domin su isar wa al'umma sahihan bayanai kan yadda ake aiwatar da su.
Tawagar ta yabawa irin ci gaban da aka samu a aikin, tare da bayyana fatan cewa idan aka kammala shi, zai inganta zirga-zirga, ƙara tsaron masu amfani da hanya, da kuma amfani ga miliyoyin 'yan Najeriya da ke zirga-zirga a kan hanyar Abuja–Kaduna.