14/11/2025
Birnin Gusau ya cika ya tumbatsa, yayin da al'umma s**a mamaye tituna wajen tarbar Minista Bello Matawalle
Mutane ba adadi, amma masu kiyasi sun ce sun kai kusan miliyan biyu, ko ma fiye, s**a cika titunan Gusau, babban birnin jihar Zamfara a yayin wata gagarumar tarbar da ba a saba ganin irinta ba, mai cike da dumbin tarihi ga Dr Bello Mohammed Matawalle, Minista a ma'aikatar tsaron Nijeriya kuma tsohon Gwamnan jihar Zamfara.
Wakilinmu ya rawaito cewa birnin ya cika da jama’a daga ko’ina, tun daga shatale-talen roundabout zuwa filayen kasuwanni, inda maza, mata, matasa, dattawa ke ta tururuwar amsa kiran dan baiwa. Yana shiga birnin na Gusau, kowa ya dauka da tafi da jinjina ana murna cike da shaukin ganin masoyi.
Magoya bayansa sun ce wannan tarba ta samo asali ne daga ayyukan da Matawalle ya gudanar lokacin yana gwamna. Sun ambaci aikin gyaran manyan hanyoyi da ya buɗe sabbin damarmakin kasuwanci, ginin sabon filin jirgin saman Gusau, ƙara samar da ruwan sha ta hanyar rijiyoyin burtsatse, da gyaran cibiyoyin kiwon lafiya da s**a taimaka wa jama’a. Haka kuma sun jingina ma ƙoƙarinsa na inganta tsaro ta hanyar samar da motocin aiki da kayan tallafi ga jami’an tsaro. Ga yawancin al'ummar jihar, waɗannan ayyuka ba alkawari ba ne kawai na shaci-fadi, sun ce abubuwa ne da s**a gani a aikace, muraran.
Yayin da ayarin motocin Minista Matawalle s**a shiga birnin, jama’a s**a cika hanyoyi. Mata sun yi layi a gefen hanya suna waƙoki na yabo da jinjina. Matasa sun yi dogon jerin gwano suna binsa cike da shauki da kauna. Tsofaffi suna daga hannaye suna addu’o'i ga Minista Matawalle. ’Yan kasuwa sun bar shaguna, dalibai suna hawa kan motocin mutane suna daga tutoci, jama’a kuma suna kiran sunansa ba kakkautawa. Bayanai sun ce birnin Gusau bai ta ganin irin wannan farin ciki ba tsawon shekaru sai a wannan lokacin da Matawalle ya yi wannan ziyara.
Wasu shugabannin siyasa da na al’umma sun ce wannan tarba shaida ce ta sake amincewar jama’a da shi. Sun bayyana cewa ba a samun irin wannan taron jama’a sai ga shugaba da ya tabo rayuwar mutane. A wurin taron an ji wasu na cewa har yanzu Matawalle shi ne ɗaya daga cikin manyan ’yan siyasa masu tasiri a jihar.
A cewarsu, irin wannan goyon baya da farin jini yana nuna cewa Matawalle zai iya sake tallafa wa Shugaba Bola Ahmed Tinubu a zaɓen shekarar 2027, k**ar yadda suke ganin ya yi a baya. Magoya bayan sun furta wadannan kalamai a wurare daban-daban a cikin birnin cewa wannan fitar farin dango da al'umma s**a yi, ya nuna yadda har yanzu jama'ar jihar ke ci gaba da nuna aminci da soyayya ga Matawalle.
Abin da ya faru a Gusau ya zarce tarba kaɗai. Alama ce ta nuna godiya daga mazauna da ke ganin ayyukan Matawalle sun taimaka wajen sauya jiharsu. An karkare da saƙo guda: Mutanen Gusau har yanzu suna tare da Bello Mohammed Matawalle saboda suna ganin ya yi musu aiki lokacin da ya fi muhimmanci.