Fara'a tv

Fara'a tv A tuntubemu 08133376020/08164949696
(1)

Fara'a Tv tasha ce dake karkashin Kamfanin Fara'a Media Services Ltd da ke kawo muku ingantattun labarai daga kowace kusurwa a faɗin duniya ba tare da nuna wariya ko banbancin addini ko kabilanci ba. Faraa TV Na Maraba Da Ku, Ku Ci Gaba Da Kasancewa Da Mu A Kowane Lokaci Domin Sanin Halin Da Kasa Ke Ciki Da Wasu Sassa Daban-daban Na Duniya, Mun Gode

“Mun ba hukumomin tsaro umarnin gaggawa su kawo ƙarshen matsalar tsaro a Zamfara. Ba sai an jira umarni daga sama ba, do...
14/11/2025

“Mun ba hukumomin tsaro umarnin gaggawa su kawo ƙarshen matsalar tsaro a Zamfara. Ba sai an jira umarni daga sama ba, domin mu ma daga nan muna bayarwa, kuma mun riga mun bayar.” — Minista Matawalle.

Shin a ra’ayinku, wane muhimmin mataki ya fi dacewa a dauka domin ganin an shawo kan matsalar tsaro a Jihar Zamfara da Arewa cikin gaggawa?

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya amince da sabunta nadin Birgediya Janar Mohammed Buba Marwa (Rtd.) a matsayin Shugaba...
14/11/2025

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya amince da sabunta nadin Birgediya Janar Mohammed Buba Marwa (Rtd.) a matsayin Shugaban Hukumar NDLEA na wa’adin shekaru biyar, k**ar yadda wata sanarwa daga Fadar Shugaban Ƙasa ta bayyana a ranar Juma’a.

Marwa, wanda aka fara nada shi shugaban hukumar a 2021 a lokacin tsohon Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari, ya yi aiki a baya a matsayin Shugaban Kwamitin Shugaban Ƙasa kan Yaki da Shan Miyagun Kwayoyi tsakanin 2018 zuwa 2020. Sabon wa’adin da aka amince da shi yanzu zai tsawaita shugabancinsa har zuwa 2031.

Tsohon gwamnan jihohin Lagos da Borno, Marwa ya samu manyan horo na soja a Nigerian Military School da kuma Nigerian Defence Academy. Ya rike muhimman muk**ai a rundunar sojin Najeriya, ciki har da zama Brigade Major na 23 Armoured Brigade da kuma Aide-de-Camp ga tsohon Babban Hafsan Sojin Najeriya, Laftanar Janar Theophilus Danjuma (Rtd.).

Haka kuma ya kasance Mataimakin mai ba da shawara kan tsaro a Jakadancin Najeriya da ke Washington DC, tare da zama mai ba da shawara kan tsaro ga wakilan Najeriya a Majalisar Dinkin Duniya. Marwa na da digiri na biyu a Public and International Affairs daga Jami’ar Pittsburgh, da kuma Master of Public Administration daga Jami’ar Harvard.

A wa’adin sa na farko, NDLEA ta samu manyan nasarori, ciki har da k**a sama da mutane 73,000 da ake zargi da safarar kwayoyi, da kwace miyagun kwayoyi da nauyinsu ya haura kilo miliyan 15. Hakanan hukumar ta aiwatar da gagarumin aikin wayar da kan jama’a game da illolin shan kwayoyi a fadin ƙasar.

Shugaba Tinubu, yayin bayyana jin daɗinsa kan aikin Marwa, ya ce sabunta nadin wata shaida ce ta amincewarsa da jajircewar shugaban NDLEA wajen yaƙi da fataucin miyagun kwayoyi.

“Ina kira gare ka da ka ci gaba da nuna jajircewa wajen fatattakar ’yan damfara da masu safarar kwayoyi da ke barazana ga makomar al’umma, musamman matasa,” in ji shugaban ƙasar.

Fara'a tv

YANZU-YANZU: Babbar Kotun Tarayya ta ba da umarni cewa a bai wa Sule Lamido damar sayen fom da kuma shiga tantancewa dom...
14/11/2025

YANZU-YANZU: Babbar Kotun Tarayya ta ba da umarni cewa a bai wa Sule Lamido damar sayen fom da kuma shiga tantancewa domin takarar Shugaban Jam’iyyar PDP na kasa.

Alkalin kotun, Justice Peter Life, ya kuma hana PDP ci gaba da shirye-shiryen gudanar da babban taronta na kasa, inda ya ce duk wani taro da aka yi ba tare da biyayya ga wannan hukunci ba, zai zama bai inganta ba.

A daidai wannan lokacin kuma PDP na can tana shirin taronta a gobe Asabar duk da umarnin hani da kotun ta yi .

Kungiyar Malaman Jami’o’i ta ƙasa (ASUU) ta ja kunnen Gwamnatin Tarayya da ta yi amfani da kwanaki 10 da s**a rage cikin...
14/11/2025

Kungiyar Malaman Jami’o’i ta ƙasa (ASUU) ta ja kunnen Gwamnatin Tarayya da ta yi amfani da kwanaki 10 da s**a rage cikin wa’adin wata guda da aka ba ta, domin warware dukkan batutuwan da s**a jima suna dagule tsarin jami’o’i a ƙasar.

Gargadin ya fito ne bayan zaman Majalisar Zartarwar Ƙasa ta ASUU da aka gudanar a Jami’ar Taraba da ke Jalingo tsakanin 8 zuwa 9 ga Nuwamba.

A cikin sanarwar da Shugaban ASUU, Farfesa Chris Piwuna ya fitar, ya zargi wasu jami’an gwamnati da yin kalaman da ke karkatar da sahihin yanayin tattaunawa, tare da bayyana abubuwan da ba su wakilci ainihin tayin gwamnati ko matsayinta kan aiwatar da yarjejeniya ba.

ASUU ta dakatar da yajin aikin gargadi na makonni biyu a ranar 22 ga Oktoba, har zuwa 22 ga Nuwamba domin gwamnata ta cika manyan bukatunta, ciki har da sabunta yarjejeniyar 2009, biyan albashi da alawus-alawus da s**a tsaya, da sakin kudaden farfado da jami’o’i.

Kungiyar ta gargadi cewa za ta dawo kan yajin aiki ba tare da sanarwa ba idan gwamnati ta gaza ɗaukar matakan da s**a dace.

Piwuna ya ce biyan rabi na bashin karin girma tun daga 2017 da kuma sakin kudaden cirewa na bangarori na uku ba su daga cikin muhimman batutuwan da ake tattaunawa, sai dai matakan da ke ƙara kwarin gwiwa ne kawai. Ya bayyana cewa ko da yake an samu ci gaba a wasu fannoni marasa alaka da kudi, batun albashi da walwalar malamai na bukatar matakin da ya fi ƙarfin tsohuwar dabara.

ASUU ta jaddada cewa babban kalubalen shi ne rashin niyyar gwamnati wajen bai wa ilimi muhimmanci, tana mai cewa malamai sun cancanci yanayin aiki da rayuwa mafi inganci.

Fara'a tv

Hotuna: yadda dandazon al'umma s**a karbi gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf a lokacin da ya halarci sallar Jumma'a a m...
14/11/2025

Hotuna: yadda dandazon al'umma s**a karbi gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf a lokacin da ya halarci sallar Jumma'a a masallacin jami'ar Northwest.

Hotuna: Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Mohammed Idris, ya halarci taron Talla na Ƙasa karo na biyar da Hukumar K...
14/11/2025

Hotuna: Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Mohammed Idris, ya halarci taron Talla na Ƙasa karo na biyar da Hukumar Kula da Talla ta Najeriya ( Advertising Regulatory Council of Nigeria - ARCON) ta shirya, a ranar 13 ga Nuwamba 2025, a Abuja.”

Birnin Gusau ya cika ya tumbatsa, yayin da al'umma s**a mamaye tituna wajen tarbar Minista Bello MatawalleMutane ba adad...
14/11/2025

Birnin Gusau ya cika ya tumbatsa, yayin da al'umma s**a mamaye tituna wajen tarbar Minista Bello Matawalle

Mutane ba adadi, amma masu kiyasi sun ce sun kai kusan miliyan biyu, ko ma fiye, s**a cika titunan Gusau, babban birnin jihar Zamfara a yayin wata gagarumar tarbar da ba a saba ganin irinta ba, mai cike da dumbin tarihi ga Dr Bello Mohammed Matawalle, Minista a ma'aikatar tsaron Nijeriya kuma tsohon Gwamnan jihar Zamfara.

Wakilinmu ya rawaito cewa birnin ya cika da jama’a daga ko’ina, tun daga shatale-talen roundabout zuwa filayen kasuwanni, inda maza, mata, matasa, dattawa ke ta tururuwar amsa kiran dan baiwa. Yana shiga birnin na Gusau, kowa ya dauka da tafi da jinjina ana murna cike da shaukin ganin masoyi.

Magoya bayansa sun ce wannan tarba ta samo asali ne daga ayyukan da Matawalle ya gudanar lokacin yana gwamna. Sun ambaci aikin gyaran manyan hanyoyi da ya buɗe sabbin damarmakin kasuwanci, ginin sabon filin jirgin saman Gusau, ƙara samar da ruwan sha ta hanyar rijiyoyin burtsatse, da gyaran cibiyoyin kiwon lafiya da s**a taimaka wa jama’a. Haka kuma sun jingina ma ƙoƙarinsa na inganta tsaro ta hanyar samar da motocin aiki da kayan tallafi ga jami’an tsaro. Ga yawancin al'ummar jihar, waɗannan ayyuka ba alkawari ba ne kawai na shaci-fadi, sun ce abubuwa ne da s**a gani a aikace, muraran.

Yayin da ayarin motocin Minista Matawalle s**a shiga birnin, jama’a s**a cika hanyoyi. Mata sun yi layi a gefen hanya suna waƙoki na yabo da jinjina. Matasa sun yi dogon jerin gwano suna binsa cike da shauki da kauna. Tsofaffi suna daga hannaye suna addu’o'i ga Minista Matawalle. ’Yan kasuwa sun bar shaguna, dalibai suna hawa kan motocin mutane suna daga tutoci, jama’a kuma suna kiran sunansa ba kakkautawa. Bayanai sun ce birnin Gusau bai ta ganin irin wannan farin ciki ba tsawon shekaru sai a wannan lokacin da Matawalle ya yi wannan ziyara.

Wasu shugabannin siyasa da na al’umma sun ce wannan tarba shaida ce ta sake amincewar jama’a da shi. Sun bayyana cewa ba a samun irin wannan taron jama’a sai ga shugaba da ya tabo rayuwar mutane. A wurin taron an ji wasu na cewa har yanzu Matawalle shi ne ɗaya daga cikin manyan ’yan siyasa masu tasiri a jihar.

A cewarsu, irin wannan goyon baya da farin jini yana nuna cewa Matawalle zai iya sake tallafa wa Shugaba Bola Ahmed Tinubu a zaɓen shekarar 2027, k**ar yadda suke ganin ya yi a baya. Magoya bayan sun furta wadannan kalamai a wurare daban-daban a cikin birnin cewa wannan fitar farin dango da al'umma s**a yi, ya nuna yadda har yanzu jama'ar jihar ke ci gaba da nuna aminci da soyayya ga Matawalle.

Abin da ya faru a Gusau ya zarce tarba kaɗai. Alama ce ta nuna godiya daga mazauna da ke ganin ayyukan Matawalle sun taimaka wajen sauya jiharsu. An karkare da saƙo guda: Mutanen Gusau har yanzu suna tare da Bello Mohammed Matawalle saboda suna ganin ya yi musu aiki lokacin da ya fi muhimmanci.

14/11/2025

Kai tsaye: yadda Taron da Ministan Tsaro, Bello Matawalle, ke jagoranta tare da manyan jiga-jigai na jam’iyyar APC a Jihar Zamfara ke gudana yanzu haka.

Daukar nauyi: Jam’iyyar APC ta Jihar Zamfara.

13/11/2025

Kai tsaye: yadda al'ummar Zamfara s**a tarbi Dr Bello Matawalle, a wata ziyarar da ya kai jihar

Address

Government House Gusau
Gusau
3337

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Fara'a tv posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Fara'a tv:

Share

Category