Fara'a tv

Fara'a tv A tuntubemu 08133376020/08164949696
(2)

Fara'a Tv tasha ce dake karkashin Kamfanin Fara'a Media Services Ltd da ke kawo muku ingantattun labarai daga kowace kusurwa a faɗin duniya ba tare da nuna wariya ko banbancin addini ko kabilanci ba. Faraa TV Na Maraba Da Ku, Ku Ci Gaba Da Kasancewa Da Mu A Kowane Lokaci Domin Sanin Halin Da Kasa Ke Ciki Da Wasu Sassa Daban-daban Na Duniya, Mun Gode

Jagorar Matan APC Ta Arewa Ta Tsakiya Ta Miƙa Motar “Tinubu Torchbearers” Ga Gwamna SuleJagorar Matan Jam’iyyar APC ta s...
07/06/2026

Jagorar Matan APC Ta Arewa Ta Tsakiya Ta Miƙa Motar “Tinubu Torchbearers” Ga Gwamna Sule

Jagorar Matan Jam’iyyar APC ta shiyyar Arewa ta Tsakiya, Esther Samuel Alu, ta miƙa motar “Tinubu Torchbearers” ga Gwamnan Jihar Nasarawa, Abdullahi A. Sule, a wani taro da ya gudana domin ƙarfafa ayyukan siyasa a matakin ƙasa.

An bayyana cewa Uwargidan Shugaban Ƙasa, Oluremi Tinubu, ce ta bai wa Dr. Alu motar a matsayin wani ɓangare na shirin raba kayayyakin tallafi ga jagororin mata na jam’iyyar APC a sassa daban-daban na ƙasar nan.

Shirin na da manufar ƙarfafa mata masu ruwa da tsaki a harkokin siyasa tare da bunƙasa wayar da kan jama'a da kuma tattara goyon baya ga manufofin jam’iyyar daga matakin ƙasa har zuwa tushe.

Da take jawabi yayin miƙa motar, Dr. Alu ta ce tallafin wata alama ce ta ƙudurin shugabancin jam’iyyar na bai wa mata damar taka muhimmiyar rawa wajen gina jam’iyya da ƙarfafa dimokuraɗiyya.

A nasa ɓangaren, Gwamna Abdullahi Sule ya yabawa wannan yunƙuri, yana mai cewa zai taimaka wajen ƙara haɗa kan mambobin jam’iyyar da kuma inganta ayyukan siyasa ga al’umma.

Rundunar ’Yan Sandan Jihar Edo ta ce ta k**a wani mutum mai suna Uzebor Emmanuel, wanda aka fi sani da “Aza Woman” a kaf...
07/06/2026

Rundunar ’Yan Sandan Jihar Edo ta ce ta k**a wani mutum mai suna Uzebor Emmanuel, wanda aka fi sani da “Aza Woman” a kafafen sada zumunta, bisa zargin yaɗa rahoton ƙarya cewa an sace wasu ɗalibai a wasu makarantu da ke Birnin Benin.

A cewar ’yan sandan, wanda ake zargin ya wallafa wani bidiyo da ya yaɗu a intanet, inda ya yi ikirarin cewa wasu masu garkuwa da mutane sun kutsa cikin makarantun Green Park Academy da Western Boys’ College tare da yin awon gaba da ɗalibai.

Sai dai rundunar ta ce binciken farko da ta gudanar ya nuna cewa babu wani harin sace ɗaliban da ya faru a makarantun da aka ambata.

’Yan sandan sun bayyana cewa an k**a wanda ake zargin ne domin ci gaba da bincike, yayin da s**a gargadi jama'a kan illar yaɗa bayanan da ba a tabbatar da sahihancinsu ba.

Tsohon tauraron ƙwallon ƙafa na ƙungiyoyin Real Madrid da Manchester United, David Beckham, ya bayyana cewa yana ganin I...
07/06/2026

Tsohon tauraron ƙwallon ƙafa na ƙungiyoyin Real Madrid da Manchester United, David Beckham, ya bayyana cewa yana ganin Ingila ce ke da mafi kyawun damar lashe gasar cin kofin duniya ta FIFA ta 2026.

Mataimakiyar Gwamnan Kaduna Ta Wakilci Uba Sani a Gasar Polo ta Sadaka ta Access Bank da UNICEFMataimakiyar Gwamnan Jiha...
07/06/2026

Mataimakiyar Gwamnan Kaduna Ta Wakilci Uba Sani a Gasar Polo ta Sadaka ta Access Bank da UNICEF

Mataimakiyar Gwamnan Jihar Kaduna, Hadiza Sabuwa Balarabe, ta wakilci Gwamna Uba Sani a matsayin babbar baƙuwar girmamawa a Gasar Polo ta Sadaka ta 2026 da haɗin gwiwar Access Bank da UNICEF s**a shirya.

An gudanar da taron ne a Fifth Chukker Polo and Country Club da ke Maraban Jos a Jihar Kaduna, inda ya samu halartar manyan baƙi daga sassa daban-daban na ƙasar nan. Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, ya samu wakilcin Mataimakin Shugaban Ma’aikatansa, Ibrahim Hassan Hadejia.

Daga cikin fitattun waɗanda s**a halarci taron akwai Kakakin Majalisar Wakilai, Tajuddeen Abbas, Gwamnan Jihar Neja, Umaru Mohammed Bago, da Sarkin Katsina, Abdulmumini Kabir Usman.

Gasar, wadda ta fara ne ranar 30 ga Mayu kuma ake sa ran kammala ta a ranar 7 ga Yuni, ta zama wata muhimmiyar kafa ta tattara tallafi domin shirye-shiryen UNICEF na inganta rayuwa da walwalar yara masu buƙata a Najeriya, tare da ƙarfafa ruhin wasanni da haɗin kai a tsakanin al’umma.

Gwamna Bala Mohammed Ya Kai Ziyarar Ta’aziyya Lanzai Bayan Rikicin da Ya Yi Sanadin Asarar RayukaGwamnan Jihar Bauchi, B...
07/06/2026

Gwamna Bala Mohammed Ya Kai Ziyarar Ta’aziyya Lanzai Bayan Rikicin da Ya Yi Sanadin Asarar Rayuka

Gwamnan Jihar Bauchi, Bala Abdulkadir Mohammed, ya kai ziyarar ta’aziyya garin Lanzai da ke Ƙaramar Hukumar Darazo, bayan rikicin da ya ɓarke tsakanin al’ummomin Lanzai da Dosho wanda ya yi sanadin asarar rayuka da lalata dukiyoyi.

Yayin da yake jajanta wa waɗanda lamarin ya shafa, gwamnan ya bayyana rikicin a matsayin abin takaici da bai dace ya faru ba, musamman ganin cewa al’ummomin biyu suna da alaƙa ta kabila da addini. Ya ce gwamnati ba za ta yi ƙasa a gwiwa ba wajen tabbatar da adalci da dawo da zaman lafiya mai ɗorewa a yankin.

Gwamna Bala Mohammed ya sanar da kafa kwamitin bincike domin gano musabbabin rikicin tare da zakulo waɗanda ke da hannu a tashin hankalin. Ya kuma yi gargadin cewa duk wanda aka samu da hannu wajen tayar da rikicin zai fuskanci hukunci bisa tanadin doka.

Hakazalika, ya umarci hukumomin tsaro da su ci gaba da kasancewa a yankunan da abin ya faru domin tabbatar da cikakken kwanciyar hankali, tare da bayar da tallafi ga iyalan waɗanda abin ya rutsa da su.

A nasa bangaren, Kwamishinan ’Yan Sandan Jihar Bauchi, Sani Aliyu-Omolori, ya ce an samu nasarar dawo da zaman lafiya a yankin, yana mai jaddada muhimmancin haɗin gwiwa tsakanin hukumomin tsaro da shugabannin al’umma wajen dakile irin waɗannan rikice-rikice a nan gaba.

07/06/2026

Sako cikin bidiyo

Dakarun Soji Sun Ceto Mutane 360 Daga Hannun Boko Haram a Dutsen MandaraDakarun rundunar haɗin gwiwa ta Operation Hadin ...
07/06/2026

Dakarun Soji Sun Ceto Mutane 360 Daga Hannun Boko Haram a Dutsen Mandara

Dakarun rundunar haɗin gwiwa ta Operation Hadin Kai sun sanar da ceto mutane 360 da aka yi garkuwa da su daga wani sansanin mayaƙan Boko Haram da ke cikin tsaunukan Mandara a kudancin jihar Borno.

A cewar rundunar, aikin ceton ya kasance ɗaya daga cikin manyan hare-haren ceto da aka gudanar a yankin Arewa maso Gabas cikin 'yan shekarun nan, bayan shafe makonni ana tattara bayanan sirri da kuma sa ido kan motsin mayaƙan ƙungiyar.

Mutanen da aka ceto sun haɗa da maza, mata da yara da aka sace daga wasu al'ummomi, musamman yankin Ngoshe, inda s**a shafe lokaci mai tsawo a hannun mayaƙan cikin mawuyacin hali.

Rundunar ta bayyana cewa nasarar aikin ta samo asali ne daga haɗa bayanan sirri daga mabambantan hanyoyi da s**a haɗa da bayanan jama'a, sa ido ta na'urorin zamani da kuma sintirin leƙen asiri a yankunan da mayaƙan ke buya.

Bayanan da aka tattara sun bai wa dakarun damar gano ainihin wurin da mutanen suke tare da fahimtar tsarin tsaron sansanin, hanyoyin shiga da fita, da kuma yadda mayaƙan ke gudanar da harkokinsu.

A cewar rundunar, jami'an leƙen asiri sun samu nasarar kutsawa cikin wajan mayaƙan, lamarin da ya ba su damar samun muhimman bayanai kan wuraren da aka ajiye waɗanda aka sace da kuma yadda mayaƙan ke shirya sauya musu matsuguni.

Bayan tabbatar da sahihancin bayanan, dakarun runduna ta musamman da sojojin sashe na 1 s**a ƙaddamar da farmaki daga bangarori daban-daban cikin dare domin kewaye sansanin da kuma hana mayaƙan tserewa.

Rahoton ya ce harin ya zo wa mayaƙan da bazata, inda da dama daga cikinsu s**a tsere zuwa cikin tsaunuka yayin da wasu s**a miƙa wuya ga dakarun.

An yi gaggawar fitar da waɗanda aka ceto tare da yi musu gwajin lafiya kafin kai su wuraren da za su samu kulawa da tallafin jin kai.

Sai dai rundunar ta bayyana cewa jarirai biyu sun rasu sak**akon gajiya da kuma wahalhalun da s**a sha a lokacin da suke tsarewa a hannun mayaƙan, da kuma ƙalubalen da aka fuskanta yayin ficewa daga yankin tsaunukan.

Babban hafsan sojoji ya yaba da jajircewa, ƙwarewa da kuma ladabin da dakarun da s**a gudanar da aikin s**a nuna, yana mai cewa nasarar ta sake nuna ƙarfin dabarun tattara bayanan sirri da kuma ƙudirin sojojin Najeriya na kare rayuka da dukiyoyin al'umma.

Rundunar ta kuma tabbatar da cewa tana ci gaba da gudanar da wasu ayyuka domin bibiyar mayaƙan da s**a tsere, rushe ragowar sansanoninsu da kuma hana sake aukuwar irin waɗannan hare-haren sace mutane a nan gaba.

06/06/2026

Mabuɗin kunne!

Kwamitin Tsabtace Muhalli na Zamfara Ya Kammala Aikin Wannan Wata, Ya K**a Masu Karya DokaKwamitin Tsabtace Muhalli na J...
06/06/2026

Kwamitin Tsabtace Muhalli na Zamfara Ya Kammala Aikin Wannan Wata, Ya K**a Masu Karya Doka

Kwamitin Tsabtace Muhalli na Jihar Zamfara ƙarƙashin jagorancin Hon. Muhammad Zangina Abdullahi (Yarin Gusau) ya bayyana kammala aikin tsaftar muhalli na wannan wata, tare da ci gaba da aiwatar da dokokin da s**a shafi tsafta da kare muhalli a faɗin birnin Gusau.

A yayin gudanar da aikin tsaftar muhalli na watan nan a ranar Asabar, jami’an kwamitin sun ci gaba da sintiri da sa ido domin tabbatar da bin dokokin muhalli da na hanyoyi, inda s**a k**a wasu da ake zargi da karya ƙa’idojin da kwamitin ya gindaya.

Shugaban kwamitin, Hon. Muhammad Zangina Abdullahi, ya jaddada aniyar kwamitin na ci gaba da tabbatar da tsafta da kyawun muhalli a faɗin jihar, yana mai gargadin masu karya doka da su guji aikata duk wani abu da zai iya gurbata muhalli ko karya dokokin tsafta.

Ya kuma yabawa mazauna Gusau da sauran al’ummomin jihar da ke bada haɗin kai wajen tabbatar da tsaftataccen muhalli, yana mai cewa kare muhalli nauyi ne da ya rataya a wuyan kowa domin inganta lafiyar al'umma da bunƙasa ci gaban jihar.

Al’ummar Jumrawa Sun Jinjinawa Rundunar ’Yan Sanda a Zamfara Kan Inganta TsaroAl’ummar yankin Jumrawa da ke jihar Zamfar...
06/06/2026

Al’ummar Jumrawa Sun Jinjinawa Rundunar ’Yan Sanda a Zamfara Kan Inganta Tsaro

Al’ummar yankin Jumrawa da ke jihar Zamfara sun yabawa Rundunar ’Yan Sandan jihar bisa irin nasarorin da ta samu wajen inganta tsaro da tabbatar da zaman lafiya a yankin.

Wannan na kunshe ne a wata ziyara ta bangirma da shugabanni da wakilan al’ummar yankin s**a kai wa Kwamishinan ’Yan Sandan Jihar Zamfara, CP Ahmad Muhammad Bello, a hedikwatar rundunar da ke Gusau ranar Juma’a.

A yayin ziyarar, wakilan al’ummar sun bayyana gamsuwarsu da yadda rundunar ke gudanar da ayyukanta, musamman ta fuskar dakile laifuka da kuma ɗaukar matakan kariya kafin aikata su. Sun ce waɗannan matakai sun taimaka wajen samar da zaman lafiya da kwanciyar hankali, tare da bai wa mazauna yankin damar gudanar da harkokinsu na yau da kullum cikin walwala.

Da yake magana a madadin tawagar, shugaban al’ummar ya ce ƙoƙarin da rundunar ke yi na yaƙi da masu aikata laifuka ya haifar da gagarumin sauyi a yankin, inda ya jaddada cewa jama’a na ci gaba da amfana da yanayin tsaron da aka samu.

Tawagar ta kuma yi alƙawarin ci gaba da bai wa jami’an tsaro haɗin kai, musamman wajen samar da sahihan bayanan sirri da za su taimaka wajen kare wannan ci gaba da aka samu a fannin tsaro.

A nasa jawabin, Kwamishinan ’Yan Sandan Jihar Zamfara, CP Ahmad Muhammad Bello, ya gode wa al’ummar yankin kan wannan ziyara, yana mai cewa irin wannan haɗin gwiwa tsakanin jama’a da jami’an tsaro na da matuƙar muhimmanci wajen yaƙi da miyagun laifuka.

Ya tabbatar da cewa rundunar za ta ci gaba da aiwatar da matakan kare rayuka da dukiyoyin al’umma tare da tabbatar da doka da oda a faɗin jihar. Haka kuma ya buƙaci jama’a su kasance masu sa ido tare da ci gaba da bai wa hukumomin tsaro bayanai cikin gaggawa idan s**a lura da duk wani abu da zai iya zama barazana ga zaman lafiya.

Address

Government House Gusau
Gusau
3337

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Fara'a tv posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Fara'a tv:

Share

Category