07/06/2026
Dakarun Soji Sun Ceto Mutane 360 Daga Hannun Boko Haram a Dutsen Mandara
Dakarun rundunar haɗin gwiwa ta Operation Hadin Kai sun sanar da ceto mutane 360 da aka yi garkuwa da su daga wani sansanin mayaƙan Boko Haram da ke cikin tsaunukan Mandara a kudancin jihar Borno.
A cewar rundunar, aikin ceton ya kasance ɗaya daga cikin manyan hare-haren ceto da aka gudanar a yankin Arewa maso Gabas cikin 'yan shekarun nan, bayan shafe makonni ana tattara bayanan sirri da kuma sa ido kan motsin mayaƙan ƙungiyar.
Mutanen da aka ceto sun haɗa da maza, mata da yara da aka sace daga wasu al'ummomi, musamman yankin Ngoshe, inda s**a shafe lokaci mai tsawo a hannun mayaƙan cikin mawuyacin hali.
Rundunar ta bayyana cewa nasarar aikin ta samo asali ne daga haɗa bayanan sirri daga mabambantan hanyoyi da s**a haɗa da bayanan jama'a, sa ido ta na'urorin zamani da kuma sintirin leƙen asiri a yankunan da mayaƙan ke buya.
Bayanan da aka tattara sun bai wa dakarun damar gano ainihin wurin da mutanen suke tare da fahimtar tsarin tsaron sansanin, hanyoyin shiga da fita, da kuma yadda mayaƙan ke gudanar da harkokinsu.
A cewar rundunar, jami'an leƙen asiri sun samu nasarar kutsawa cikin wajan mayaƙan, lamarin da ya ba su damar samun muhimman bayanai kan wuraren da aka ajiye waɗanda aka sace da kuma yadda mayaƙan ke shirya sauya musu matsuguni.
Bayan tabbatar da sahihancin bayanan, dakarun runduna ta musamman da sojojin sashe na 1 s**a ƙaddamar da farmaki daga bangarori daban-daban cikin dare domin kewaye sansanin da kuma hana mayaƙan tserewa.
Rahoton ya ce harin ya zo wa mayaƙan da bazata, inda da dama daga cikinsu s**a tsere zuwa cikin tsaunuka yayin da wasu s**a miƙa wuya ga dakarun.
An yi gaggawar fitar da waɗanda aka ceto tare da yi musu gwajin lafiya kafin kai su wuraren da za su samu kulawa da tallafin jin kai.
Sai dai rundunar ta bayyana cewa jarirai biyu sun rasu sak**akon gajiya da kuma wahalhalun da s**a sha a lokacin da suke tsarewa a hannun mayaƙan, da kuma ƙalubalen da aka fuskanta yayin ficewa daga yankin tsaunukan.
Babban hafsan sojoji ya yaba da jajircewa, ƙwarewa da kuma ladabin da dakarun da s**a gudanar da aikin s**a nuna, yana mai cewa nasarar ta sake nuna ƙarfin dabarun tattara bayanan sirri da kuma ƙudirin sojojin Najeriya na kare rayuka da dukiyoyin al'umma.
Rundunar ta kuma tabbatar da cewa tana ci gaba da gudanar da wasu ayyuka domin bibiyar mayaƙan da s**a tsere, rushe ragowar sansanoninsu da kuma hana sake aukuwar irin waɗannan hare-haren sace mutane a nan gaba.