Fara'a tv

Fara'a tv A tuntubemu 08133376020/08164949696
(1)

Fara'a Tv tasha ce dake karkashin Kamfanin Fara'a Media Services Ltd da ke kawo muku ingantattun labarai daga kowace kusurwa a faɗin duniya ba tare da nuna wariya ko banbancin addini ko kabilanci ba. Faraa TV Na Maraba Da Ku, Ku Ci Gaba Da Kasancewa Da Mu A Kowane Lokaci Domin Sanin Halin Da Kasa Ke Ciki Da Wasu Sassa Daban-daban Na Duniya, Mun Gode

Rundunar Sojin Najeriya ta ce dakarun Operation MESA da s**a haɗa da jami’an Sojin Sama da ’yan sanda sun ceto mutane ba...
30/11/2025

Rundunar Sojin Najeriya ta ce dakarun Operation MESA da s**a haɗa da jami’an Sojin Sama da ’yan sanda sun ceto mutane bakwai da aka yi garkuwa da su a ƙauyen Yank**aye Cikin Gari da ke cikin ƙaramar hukumar Tsanyawa, Jihar Kano.

Lamarin ya faru da misalin ƙarfe 11 na dare a ranar 29 ga Nuwamba, bayan samun kiran gaggawa kan farmakin ’yan bindiga a yankin. Rundunar ta ce an tarar da cewa maharan sun kashe wata mata mai shekaru 60 kafin isowar jami’an tsaro.

Dakarun da s**a bi sawun ’yan bindigar zuwa hanyar Rimaye sun yi musayar wuta da su, inda s**a ƙwato mutanen bakwai da aka sace. Sai dai rundunar ta ce mutane huɗu da aka yi garkuwa da su har yanzu ba a san inda suke ba.

Rundunar ta bayyana cewa maharan sun tsere ne zuwa ƙaramar hukumar Kankia ta Jihar Katsina, kuma ana ci gaba da neman su.

Kwamandan runduna ta 3 ya yaba wa dakarun kan jajircewarsu, tare da kiran jama’a da su ci gaba da bai wa hukumomin tsaro bayanai cikin lokaci domin inganta ayyukan farfado da tsaro.

30/11/2025

Shugaban Daliban Zamfara ya ce sauye-sauyen da s**a aiwatar sun haifar da sak**ako

Ministan kasa a ma'aikatar tsaron Nijeriya kuma tsohon gwamnan jihar Zamfara, Dr. Bello Muhammed Matawalle, ya ziyarci ’...
30/11/2025

Ministan kasa a ma'aikatar tsaron Nijeriya kuma tsohon gwamnan jihar Zamfara, Dr. Bello Muhammed Matawalle, ya ziyarci ’yan kasuwa 'yan asalin jihar Zamfara da s**a yi asarar shaguna sak**akon gobarar da ta tashi a Kasuwar Panteka da ke Apo, Abuja, a ranar Asabar 29 ga watan Nuwamba.

Sanarwar da mai taimaka wa ministan kan harkokin yaɗa labarai, Ahmad Dan-Wudil, ya fitar ta tabbatar da ziyarar, inda ya ce gobarar ta ƙone fiye da shaguna 400 da dakuna da dama tare da lalata dukiyoyi da darajarsu ta kai miliyoyin Naira.

Shugaban ’yan kasuwar ‘yan asalin jihar Zamfara, Umar Sahabi Kaura-Namoda, ya bayyana ziyarar a matsayin abin tarihi, yana mai cewa ba a taɓa samun wani babban jami’in gwamnati daga Zamfara da ya ziyarci ’yan kasuwar a irin wannan mawuyacin lokaci ba tsawon shekaru 20 da s**a gabata.

A jawabin sa ga ’yan kasuwar, Matawalle ya jajanta musu bisa asarar da s**a yi, tare da yin addu’ar Allah ya tsare su daga irin wannan masifa a nan gaba.

Haka kuma, ya bayar da tallafin zunzurutun kudi naira miliyan 20 domin rage musu radadin asara da kuma taimaka musu su a wannan mawuyacin lokaci.

Dubban Mutane Sun Hallara a Turai da New York Don Bayar da Goyon Baya ga Palestine. Dubban mutane sun fito tituna a many...
30/11/2025

Dubban Mutane Sun Hallara a Turai da New York Don Bayar da Goyon Baya ga Palestine.

Dubban mutane sun fito tituna a manyan biranen Turai da New York a Ranar Goyon Bayan ‘Yan Palestine ta duniya, suna ɗauke da tutocin Palestinu, rera waƙoƙi da taken zanga-zanga, da rike allunan nuna adawa da goyon bayan siyasa da na soja da gwamnatocinsu ke bai wa Isra’ila, tare da kiran dakatar da harbe-harbe nan take, samar da agajin jin kai ga Gaza, da neman adalci ga fararen hula na Palestinu yayin da rikicin ke kara tsananta a yankin.

Rundunar Sojin Najeriya ta 6 Brigade da ke ƙarƙashin Operation Peace Shield ta tabbatar da kashe ’yan ta’adda hudu a wan...
30/11/2025

Rundunar Sojin Najeriya ta 6 Brigade da ke ƙarƙashin Operation Peace Shield ta tabbatar da kashe ’yan ta’adda hudu a wani samame da ta kai a kauyen Usmanu, cikin ƙaramar hukumar Karim Lamido, Jihar Taraba.

Lamarin ya biyo bayan rikicin filaye da ya ɓarke tsakanin al’ummomin Shomo da Wurkun, wanda ya janyo kona gidaje da tashin hankali a yankin.

Sojojin da s**a isa yankin Fadama sun yi arangama da maharan, kafin su mayar da martani su tarwatsa su. Rundunar ta ce an kwato bindigogi uku na gargajiya, wata AK-47 da aka ƙera a gida, harsasai 25 na 7.62mm da babura biyu.

An kuma k**a wani jami’in ’yan sanda da ake zargi da taimaka wa ’yan bindigar.

Kwamandan 6 Brigade, Manjo Janar Kingsley Chidiebere Uwa, ya ce rundunar za ta ci gaba da ayyukan farfado da zaman lafiya a fadin Taraba, tare da tabbatar da cewa duk masu tayar da hankali za su fuskanci hukunci.

Uwargidan Shugaban Ƙasa ta yi kira ga ’yan majalisa su amince da kudirin kara wa mata kujeruSanata Asuquo Ekpenyong, dag...
30/11/2025

Uwargidan Shugaban Ƙasa ta yi kira ga ’yan majalisa su amince da kudirin kara wa mata kujeru

Sanata Asuquo Ekpenyong, daga jihar Cross River ya ce ya halarci taron cin abinci na musamman da Uwargidan Shugaban Ƙasa, Sanata Oluremi Tinubu, ta shirya wa mambobin Majalisar Dokoki a Banquet Hall da ke Fadar Shugaban Ƙasa.

A cewarsa, Uwargidan Shugaban Ƙasa ta yi amfani da taron wajen sake jaddada bukatar amincewa da Kudirin Daidaito tsakanin Jinsi wajen samun kujeru, wanda ke neman tanadar da kujeru na musamman ga mata a majalisar dokoki. Ta ce hakan zai taimaka wajen kara wa mata damar shiga harkokin dimokuraɗiyya yadda ya k**ata.

Taron ya samu halartar Mataimakin Shugaban Ƙasa Kashim Shettima, Shugaban Majalisar Dattawa Godswill Akpabio, Kakakin Majalisar Wakilai Rt. Hon. Tajudeen Abbas, Shugaban jam’iyyar APC Farfesa Nentawe Goshwe Yilwatda da Gwamna Hope Uzodinma, tare da wasu manyan jami’an gwamnati da ’yan majalisa.

Sanata Ekpenyong ya ce taron ya ba da damar tunani da tattaunawa kan yadda za a inganta tsarin dimokuraɗiyya. Ya kuma tabbatar da goyon bayansa ga duk wani yunƙuri da ke ƙara wa mata damar shiga siyasa da kuma ƙarfafa tsarin mulkin Najeriya.

Hotuna: yadda Rundunar Sojin Ruwa ta Najeriya ƙarƙashin Operation DELTA SANITY II, ta samu nasarar bankadowa tare da tar...
30/11/2025

Hotuna: yadda Rundunar Sojin Ruwa ta Najeriya ƙarƙashin Operation DELTA SANITY II, ta samu nasarar bankadowa tare da tarwatsa wurin boye ɗanyen man fetur a yankin Oteghele Creek, dake jihar Delta.

30/11/2025

Bidiyo Mai Taba Zuciya: Hawaye da Farin Ciki Yayin da ’Yan Mata 12 S**a Kuɓuta a Borno

30/11/2025

Yadda gwamna Dauda Lawal yazuba ayukkan Sama da naira biliyan 10 a karamar hukumar mulkin Anka

30/11/2025

Yadda gwamnatin jihar zamfara ta sabunta masarautar Anka

Sojojin Najeriya sun ceto ƴan mata 12 da aka sace a Askira/Uba dake Jihar BornoRundunar Sojojin Najeriya ta ceto wasu ƴa...
29/11/2025

Sojojin Najeriya sun ceto ƴan mata 12 da aka sace a Askira/Uba dake Jihar Borno

Rundunar Sojojin Najeriya ta ceto wasu ƴan mata 12 da ƴan Boko Haram/ISWAP s**a sace a yankin M***a da ke ƙaramar hukumar Askira/Uba, a jihar Borno.

Ƴan matan, masu shekaru tsakanin 15 da 20, an sace su ne a ranar 23 ga Nuwamba yayin da suke aikin girbi a gonakin iyayensu. Sanarwar rundunar ta ce an ceto su ne a ranar Asabar, 29 ga Nuwamba, ta hanyar wani gagarumin samame na musamman da rundunar Operation Hadin Kai ta kaddamar a kudancin Borno.

A cewar rundunar, an kwashe waɗanda aka ceto zuwa wata cibiyar tsaro ta musamman domin duba lafiyarsu, kula da su ta fuskar lafiya, kafin daga bisani a mika su ga iyalansu.

Sunayen waɗanda aka ceton sun haɗa da: Fatima Shaibu (mai shekaru 17), Fatima Umaru (mai shekaru15), Hauwa Abubakar (mai shekaru 18), Saliha Muhammed (mai shekaru 15), Sadiya Umaru (mai shekaru 17), Amira Babel (mai shekaru 15), Zara Adamu (mai shekaru 17), Nana Shaibu (mai shekaru 15), Zainab Musa (mai shekaru 18), Zainab Muhammed (mai shekaru 17), Jamila Saidu (mai shekaru 15) da Hauwa Hamidu (mai shekaru 17).

Hedikwatar Tsaro ta yaba wa dakarun ta masu jajircewa da gaggawar daukar mataki, tare da nuna godiya ga al’ummomi da masu ba da bayanan sirri da s**a taka rawar gani wajen ganin an kubutar da waɗanda aka sace.

Sojojin na ci gaba da farautar ragowar ’yan ISWAP a yankin domin hana sake kai hare-hare da kare rayukan fararen hula. Rundunar ta kuma ƙara kira ga jama’a da su ci gaba da ba da sahihan bayanai da wuri domin taimakawa yaki da ta’addanci a yankin.

Ayyukan  Biliyoyin Kuɗi Na Gwamna Dauda Lawal a Karamar Hukumar Anka: Rahoto na MusammanShugaban Karamar Hukumar Anka, H...
29/11/2025

Ayyukan Biliyoyin Kuɗi Na Gwamna Dauda Lawal a Karamar Hukumar Anka: Rahoto na Musamman

Shugaban Karamar Hukumar Anka, Hon. Bashir Musa Anka, ya bayyana manyan ayyukan raya kasa da gwamnatin Gwamna Dauda Lawal ta aiwatar a karamar hukumar, yana mai cewa “Anka na cikin jerin yankuna da ke samun gagarumar kulawa daga gwamnatin jihar tun bayan hawansa karagar mulki.”

A wata tattaunawa da ya yi da manema labarai a garin Anka, shugaban ya yi karin haske kan yadda wadannan ayyuka s**a sauya rayuwar al’umma, s**a kuma farfaɗo da sassan da ke da matuƙar muhimmanci ga ci gaban yankin.

1. Tsaro: Dorewar Zaman Lafiya da Kafuwar CPG

Hon. Bashir ya bayyana tsaro a matsayin fannin da gwamnatin Dauda Lawal ta fi mayar da hankali a kai saboda abubuwan da yankin ya taba fuskanta. Ya ce tun bayan hawansa mulki, gwamnan ya shigo da tsare-tsaren da s**a hada da:

• Karin jami’an tsaro daga hukumomi daban-daban

An karfafa hedikwatar tsaro a Anka, an inganta hanyar isar da bayanai, tare da sabunta kayan aiki domin samun ingantaccen aiki tsakanin rundunonin soji, ‘yan sanda da NSCDC.

• Daukar jami’an tsaron al’umma CPG (Community Protection Guards)

Hon. Bashir ya ce gwamnatin jihar ta dauki matasa daga cikin al’umma domin su zama Community Protection Guards (CPG) tsaro na kusa da jama’a, wanda ke aiki kai tsaye da hukumomin tsaro.
CPG na taka muhimmiyar rawa wajen:

Kula da tsaron kauyuka da yankunan da ke nesa da gari,

Taimakawa wajen gano barazanar tsaro da wuri,

Hada bayanai da hukumomin tsaro cikin gaggawa,

Tabbatar da tsaro ga manoma, 'Yan kasuwa, da makiyaya.

Shugaban ya ce wannan tsarin ya taimaka wajen rage harin 'yan bindiga, ya kuma dawo da manoma ga gonakinsu bayan dogon lokaci suna gudun hijira.

A cewarsa, ingancin wadannan matakai ya sa mutane s**a fara komawa gidajensu, kasuwanci ya fara murmurewa, sannan al’umma sun dawo harkokin yau da kullum.
Ya ce: “Idan tsaro ya daidaita, komai na daidaituwa.”

2. Gyaran Masarautar Anka: Ƙarfafa Tarihi da Al’ada

A fannin al’adu, gwamnatin Dauda Lawal ta gyara Masarautar Mai Martaba Sarkin Zamfara Anka wacce ke da dogon tarihi.

Hon. Bashir ya bayyana cewa aikin ya haɗa da:

Sabunta ginin fada,

Gyaran majalisar masarauta,

Inganta wuraren taro,

Shigar da fitilu masu aiki da hasken rana a gine-gine,

Tsabtace muhimman wuraren masarauta da ke karbar baƙi daga sassa daban-daban.

Ya ce gyaran masarautar ya kara mata martaba, ya kuma baiwa sarauta da mutanen Anka kwarin gwiwa, kasancewar masarautu su ne ginshikan zaman lafiya da zumunci a jihar Zamfara.

3. Lafiya: Kula da Marasa Lafiya

A bangaren lafiya kuwa, Gwamna Dauda Lawal ya saka gagarumar kulawa, musamman ganin cewa tsarin kiwon lafiya ya yi rauni tsawon shekaru.
Shugaban karamar hukumar ya bayyana cewa:

• Babbar Asibitin Anka ta samu sabbin kayan aiki

An inganta dakunan kwana, an sabunta dakin haihuwa, dakunan gwaje-gwaje, da dakin ɗawainiyar yara, haɗi da gidan ma'aikata.

• Gyaran wuraren shan magani a mazabu

Wuraren sun hada da Wuya Yarsabaya, Barayar Zaki, da sauran kauyuka.

Hon. Bashir ya ce marasa galihu na samun magunguna kyauta don kula da su, musamman:

Mata masu juna biyu

Yara ‘yan shekara kasa da biyar

Tsofaffi

Mutanen da ke fama da cututtukan da ke bukatar kulawa kai tsaye, k**ar irin kwalara amai da gudawa.

Ya ce hakan ya yi amfani sosai wajen rage mace-macen da ke faruwa saboda rashin kula da rashin iya biyan kudin magani.

4. Tituna da Gine-gine: Samar da Hanyoyin Ci Gaba

Tsarin gine-ginen hanya ya zama wani muhimmin bangare na farfaɗo da tattalin arzikin Anka.
Gwamnatin Dauda Lawal ta aiwatar da:

• Titin kauyen Abare, zai sauƙaƙa zirga-zirga tsakanin kauyen da cikin garin Anka

• Gadar Gangar Ruwa – gata da ta magance matsalar ratsa ruwa a lokutan damina

• Gadar Gulbi – ta bude hanyar safarar kayan amfanin gona

• Titin Anka–Mayanchi – babbar hanya da ke sauƙaƙa hulɗar kasuwanci

Hon. Bashir ya ce hanyoyin da aka gyara sun rage kudin sufuri, sun inganta kasuwanci, suna kuma kare rayuka musamman a lokacin damina.

5. Ilimi: Inganta Yanayin Makarantu

A fannin ilimi, gwamnatin jihar ta aiwatar da muhimman matakai don kara inganta rayuwar ɗalibai.

• Tsarkake ruwa da samar da rijiyoyi a makarantun Anka

Dalibai ba sa wahalar samun ruwan sha yayin karatu.

• Raba kayayyakin rubutu da littattafai kyauta

Wannan ya rage yawan yara masu barin makaranta saboda rashin kayan aiki.

• Raba uniform ga ɗalibai

Hakan ya saukaka nauyin da iyaye ke fama da shi.

Shugaban karamar hukumar ya ce waɗannan matakai sun inganta sha’awar karatu, sun kuma dawo da mutuncin tsarin makarantun firamare da sakandare.

6. Noma: Tallafin Da Ya Dawo da Murmushi

Manoma sun samu wani sabon salo na tallafi a Anka.

• Rarraba takin zamani kyauta

Wannan ya karawa gonaki inganci, ya kuma inganta yawan amfanin gona.

• Magungunan feshi kyauta

Manoma sun samu kariya ga shuka daga kwari da cututtuka masu kawo cikas ga amfanin gona.

• Samar da injinan noma kyauta

Domin rage wahala da kara inganci, musamman a fanin:

Noman shinkafa

Noman gero

Noman wake da masara

Hon. Bashir ya ce: “Manoma sun koma filayensu cikin kwanciyar hankali, kuma amfanin gona na karuwa.”

7. Walwala da Jin Dadin Al’umma

A bangaren jin dadin al’umma, gwamnatin Dauda Lawal ta aiwatar da:

• Raba tallafin shirin NG-CARES

Daruruwan iyalai, ‘yan kasuwa da matasa masu ƙaramin karfi sun amfana.

• Daukar sababbin ma’aikata

A sassa daban-daban, domin farfaɗo da ayyukan gwamnati da rage zaman kashe wando.

Shugaban ya ce wannan ya kara habaka tattalin arziki da samun kwarin gwiwa a tsakanin al’umma.

---
Kammalawa

Bisa bayanan da Hon. Bashir Musa Anka ya gabatar, ayyukan Gwamna Dauda Lawal a Karamar Hukumar Anka sun shafi tsaro, lafiya, ilimi, noma, gine-gine da walwalar al’umma, fannonin da ke da tasiri kai tsaye ga ci gaban jama’a.

Ya ce al’ummar Anka na jin tasirin wannan sauyi a zahiri, kuma suna ganin yadda gwamnati ke mayar da hankali kan farfaɗo da jihar Zamfara daga tushe.

Address

Government House Gusau
Gusau
3337

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Fara'a tv posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Fara'a tv:

Share

Category