Zamfara Online News

Zamfara Online News Sahihan Labarai

SUCCESSFUL FAZAMSS 2025 NATIONAL CONVENTION & ELECTION.The Federated Association of Zamfara State Students (FAZAMSS), In...
27/12/2025

SUCCESSFUL FAZAMSS 2025 NATIONAL CONVENTION & ELECTION.

The Federated Association of Zamfara State Students (FAZAMSS), Incorporated as NUZAMSS, successfully conducted its 2025 National Convention, culminating in the peaceful and transparent election of National Executives and Members of Parliament.
The convention activities, held at the Twin Theatre Hall, ZACAS, Gusau, featured delegates screening, sales and screening of nomination forms, manifestation, and the final election exercise. All processes were carried out in strict compliance with the FAZAMSS Constitution and guided by the principles of fairness, transparency, and inclusiveness.

The election of the National Executives and Parliament was conducted under a serene and orderly atmosphere, with the presence and observation of relevant stakeholders, security agencies, former student leaders, youth groups, and independent observers. The process was professionally supervised by the duly constituted Independent Electoral Committee (IELCOM).

We commend the maturity, discipline, and unity displayed by all aspirants, delegates, and Zamfara State students throughout the convention. The successful conclusion of the election marks a new chapter of responsible leadership, accountability, and collective progress for FAZAMSS.
The newly elected leadership is hereby charged with the responsibility of upholding the values of FAZAMSS, serving the interest of Zamfara State students, and strengthening unity across all institutions.
We sincerely appreciate the support and cooperation of all stakeholders and authorities that contributed to the success of the convention.

Congratulations to the newly elected National Executives and Members of Parliament.
Long live FAZAMSS!
Long live Zamfara State students!
Long live the Federal Republic of Nigeria!

E-sign.
Comrade Ibrahim Tukur Anka.
2025 Public Relation Officer,
FAZAMSS Convention Planning Committee.

15/11/2025

●–Minene FAZAMSS WEEK?

●–Ya FAZAMSS WEEK 2025 sai kasance?

●–Wane Abubuwa ne FAZAMSS WEEK ya ƙunsa?

●–Yaushe za,a gabatar da FAZAMSS WEEK

Ga amsar wadannan tambayoyin👇

FAZAMSS WEEK 2025...Kada ku bari a baku labari🙅‍♂️

Da dumi-dumi.Majalisar Dokokin Zamfara Ta Kori Kwamandan ZAROTA, Muhammad Bello Musa, Bisa Samunsa da Laifi.Majalisar Do...
16/10/2025

Da dumi-dumi.

Majalisar Dokokin Zamfara Ta Kori Kwamandan ZAROTA, Muhammad Bello Musa, Bisa Samunsa da Laifi.

Majalisar Dokokin Jihar Zamfara, ƙarƙashin jagorancin Rt. Hon. Bilyaminu Ismail Moriki, ta yi amfani da ikon da doka ta ba ta, inda ta kori Babban Kwamandan Hukumar ZAROTA, Muhammad Bello Musa, gaba ɗaya daga mukaminsa, bayan samun sa da laifi kai tsaye daga kwamitin bincike da majalisar ta kafa.

A cewar sanarwar da Bello Madaro Kurya, jami’in hulda da ‘yan jaridu na majalisar ya fitar tace, a zaman majalisar na yau, Alhamis, ’yan majalisar sun umurci shugaban hukumar ZAROTA da ya mika ragamar shugabanci ga wani Senior Officer na hukumar, kafin Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya amince da nadin sabon shugaban.

Shugaban Majalisar, Rt. Hon. Bilyaminu Ismail Moriki, ya bayyana hakan bayan kammala doguwar muhawara da kuma amincewar baki ɗayan ’yan majalisar dokoki.

Kana neman wajen shaƙatawa taho Gusau Jihar Zamfara.
29/09/2025

Kana neman wajen shaƙatawa taho Gusau Jihar Zamfara.

An bada umurnin k**a yan majalisun jihar Zamfara su 9  da s**a roshe tsohuwar majalisar.Jam’iyyar APC ta jihar Zamfara t...
04/05/2025

An bada umurnin k**a yan majalisun jihar Zamfara su 9 da s**a roshe tsohuwar majalisar.

Jam’iyyar APC ta jihar Zamfara ta zargi gwamnatin jihar da amfani da kotu wajen danniya da cafke wasu ‘yan majalisar dokoki tara ba tare da bin doka ba.

Jam’iyyar ta bukaci gwamnati ta daina muzgunawa ta kuma nemi mafita cikin lumana, tana kira da a kai kara gaban hukumar shari’a kan alkaliyar da ta bayar da wannan umarni.

Majalisar Dokokin jihar Zamfara ta rusa kwamitoci, data zarga da almundahana.A yau ne ɓangaren Majalisar Dokoki na Jihar...
30/04/2025

Majalisar Dokokin jihar Zamfara ta rusa kwamitoci, data zarga da almundahana.

A yau ne ɓangaren Majalisar Dokoki na Jihar Zamfara ya sanar da rushe dukkan shugabannin majalisar da kwamitocin, tare da kafa kwamitoci biyu masu muhimmanci domin sake tsara aikin majalisar bisa gaskiya da tsari.

Wannan sanarwa ta fito ne daga Shugaban Majalisar na ɓangaren, Hon. Bashar Aliyu Gummi, bayan zaman majalisa da aka gudanar a Gusau, babban birnin jihar.

Ya bayyana cewa an sake kafa kwamitoci guda biyu masu muhimmanci – wato Kwamiti na Ladubba da ’Yanci da kuma Kwamiti na Ayyuka da Ababen More Rayuwa – wadanda za su kasance ƙarƙashin jagorancin Hon. Masama da Hon. Bashir Sarkin Zango daga yau.

Majalisar ta bayyana aniyar ta ta kai rahoton duk wata almundahana da tsofaffin shugabannin majalisar s**a aikata zuwa hukumar EFCC da ICPC domin dawo da duk kudaden jama’a da aka karkatar.

A yayin zaman, ƙarƙashin batutuwa na gaggawa da s**a shafi bukatun jama’a, ‘yan majalisar sun yi tir da yadda gwamnatin Dauda Lawal ke bai wa wasu ƙananan hukumomi fifiko wajen naɗa sakatarorin dindindin, inda wasu yankuna ba su samu ko guda ba.

A cikin kudurin da Hon. Ibrahim Tudu Tukur, dan majalisa mai wakiltar gundumar Bakura ya gabatar, ya jaddada yadda wasu ƙananan hukumomi irin su Tsafe, Maradun da Birnin Magaji ba su samu naɗin sakatare dindindin ko guda ba, yayin da wasu yankuna s**a samu fiye da tara.

Ya bayyana cewa hakan ya saba wa kundin tsarin mulkin Najeriya na 1999 da aka yi wa kwaskwarima, kuma dole ne a gyara wannan al’amari domin tabbatar da adalci da daidaito ga kowa a jihar.

Majalisar ta umurci Gwamna Dauda Lawal da ya soke nadin kuma ya sake duba batun cikin adalci domin a bai wa dukkan ƙananan hukumomi wakilci.

Haka kuma, majalisar ta nuna damuwa kan jinkirin da ke cikin aikin hanya mai tsada ta Gusau-Dansadau da aka riga aka biya kwangila tun bara, amma ba a gama ko kilomita biyar ba.

Saboda haka, majalisar ta gayyaci kwamishinan ayyuka da ababen more rayuwa na jihar da ya bayyana a gaban ta don ya bayyana dalilin tsaikon aikin, inda s**a jaddada cewa “duk kuɗin jama’a da na haraji dole ne a yi amfani da su cikin gaskiya kan abin da aka tsara.”

Majalisar ta kuma bukaci Gwamna Dauda Lawal da ya buɗe aƙalla makarantun kwana biyu daga kowanne yankin Sanata guda uku na jihar, wadanda aka rufe saboda rashin tsaro, k**ar yadda iyaye s**a bukata. Majalisar ta zargi gwamnati da kin buɗe makarantu ne domin guje wa aiwatar da shirin ciyar da ɗalibai wanda ke taimaka wa yara ‘yan ƙasa marasa ƙarfi da kuma rage barin zuwa makaranta ga yara.

A wani ɓangaren majalisar dokoki ta jihar ya fito makon da ya gabata ƙarƙashin jagorancin Hon. Gummi, inda s**a fara magana kan muhimman batutuwa da s**a shafi jama’a da s**a hada da s**a ga gwamnatin jihar da kuma majalisar ɓangaren Hon. Moriki, wadda ita da gwamnatin ba su bayyana matsayinsu ba a fili.

NiQaf Yazama Silar Mutuwar Aure na Sati Daya Da Daura mana Auren nida mijina -Surayya Aminu Dan maliki.Wanda Aka daura m...
29/04/2025

NiQaf Yazama Silar Mutuwar Aure na Sati Daya Da Daura mana Auren nida mijina -Surayya Aminu Dan maliki.

Wanda Aka daura mana aure Dashi muna son junan mu, tun kafin bikin mu yake cewa Shi bayason ina sanya NiQaf, nikuma na fada masa irin Tarbiyyar Gidan mu kenan,baban mu baya barin kowa ta fita sai da NiQaf, Bai tashi fara nuna ɓacin Ransa akan Niqaf din sosai ba sai Ranar da yace in shirya muje shopping, aiko na dakko NiQaf shi kuma yace bazan saba, ni kuma nace sai dai in fasa fitar, daga karshe yace in zaba ko Umurnin sa ko in koma gida, bance masa komai ba dai,karshe yace ya sakeni saki Daya.

Daga: Abdulmalik Ahmad

Gwamnan Zamfara ya ninka alawus din masu yi wa kasa hidima da kaso 100Gwamna Dauda Lawal na Jihar Zamfara ya umarci a ƙa...
28/04/2025

Gwamnan Zamfara ya ninka alawus din masu yi wa kasa hidima da kaso 100

Gwamna Dauda Lawal na Jihar Zamfara ya umarci a ƙara kuɗaɗen alawus na masu yiwa kasa hidima (NYSC) da aka tura jihar da kashi 100.

Lawal ya bayyana haka a ranar Juma'a a Gusau, yayin da yake ƙaddamar da buɗaɗɗen atisayen shirin horaswa na 2025 rukunin ‘A’, Stream I na masu yiwa kasa hidima da aka tura jihar.

Gwamnan ya samu wakilcin Sakataren Gwamnatin Jihar, Abubakar Nakwada, a wajen taron.

Ya sake jaddada cewa gwamnatin sa ta himmatu wajen tabbatar da tsaro da walwalar dukkan matasan na NYSC 550 da aka tura jihar.

"Ina farin cikin sanar da ku cewa na bayar da umarnin dawo da biyan alawus na jiha ga dukkan masu NYSC da ke cikin jihar.

"Haka kuma na bayar da umarnin ƙara yawan alawus ɗin da ake biya da kashi 100 cikin ɗari"

Dan Majalisar Wakilan Najeriya Mai Wakiltar Gusau da Tsafe Yabada Kyautar GIDA da MOTA  zuwa ga yaran sa:-Abdoul Amag 🏠 ...
27/04/2025

Dan Majalisar Wakilan Najeriya Mai Wakiltar Gusau da Tsafe Yabada Kyautar GIDA da MOTA zuwa ga yaran sa:-

Abdoul Amag 🏠 🚗
Nasir M Imam 🏠 🚗
Yusuf S Halilu 🏠
Mansu Amadu 🏠
Zainab Maharazu 🏠
M Badaruddeen Bature 🏠 🚗
Zayyanu Abubakar Galadima 🏠 🚗
Gizo Mai Palaca Muhammad 🏠

Daga: Nura Nayababa

CIBIYAR YAƘI DA TA’ADDANCI TA ZIYARCI ZAMFARA, TA JINJINAWA GWAMNA DAUDA LAWAL BISA ƘOƘARIN SA GA SHA’ANIN TSAROCibiyar ...
24/04/2025

CIBIYAR YAƘI DA TA’ADDANCI TA ZIYARCI ZAMFARA, TA JINJINAWA GWAMNA DAUDA LAWAL BISA ƘOƘARIN SA GA SHA’ANIN TSARO

Cibiyar yaƙi da ta’addanci ta ƙasa ta yabawa Gwamna Dauda Lawal bisa jajircewar sa na tabbatar da tsaron al’ummar jihar Zamfara.

Wata babbar tawaga daga cibiyar yaƙi da ta’adanci ta ziyarci Gwamnan ranar Laraba a ɗakin taro na gidan gwamnati dake Gusau.

Wata sanarwa daga mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ta bayyana cewa, Cibiyar tana samar da shugabanci da dubarun aiki ga Sojoji, da sauran jami’an tsaro ƙarƙashin kulawar mai ba shugaban ƙasa shawara kan harkokin tsaro.

Gwamna Dauda Lawal yayi farin cikin ziyarar cibiyar Zamfara don ƙaƙarin gwamnati akan sha’anin tsaron jihar.

“A ko yaushe ina cewa idan zakuyi ƙoƙarin kai ƙarshen matsalar rashin tsaro a Zamfara, babu shakka zaku magance aƙalla kaso 80 na matsalar tsaron Arewa.

Daga ƙoƙarin da akayi kawo yanzu, mun tanadi abunda zai magance wannan matsala ta hanyar tuntuɓa da haɗin guiwa tsakanin jiha da Ofishin mai ba shugaban ƙasa shawara kan harkokin tsaro. Wannan abun ayaba ne.

“Nayi farin ciki da naji cewa EU ta ware wasu kuɗaɗe, duk da zamu samar da namu kason kuɗin. A Zamfara shirye muke tsaf na saka kason kuɗin mu. Idan kun shirya ko gobe ne, mu shirye muke.

“Shirye muke, kuma ƙofar mu a buɗe take. Muna maraba da duk wani abu da zai kawo chanji mai ma’ana a Zamfara. Zan bada mutanen mu da zasuyi aiki daku.

Tunda farko, Shugabar PCVE, Amb. Mairo Musa Abbas tace sun kawo ziyara a Zamfara ne a madadin mai baiwa shugaban ƙasa shawara kan harkokin tsaro, Mallam Nuhu Ribaɗu, da kuma shugaban cibiyar yaƙi da taadanci, Maj. Gen. Adamu Garba Laka.

“Muna gode maka akan tarbon da muka samu da kuma shugabancin da ka samar ga al’ummar jihar Zamfara. Zamu inganta haɗin guiwa tsakanin mu don tabbatar da cewa Zamfara ta samu zama lafiya.

Daga: Sulaiman Bala Idris
Kakakin Gwamnan Zamfara

Sabon Labari!!!Sabon Kakakin majalisar Dokokin jihar Zamfara Rt. Hon Bashir Aliyu Gummi, Ya sanarda roshe kasafin kudin ...
24/04/2025

Sabon Labari!!!

Sabon Kakakin majalisar Dokokin jihar Zamfara Rt. Hon Bashir Aliyu Gummi, Ya sanarda roshe kasafin kudin 2025 da Gwamnan jihar Zamfara Dauda Lawal yayi, Aikin farko da majalisar ta fara kenan.

Daga: Ambassador Bashir Isah Gusau

Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Zamfara, Rt. Hon. Bilyaminu Isma’il Moriki, ya yi wa manema labarai jawabi a Gusau danga...
24/04/2025

Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Zamfara, Rt. Hon. Bilyaminu Isma’il Moriki, ya yi wa manema labarai jawabi a Gusau dangane da zama da wasu ‘yan majalisar da aka dakatar s**a gudanar, ciki har da wanda aka bayyana kujerarsa a matsayin wacce ta zama fanko.

Kakakin Majalisar ya jaddada cewa, majalisa guda daya ce tilo take da inganci a dokance a jihar, wadda kuma ke zamanta a Gusau, babban birnin jiha.

Ya bayyana zaman da ‘yan majalisar da aka dakatar s**a yi a matsayin saba wa doka, inda ya nuna cewa lamarin nasu yana gaban kotu, kuma kotu ta umurci bangarorin biyu da su ci gaba da kasancewa a halin da suke ciki (status quo). Amma duk da haka, ‘yan majalisar da aka dakatar sunyi gaban kansu, sun yi zama ba tare da la’akari da wannan umarni na kotu ba.

Kakakin majalisar ya nuna damuwa matuka kan halartar zaman da wani tsohon dan majalisar ya yi, wanda kujerarsa ta riga ta zama fanko, yana mai jaddada cewa mutumin ba shi da wani hurumin doka na ci gaba da kiran kansa dan majalisa saboda ya saba doka kuma doka ta koreshi daga kujerarsa.

Daga: Abdul Balarabe

Address

Gusau

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Zamfara Online News posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Zamfara Online News:

Share