Zamfara Online News

Zamfara Online News Sahihan Labarai

An bada umurnin k**a yan majalisun jihar Zamfara su 9  da s**a roshe tsohuwar majalisar.Jam’iyyar APC ta jihar Zamfara t...
04/05/2025

An bada umurnin k**a yan majalisun jihar Zamfara su 9 da s**a roshe tsohuwar majalisar.

Jam’iyyar APC ta jihar Zamfara ta zargi gwamnatin jihar da amfani da kotu wajen danniya da cafke wasu ‘yan majalisar dokoki tara ba tare da bin doka ba.

Jam’iyyar ta bukaci gwamnati ta daina muzgunawa ta kuma nemi mafita cikin lumana, tana kira da a kai kara gaban hukumar shari’a kan alkaliyar da ta bayar da wannan umarni.

Majalisar Dokokin jihar Zamfara ta rusa kwamitoci, data zarga da almundahana.A yau ne ɓangaren Majalisar Dokoki na Jihar...
30/04/2025

Majalisar Dokokin jihar Zamfara ta rusa kwamitoci, data zarga da almundahana.

A yau ne ɓangaren Majalisar Dokoki na Jihar Zamfara ya sanar da rushe dukkan shugabannin majalisar da kwamitocin, tare da kafa kwamitoci biyu masu muhimmanci domin sake tsara aikin majalisar bisa gaskiya da tsari.

Wannan sanarwa ta fito ne daga Shugaban Majalisar na ɓangaren, Hon. Bashar Aliyu Gummi, bayan zaman majalisa da aka gudanar a Gusau, babban birnin jihar.

Ya bayyana cewa an sake kafa kwamitoci guda biyu masu muhimmanci – wato Kwamiti na Ladubba da ’Yanci da kuma Kwamiti na Ayyuka da Ababen More Rayuwa – wadanda za su kasance ƙarƙashin jagorancin Hon. Masama da Hon. Bashir Sarkin Zango daga yau.

Majalisar ta bayyana aniyar ta ta kai rahoton duk wata almundahana da tsofaffin shugabannin majalisar s**a aikata zuwa hukumar EFCC da ICPC domin dawo da duk kudaden jama’a da aka karkatar.

A yayin zaman, ƙarƙashin batutuwa na gaggawa da s**a shafi bukatun jama’a, ‘yan majalisar sun yi tir da yadda gwamnatin Dauda Lawal ke bai wa wasu ƙananan hukumomi fifiko wajen naɗa sakatarorin dindindin, inda wasu yankuna ba su samu ko guda ba.

A cikin kudurin da Hon. Ibrahim Tudu Tukur, dan majalisa mai wakiltar gundumar Bakura ya gabatar, ya jaddada yadda wasu ƙananan hukumomi irin su Tsafe, Maradun da Birnin Magaji ba su samu naɗin sakatare dindindin ko guda ba, yayin da wasu yankuna s**a samu fiye da tara.

Ya bayyana cewa hakan ya saba wa kundin tsarin mulkin Najeriya na 1999 da aka yi wa kwaskwarima, kuma dole ne a gyara wannan al’amari domin tabbatar da adalci da daidaito ga kowa a jihar.

Majalisar ta umurci Gwamna Dauda Lawal da ya soke nadin kuma ya sake duba batun cikin adalci domin a bai wa dukkan ƙananan hukumomi wakilci.

Haka kuma, majalisar ta nuna damuwa kan jinkirin da ke cikin aikin hanya mai tsada ta Gusau-Dansadau da aka riga aka biya kwangila tun bara, amma ba a gama ko kilomita biyar ba.

Saboda haka, majalisar ta gayyaci kwamishinan ayyuka da ababen more rayuwa na jihar da ya bayyana a gaban ta don ya bayyana dalilin tsaikon aikin, inda s**a jaddada cewa “duk kuɗin jama’a da na haraji dole ne a yi amfani da su cikin gaskiya kan abin da aka tsara.”

Majalisar ta kuma bukaci Gwamna Dauda Lawal da ya buɗe aƙalla makarantun kwana biyu daga kowanne yankin Sanata guda uku na jihar, wadanda aka rufe saboda rashin tsaro, k**ar yadda iyaye s**a bukata. Majalisar ta zargi gwamnati da kin buɗe makarantu ne domin guje wa aiwatar da shirin ciyar da ɗalibai wanda ke taimaka wa yara ‘yan ƙasa marasa ƙarfi da kuma rage barin zuwa makaranta ga yara.

A wani ɓangaren majalisar dokoki ta jihar ya fito makon da ya gabata ƙarƙashin jagorancin Hon. Gummi, inda s**a fara magana kan muhimman batutuwa da s**a shafi jama’a da s**a hada da s**a ga gwamnatin jihar da kuma majalisar ɓangaren Hon. Moriki, wadda ita da gwamnatin ba su bayyana matsayinsu ba a fili.

NiQaf Yazama Silar Mutuwar Aure na Sati Daya Da Daura mana Auren nida mijina -Surayya Aminu Dan maliki.Wanda Aka daura m...
29/04/2025

NiQaf Yazama Silar Mutuwar Aure na Sati Daya Da Daura mana Auren nida mijina -Surayya Aminu Dan maliki.

Wanda Aka daura mana aure Dashi muna son junan mu, tun kafin bikin mu yake cewa Shi bayason ina sanya NiQaf, nikuma na fada masa irin Tarbiyyar Gidan mu kenan,baban mu baya barin kowa ta fita sai da NiQaf, Bai tashi fara nuna ɓacin Ransa akan Niqaf din sosai ba sai Ranar da yace in shirya muje shopping, aiko na dakko NiQaf shi kuma yace bazan saba, ni kuma nace sai dai in fasa fitar, daga karshe yace in zaba ko Umurnin sa ko in koma gida, bance masa komai ba dai,karshe yace ya sakeni saki Daya.

Daga: Abdulmalik Ahmad

Gwamnan Zamfara ya ninka alawus din masu yi wa kasa hidima da kaso 100Gwamna Dauda Lawal na Jihar Zamfara ya umarci a ƙa...
28/04/2025

Gwamnan Zamfara ya ninka alawus din masu yi wa kasa hidima da kaso 100

Gwamna Dauda Lawal na Jihar Zamfara ya umarci a ƙara kuɗaɗen alawus na masu yiwa kasa hidima (NYSC) da aka tura jihar da kashi 100.

Lawal ya bayyana haka a ranar Juma'a a Gusau, yayin da yake ƙaddamar da buɗaɗɗen atisayen shirin horaswa na 2025 rukunin ‘A’, Stream I na masu yiwa kasa hidima da aka tura jihar.

Gwamnan ya samu wakilcin Sakataren Gwamnatin Jihar, Abubakar Nakwada, a wajen taron.

Ya sake jaddada cewa gwamnatin sa ta himmatu wajen tabbatar da tsaro da walwalar dukkan matasan na NYSC 550 da aka tura jihar.

"Ina farin cikin sanar da ku cewa na bayar da umarnin dawo da biyan alawus na jiha ga dukkan masu NYSC da ke cikin jihar.

"Haka kuma na bayar da umarnin ƙara yawan alawus ɗin da ake biya da kashi 100 cikin ɗari"

Dan Majalisar Wakilan Najeriya Mai Wakiltar Gusau da Tsafe Yabada Kyautar GIDA da MOTA  zuwa ga yaran sa:-Abdoul Amag 🏠 ...
27/04/2025

Dan Majalisar Wakilan Najeriya Mai Wakiltar Gusau da Tsafe Yabada Kyautar GIDA da MOTA zuwa ga yaran sa:-

Abdoul Amag 🏠 🚗
Nasir M Imam 🏠 🚗
Yusuf S Halilu 🏠
Mansu Amadu 🏠
Zainab Maharazu 🏠
M Badaruddeen Bature 🏠 🚗
Zayyanu Abubakar Galadima 🏠 🚗
Gizo Mai Palaca Muhammad 🏠

Daga: Nura Nayababa

CIBIYAR YAƘI DA TA’ADDANCI TA ZIYARCI ZAMFARA, TA JINJINAWA GWAMNA DAUDA LAWAL BISA ƘOƘARIN SA GA SHA’ANIN TSAROCibiyar ...
24/04/2025

CIBIYAR YAƘI DA TA’ADDANCI TA ZIYARCI ZAMFARA, TA JINJINAWA GWAMNA DAUDA LAWAL BISA ƘOƘARIN SA GA SHA’ANIN TSARO

Cibiyar yaƙi da ta’addanci ta ƙasa ta yabawa Gwamna Dauda Lawal bisa jajircewar sa na tabbatar da tsaron al’ummar jihar Zamfara.

Wata babbar tawaga daga cibiyar yaƙi da ta’adanci ta ziyarci Gwamnan ranar Laraba a ɗakin taro na gidan gwamnati dake Gusau.

Wata sanarwa daga mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ta bayyana cewa, Cibiyar tana samar da shugabanci da dubarun aiki ga Sojoji, da sauran jami’an tsaro ƙarƙashin kulawar mai ba shugaban ƙasa shawara kan harkokin tsaro.

Gwamna Dauda Lawal yayi farin cikin ziyarar cibiyar Zamfara don ƙaƙarin gwamnati akan sha’anin tsaron jihar.

“A ko yaushe ina cewa idan zakuyi ƙoƙarin kai ƙarshen matsalar rashin tsaro a Zamfara, babu shakka zaku magance aƙalla kaso 80 na matsalar tsaron Arewa.

Daga ƙoƙarin da akayi kawo yanzu, mun tanadi abunda zai magance wannan matsala ta hanyar tuntuɓa da haɗin guiwa tsakanin jiha da Ofishin mai ba shugaban ƙasa shawara kan harkokin tsaro. Wannan abun ayaba ne.

“Nayi farin ciki da naji cewa EU ta ware wasu kuɗaɗe, duk da zamu samar da namu kason kuɗin. A Zamfara shirye muke tsaf na saka kason kuɗin mu. Idan kun shirya ko gobe ne, mu shirye muke.

“Shirye muke, kuma ƙofar mu a buɗe take. Muna maraba da duk wani abu da zai kawo chanji mai ma’ana a Zamfara. Zan bada mutanen mu da zasuyi aiki daku.

Tunda farko, Shugabar PCVE, Amb. Mairo Musa Abbas tace sun kawo ziyara a Zamfara ne a madadin mai baiwa shugaban ƙasa shawara kan harkokin tsaro, Mallam Nuhu Ribaɗu, da kuma shugaban cibiyar yaƙi da taadanci, Maj. Gen. Adamu Garba Laka.

“Muna gode maka akan tarbon da muka samu da kuma shugabancin da ka samar ga al’ummar jihar Zamfara. Zamu inganta haɗin guiwa tsakanin mu don tabbatar da cewa Zamfara ta samu zama lafiya.

Daga: Sulaiman Bala Idris
Kakakin Gwamnan Zamfara

Sabon Labari!!!Sabon Kakakin majalisar Dokokin jihar Zamfara Rt. Hon Bashir Aliyu Gummi, Ya sanarda roshe kasafin kudin ...
24/04/2025

Sabon Labari!!!

Sabon Kakakin majalisar Dokokin jihar Zamfara Rt. Hon Bashir Aliyu Gummi, Ya sanarda roshe kasafin kudin 2025 da Gwamnan jihar Zamfara Dauda Lawal yayi, Aikin farko da majalisar ta fara kenan.

Daga: Ambassador Bashir Isah Gusau

Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Zamfara, Rt. Hon. Bilyaminu Isma’il Moriki, ya yi wa manema labarai jawabi a Gusau danga...
24/04/2025

Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Zamfara, Rt. Hon. Bilyaminu Isma’il Moriki, ya yi wa manema labarai jawabi a Gusau dangane da zama da wasu ‘yan majalisar da aka dakatar s**a gudanar, ciki har da wanda aka bayyana kujerarsa a matsayin wacce ta zama fanko.

Kakakin Majalisar ya jaddada cewa, majalisa guda daya ce tilo take da inganci a dokance a jihar, wadda kuma ke zamanta a Gusau, babban birnin jiha.

Ya bayyana zaman da ‘yan majalisar da aka dakatar s**a yi a matsayin saba wa doka, inda ya nuna cewa lamarin nasu yana gaban kotu, kuma kotu ta umurci bangarorin biyu da su ci gaba da kasancewa a halin da suke ciki (status quo). Amma duk da haka, ‘yan majalisar da aka dakatar sunyi gaban kansu, sun yi zama ba tare da la’akari da wannan umarni na kotu ba.

Kakakin majalisar ya nuna damuwa matuka kan halartar zaman da wani tsohon dan majalisar ya yi, wanda kujerarsa ta riga ta zama fanko, yana mai jaddada cewa mutumin ba shi da wani hurumin doka na ci gaba da kiran kansa dan majalisa saboda ya saba doka kuma doka ta koreshi daga kujerarsa.

Daga: Abdul Balarabe

Hukumar ZITDA Zata Ceto Matasan Jihar Zamfara Hukumar Zamfara Information Technology Development Agency - ZITDA sun wall...
24/04/2025

Hukumar ZITDA Zata Ceto Matasan Jihar Zamfara

Hukumar Zamfara Information Technology Development Agency - ZITDA sun wallafa ashafin su na facebook cewa sun shirya tsaf, domin samar da ayukkan yi, Musamman ga matasa masu shaidar kammala karatun Gaba da sakandare.

24/04/2025

Matsalar Tsaron Bukkuyum

Shugaban Karamar Hukumar Mulkin Bukkuyum Hon. Umar Faru Matawallen Nasarawar Burkullu, Ya Magantu Tareda Mika Sako Cikin Fushi Ga Shugabannin Jihar Zamfara Inda Ya Jaddada Cewa Rayuwarsa Da Kujerarsa Ashire Yake Da Yarasa Su A Kan Ganin Karamar Hukumar Mulkin Bukkuyum Tasamu Zaman Lafiya,

Shugaban Yakuma Jaddada Cewa Dolene Abari Karamar Hukumar Mulkin Bukkuyum Tazauna Lafiya, Idan Ba Haka Ba Babu Wani Mahalukin Dan Siyasa Da Ya Isa Yashigo Kamfen A Neman Goyon Bayan A zabesa, Shugaban Yace Babu Gudu Babu Ja Da Baya A Ganin Tabbatarda Samun Tsaron Karamar Hukumar Mulkin Bukkuyum

Inda Yace Yayi Duk Shige Da Ficenda Zai Yi Domin Ganin An Samu Tsaro, Amma Shuwagabannin Tsaro Sun Kasa Bashi Hadin Kai Inda Yakuma Sake Jaddada Cewa Ashire Yake Kuma Baya Jin Tsoron Kowa Indai A Kan Samun Masalahar Talakkawan Bukkuyum Ne

Yakuma ce Kwana kwanannan anturo Jami'an tsaro masu yawa domin subada kariya ashiga dajin nasarawa domin dibar ma'adanai inda yacce Wannan hujjar shi yanuna babu raayin yakar yan bindiga kuma bashine gaban shugabanni ba,

Saboda haka babu wani wanda zai shigo a Karamar Hukumar Mulkin Bukkuyum domin dibar azzikinta matukar bai shigoa aka kai karshen matsalar Tsaron Bukkuyum ba wallahi,

Daga: Iliyasu Aliyu Roba Roba

Sabon Labari!!!Yan Majalisun jiha mutun 9 da aka dakatar a Watan Feb 2024, Sun gabatar da zama yau a Gusau, Sun zabi Hon...
23/04/2025

Sabon Labari!!!

Yan Majalisun jiha mutun 9 da aka dakatar a Watan Feb 2024, Sun gabatar da zama yau a Gusau, Sun zabi Hon Bashir Aliyu Gummi a matsayin sabon Speaker na majalisar Dokoki ta jihar Zamfara.

Makarantar Primary mafi tsada a Najeriya.......Naira miliyan 42 ne kudin da kowane dalibi yake biya a kowace shekara ban...
22/04/2025

Makarantar Primary mafi tsada a Najeriya.......

Naira miliyan 42 ne kudin da kowane dalibi yake biya a kowace shekara bangaren Primary da Secondary. Kudin Admission din makarantar kuma Naira miliyan biyu.

Turawa ne s**a kaba makarantar a Ogombo Road, Ogombo, Lekki, jihar Legas.

Address

Gusau

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Zamfara Online News posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Zamfara Online News:

Share