Qafila Tv Gusau

Qafila Tv Gusau Manufar Buda wannan shafi shine yada da'awar musulunci a sauka ke ga Al'ummar Sayyiduna Rasulullahi Sallallahu Alaihi Wasallam.

QAFILATUL MAHABBA ISLAMIC FOUNDATION OF NIGERIAReshen Gusau, Jihar ZamfaraSHAH'RU RAHMA 2026Alhamdulillah! Alhamdulillah...
31/08/2026

QAFILATUL MAHABBA ISLAMIC FOUNDATION OF NIGERIA
Reshen Gusau, Jihar Zamfara

SHAH'RU RAHMA 2026

Alhamdulillah! Alhamdulillah! Alhamdulillah!

Qafilatul Mahabba Islamic Foundation of Nigeria, Reshen Gusau, Jihar Zamfara, ƙarƙashin jagorancin Jagoranmu mai albarka, Sheikh Prof. Ibrahim Maqari, Chief Imam na National Mosque Abuja.

Ta gudanar da taron raba tallafin watan Rabi'ul Auwal (Shahrur Rahmah), watan haihuwar Annabi Muhammad (SAW), cikin nasara da yardar Allah.
Wanda jagora kuma shugaba na wannan gidauniya na kasa reshen Jihar Zamfara, Sheikh Dr. Saminu Dalhat Ahmad ya jagoranta.

Wanda ya Gudana A jiya Laraba 17_Rabi'ul Awwal_1448 Dai Dai da 30/08/2026
A Makarantar Azzahra, Unguwar Yarima, Gusau, Jihar Zamfara.
Da 10:00 na safe.

A cikin wannan taro mai albarka, an gudanar da ayyukan alkhairi kamar haka:

1. Ciyar da mabukata abinci dafaffe tare da nama.
2. Raba kayan abinci ga mabukata.
3. Raba fom ɗin rajista ga waɗanda za a koyar da sana'o'i (Entrepreneurship).
4. Ɗaukar nauyin karatun 'ya'yan marayu na matakin Firamare da Sakandare.
5. Yanka shanu tare da rabon naman ga mabukata.
6. Ziyartar asibiti domin tallafa wa marasa lafiya.
7. Raba littafin Tambayoyin Addinin Musulunci – Kashi na Biyu, wanda Sheikh Ibrahim Ahmad Makari ya wallafa.
8. Raba kwafe-kwafen Alƙur'ani Mai Girma ga ɗaliban makarantu da s**a halarci taron.

Muna miƙa godiya ta musamman ga:

- Jagoranmu, Sheikh Prof. Ibrahim Ahmad Makari, bisa jagoranci nagari da ci gaba da bayar da goyon baya.
- Jagoran wannan na jihar zamfara Dr. Samin Dalhat Ahmad
- Dukkan masu bayar da tallafi da gudummawa da s**a ba da tasu gudunmawar wajen nasarar wannan aiki.
- Kwamitin gudanarwa na Reshen Gusau da dukkan masu aikin sakai.
- Babban baƙon mai jawabi, Dr. Nasir Sheikh Balarabe Gusau.
- Dukkan 'yan'uwa Musulmi da s**a halarta tare da addu'o'insu.

Muna roƙon Allah (SWT) Ya karɓi wannan aiki a matsayin Sadakatul Jariya, Ya sanya shi cikin ayyukan alheri masu ɗorewa, Ya saka wa duk wanda ya ba da gudunmawa da mafificin alheri, Ya ƙara mana haɗin kai, soyayya da zaman lafiya domin cigaban addini da al'umma.

«"Wa mā tunfiqū min shay'in fī sabīlillāhi yuwaffa ilaykum wa antum lā tuẓlamūn."»

Allah (SWT) Ya ƙara mana ikon ci gaba da gudanar da irin waɗannan ayyukan alheri. Amin.

30/08/2026

QAFILATUL MAHABBA ISLAMIC FOUNDATION OF NIGERIA GUSAU, ZAMFARA STATE CHAPTER

Alhamdulillah! Alhamdulillah! Alhamdulillah!

Qafilatul Mahabbah Islamic Foundation of Nigeria, Gusau Branch, Jihar Zamfara, karkashin jagorancin Jagoranmu mai albarka, Sheikh Prof. Ibrahim Ahmad Makari, Chief Imam na National Mosque Abuja, ta yi taron raba tallafin watan Rabi’ul Auwal - (Shahrur Rahmah) watan haihuwar Shugaba SAWW cikin nasara da yardar Allah.

Taron ya gudana kamar haka:
Wuri: Makarantar Azzahra, Unguwar Yarima, Gusau, Jihar Zamfara
Rana: Jiya Lahadi, 30/08/2025
Lokaci: 10:00am

A cikin wannan taro mai albarka, an gudanar da ayyukan alkhairi kamar haka:
1. Ciyar da abinci (dafaffe) da nama ga mabukata
2. Raba danyen abinci
3. Raba takardar cikewa (Form) ga waɗanda za'a koyawa sana'o'in (Enterpreneurship)
4. Daukar nauyin ‘ya’ya marayu na karatun Primary da Secondary
5. Yanka shanu domin rabawa mabukata
6. Ziyartar asibiti domin tallafawa majinyata
7. Raba littattafan tambayoyin Addinin Musulunci - Kashi na 2 na Sheikh Ibrahim Ahmad Maqari
8. Raba copies na Alqur'ani Mai Girma ga ɗaliban makarantu da s**a halarta.

Muna miqa godiya ta musamman ga:
¤ Jagoranmu Sheikh Prof. Ibrahim Maqari bisa jagoranci da goyon bayansa
¤ Dukkan masu bayar da tallafi da gudunmawa domin musharala acikin aiki
¤ Kwamitin gudanarwa na Gusau Branch da sauran masu aikin sa kai
¤ Babban bako mai jawabi Dr. Nasir Sheikh Balarabe Gusau
¤ ‘Yan uwa Musulmi da s**a halarta tare da addu’o’i

Muna rokon Allah SWT ya karbi wannan aiki a matsayin Sadakatul Jariya da kuma koyi da jinƙan Manzon SAWW, ya saka wa kowa da alkhairi, ya kara mana hadin kai da soyayya domin cigaban Al’umma.

Allah Ya Sakawa Dr. Saminu Dalhat Ahmad da alkhairi bisa tsayawa har sai da akayi tarin cikin Nasara.

“Wa ma tunfiquu min shai’in fii sabilillah yuwaffa ilaikum wa antum la tuzlamuun”

Allah ya kara mana ikon cigaba da gudanar da wannan aiki.

AMSOSHIN TAMBAYOYIN KU kashi Na 2Za,a Kaddamarda Wannan Littafi a Ranar Jinkai Ranar Raba Tallafi Zuwa ga Mabuqata domin...
29/08/2026

AMSOSHIN TAMBAYOYIN KU kashi Na 2

Za,a Kaddamarda Wannan Littafi a Ranar Jinkai Ranar Raba Tallafi Zuwa ga Mabuqata domin Murnar zagayowar Watan haihuwar Annabi Sallalahu Alaihi Wa Sallam

SHAHRURRAHMA
25/08/2026

SHAHRURRAHMA

08/06/2026

QAFILATUL MAHABBA GUSAU BRANCH
(ORPHAN'S DAY 2026)

Address

Gusau

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Qafila Tv Gusau posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Qafila Tv Gusau:

Shortcuts

Share