Bushira bala mada

Bushira bala mada Besensible is to become a success man

Masarautun Hausawa da Ba a Ci da Yaki ba a Lokacin Jihadin 1804Lokacin Jihadin Shehu Usman ɗan Fodio a ƙarni na 19, duk ...
23/08/2025

Masarautun Hausawa da Ba a Ci da Yaki ba a Lokacin Jihadin 1804

Lokacin Jihadin Shehu Usman ɗan Fodio a ƙarni na 19, duk da girman tasirinsa, ba dukkan masarautun Hausawa aka ci su da yaki ba. Wasu sun tsira ta hanyar hijira da sauya cibiyar mulki, wasu kuma nisan wuri, hikima, ko matsayar shugabanni sun hana jihadin ya shafe su. Wannan bayani na kawo jerin waɗannan masarautu tare da takaitaccen bayani kan yadda s**a tsira.

I. Masarautun da S**a Yi Hijira ko S**a Gusa Daula:

1. Gobir
– Bayan faduwar Alkalawa, masarautar ta koma Tsibiri da Sabon Birni, inda sarauta ta ci gaba.

2. Zamfara
– Bayan rushewar daula, Hausawan Zamfara s**a watse s**a kafa sababbin masarautu k**ar:

Anka

Mafara

Bakura

Bukkuyum

Gumi

Tsafe

Kwatarkwashi

3. Katsina
– Sarautar ta koma Maradi (a Jamhuriyar Nijar), inda ta ci gaba da wanzuwa bayan faduwar Birnin Katsina.

4. Zazzau
– Bayan shan kaye a Zariya, sarakunan Zazzau s**a kafa sabuwar cibiyar mulki a Suleja (wanda ake kira "Zazzau Suleja").

5. Hadejia
– Sarkin Hadejia ya janye ba tare da fada ba, ya miƙa mulki cikin salama ga Fulanin jihadi. Ya ɓoye kansa don kauce wa zubar da jinin talakawansa, yana mai cewa “mulkin suke so, to gashi nan.”

6. Azare
– Mai mulkin ya miƙa mulki da hikima, don kare rayukan jama’a daga bala’in yaki.

7. Kebbi
– Masarautar ta koma daga Kabi zuwa Argungu, inda s**a kafa sabuwar cibiyar mulki.

8. Daura kuma s**a kafa Zangon Daura

II. Masarautun da Jihadin Bai Shafa ba Ko S**a Tsira Saboda Nisan Wuri Ko Hikima:

1. Agadez (Nijar)
– Tsohuwar daula ce tun ƙarni na 14, haɗakar Berber da Hausawa. Ta kauce wa jihadi saboda nisan wuri da tsarin mulkinta mai zaman kansa.

2. Tessaoua (Tasawa)
– Masarauta a Nijar da ke gefen yammacin Katsina, ta tsira daga jihadi.

3. Damagaram
– Masarautar Larabawa da Hausawa da aka kafa a ƙarni na 17. Da fari suna ƙarƙashin umarnin Borno, amma daga bisani s**a ɓalle a ƙarni na 19.

4. Adar
– Ƙaramar masarauta a Nijar da ke tsakanin Damagaram da Tessaoua, ba ta fuskanci ji

TSİNANNE Mara imaniALLAH YA Hadaka da BALA'İN su bello turji
14/08/2025

TSİNANNE
Mara imani
ALLAH YA
Hadaka da
BALA'İN su bello turji

Waye barawon acikin su
11/08/2025

Waye barawon acikin su

11/08/2025
Ba tantamaBa haufi
11/08/2025

Ba tantama
Ba haufi

®️ DON ALLAH ARINKA KOYAWA YARA IRIN WANNAN KACICI-KACICIN, SANNAN MU KANMU MURINKA CAJIN KWAKWALENMU DA IRIN WANNAN.......
10/08/2025

®️ DON ALLAH ARINKA KOYAWA YARA IRIN WANNAN KACICI-KACICIN, SANNAN MU KANMU MURINKA CAJIN KWAKWALENMU DA IRIN WANNAN.....”

1. Ayoyi nawane Qur'ani mai tsarki yake dauke dasu?.

A. 6235
B. 6666.√
C. 6237
D. 6238

2. Sau nawa kalmar Qur'an yazo acikin Alqur’an Mai girma?

A. 67
B. 68
C. 69
D. 70.√

3. Wani abun sha ne da ake sonshi sosai kuma aka ambata a Qur'ani?

A. Zuma
B. Madara.√
C. Ruwa
D. Juice

4. Wani abinci ne da akafiso kuma aka ambace shi a Qur'ani?

A. Zuma.√
B. Madara
C. Kankana
D. Dabino

5. Wacce surah ce mafi gajarta acikin Qur'ani?

A. Falaq
B. NASS
C. IKLASS
D. KAUSAR.√

6. Wani abune Allah yafi rashin kaunarsa a Alqur’ani duk da cewa halal ne?

A. Aikin Hajji
B. Mutuwar aure ko saki.√
C. Aure
D. Kisan kai

7. Wani harafine akafi amfani dashi sosai dashi acikin Qur'ani?

A. Wa
B. Ba'un
C. Alif.√
D. Qaf

8. Wani harafine akafi karancin amfani dashi acikin Qur'ani?

A. Zaa.√
B. Maa
C. Taa
D. Laa

9. Wace dabbace datafi kowacce girma da aka ambata acikin Qur'ani?

A. KifiShiaton kifin ruwa
C. Giwa.√
D. Macijiya

10. Wace dabbace kankanuwa da aka ambata a Qur'ani?

A. Quda
B. Sauro.√
C. Gizo-Gizo
D. Tururuwa
Ans = Saura Q.2:26

11. Wacce sura ce ke daukeda mafi qanqantan harufa a Qur'ani?

A. 41
B. Suratul kausar 42.√
C. 43
D. 44

12. Wacce surace ake kiranta da suna uwar Qur'ani?.

A. Baqara
B. Fatiha.√
C. Iklass
D. Yaseen

13. Surori nawane s**a fara da: Al-Hamdulillah?

A. Hudu
B. Biyar.√
C. Shida
D. Bakwai

[ Fatihah, Anaam, Kahf, Saba & Fatir ]

14. Surori nawane sunansu harafi dayane kawai?

A. Biyu
B. Uku.√
C. Hudu
D. Biyar
[ Qaf, Sad & Noon ]

15. Surori nawane s**a fara da kalmar ‘Inna ‘?

A. Uku
B. Hudu.√
C. Biyar
D. Shida.
[ Sura Fatha, Nuh,Qadr, Kausar ]

16. Surori nawane aka saukar a makkah?
A. 85
B. 86.√
C. 87
D. 88

17. Surori nawane aka saukar a Madinah

A. 28.√
B. 27
C. 26
D. 25.

18. Wacce surace mai sunan yaren Sayyidul waraa sallallahu alaihi wasallam?.

A. Lahab
B. Quraish.√
C. Hashim
D. Sab'i

10/08/2025

Alhmdulillahi Burkina Faso muna godiya

YADDA AKE SASANCI DA YAN TA'ADDA A BURKINAFASO

Abu iri ɗaya ne ke faruwa a najeriya da Burkinafaso da wasu yankunan kasar Mali da Nijar.

Amma kalli irin yadda ake cin uban waɗannan yan ta'addan a Burkinafaso da Nijar da Mali. Domin rage mumunan iri

Amma a najeriya labarin ya bambanta sosai. Nasarar yan ta'adda tafi ta jami'an tsaro yawa.

Meyasa? Alhmdulillahi kaji maza Burkina Faso muna godiya

Tambayoyi biyar zuwa ga Sheikh Musa Yusuf  Asadussunnah da duk masu neman sasanci wa ƴan bindiga.1)  Shin da a ce ƴan Sh...
05/08/2025

Tambayoyi biyar zuwa ga Sheikh Musa Yusuf Asadussunnah da duk masu neman sasanci wa ƴan bindiga.

1) Shin da a ce ƴan Shi'a ne ko ƴan qur'aniyun suke yin abin da ƴan bindigar nan suke yi a Arewa, zaku dage wajen neman gwamnati tayi sasanci dasu?

2) Shin da ace Sheikh Abduljabbar ne ya zama ya haɗa rundunar ɗaluban sa ya ɗauki mak**ai yake yiwa musulmai irin abinda Bello Turji yake yi a dazukan Zamfara da Sokoto, zaku dage akan sai anyi sasanci dashi?

3) Shin da ace Inyamurai ne suke ɗauke da miyagun mak**ai suke kashe manya da yara kuma suyi ma mata fyaɗe k**ar yadda Fulanin daji sukeyi, zaku dage akan sai anyi sasanci dasu ko da inyamuran ɗaukan fansa sukeyi?

4) Shin da ace Kiristocin Arewa ne tare da maguzawan Arewa s**a haɗe kai suke tashin garuruwan musulmi zaku dage akan ayi sasanci dasu ko da anyi musu laifi ne?

5) Inda ace a zamanin Manzon Allah kawai sai aka samu wasu ƴan ta'adda s**a je s**a kwashi wasu daga cikin sahabban sa kuma s**a yiwa matayen su fyaɗe sannan s**a ce sai an biya maƙudan kuɗin fansa. Shin manzon Allah da su sayyadina Umar, Ali, Abubakar, da irin su Hamza, Abdullahi bn Zubair da su Abu Zarr, Khalid bin Waleed, zasu nemi aje ayi sasanci da irin waɗannan mutane?


Note: A tambaya ta 5 kar ma a soma bamu misali da sulhun Hudaibiyya ko wani abu da yayi k**a da haka. Domin sulhun hudaibiyya yarjejeniya ce akan buƙatu na addini da ibada kuma sana karya alƙawari annabi ya yaƙe su.

A fito a bamu amsa.

Abba M Abba M Sabilu

MADA İKON ALLAH
22/07/2025

MADA İKON ALLAH

Address

MADA Kware
Gusau

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Bushira bala mada posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share