Zamfara Online

  • Home
  • Zamfara Online

Zamfara Online Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from Zamfara Online, Newspaper, .

Muna yaba wa Minista Matawalle wajen kara karfafa tsaron Nijeriya - Kungiyar Northern Concern CitizensƘungiyar Northern ...
21/10/2025

Muna yaba wa Minista Matawalle wajen kara karfafa tsaron Nijeriya - Kungiyar Northern Concern Citizens

Ƙungiyar Northern Concerned Citizens ta yaba da irin namijin kokarin ministan kasa a ma'aikatar tsaron Nijeriya, Dr Bello Muhammad Matawalle, MON, wajen sauya tsarin tsaro da karfafa guiwar jami’an tsaro a fadin Nijeriya.

Sakataren ƙungiyar ‘yan Arewa masu kishin kasa, Muhammad Abdullahi, ya ce, tun bayan da aka nada Matawalle mukamin ministan tsaro a watan Agustan 2023, ya nuna ƙwazo, hangen nesa da jajircewa wajen tabbatar da ci-gaban da ake samu a yaki da ta’addanci da ‘yan bindiga.

Haka kuma, Dr Bello Matawalle ya nuna kwarewa a shugabanci mai tasiri wanda ya kara wa hukumomin tsaro kwarin guiwa, tare da bai wa ‘yan Nijeriya sabuwar fata da kwarin guiwa kan abubuwan da s**a shafi tsaro.

Ƙungiyar ta kuma yaba wa yadda Matawalle ke tallafar haɗin-kai tsakanin hukumomin tsaro, tare da kira da a karfafa saka hannun jari da kuma samar da wadatattun kudade ga bangaren tsaro domin kara daukar matakai wadanda za su yi tasiri kan yaki da ‘yan ta’adda da sauran matsalolin tsaro.

Abdullahi ya kara da cewa, kulawar ministan ga walwala da jin dadin sojoji, musamman ta hanyar shirye-shiryen inganta harkar lafiyar sojoji da haɗin guiwa da ƙasashen waje, na nuna irin shugabanci mai cike da kishin jama’a da Matawalle ke jagoranta.

A cewarsa, shugabancin Bello Matawalle ya bambanta domin ba kawai filin daga ya mayar da hankali ba, lafiyar ma’aikatansa ma bai manta da ita ba. Wannan shi ne ainihin shugabanci na gaskiya a bangaren tsaro.

A karshe, Abdullahi ya bukaci gwamnati, majalisa, kamfanoni da jama’a da su ci-gaba da mara wa ma’aikatar tsaro baya wajen tabbatar da ci-gaba, inganta kayan aiki da karfafa dabarun tsaro.

Abdullahi ya ce, “Ginin da Matawalle ke shimfidawa a yau shi ne ginshikin karfin tsaron Nijeriya na shekaru masu zuwa.”

20/10/2025

Mu yan Darika tujjaniya mun Shirya wallahi sai mun ga Zannan Bungudu bai yi nasara ba, domin ya nuna muna mu ba kowa ba ne- Shugaban Matasan Yan Darika na Zamfara

Malamai a jihar Zamfara sun cancanci girmamawa, ba amfani da su don cimma wata manufa ta siyasa ba — cewar kungiyar da k...
20/10/2025

Malamai a jihar Zamfara sun cancanci girmamawa, ba amfani da su don cimma wata manufa ta siyasa ba — cewar kungiyar da ke rajin samar da kyakkyawan shugabanci a jihar Zamfara.

Kungiyar rajin samar da kyakkyawan shugabanci ta jihar Zamfara, wato Zamfara Good Governance Forum, ta nuna damuwa kan yadda gwamnan jihar Zamfara, Dauda Lawal Dare ke kokarin amfani da manyan malamai na jihar domin cimma muradun siyasa yayin da ake dab da zaben 2027.
Kungiyar ta bayyana wannan mataki nasa a matsayin rashin gaskiya da neman amfani da addini wajen neman goyon bayan jama’a, abin da ya saba da tsarin mutuntaka da girmamawa da tsohon gwamnan jihar kuma ministan tsaro, Dr Bello Muhammad Matawalle, ya kafa tsakanin gwamnati da malamai.

A zamanin mulkin Matawalle, gwamnatin jihar ta bai wa malamai babban matsayi, ta kuma ba su muhimmanci a cikin tafiyar da mulki, tare da samar musu da ofishi na dindindin a gidan gwamnati. Haka kuma, ya gina musu katafaren ofishi mai dauke da ɗakin karatu na addinin Musulunci wanda ke cike da littattafai na addini da na zamani, tare da kula da jin dadinsu da ci-gaban iliminsu ta hanyar tallafa musu su yi karatu a cikin gida da waje.

A cikin nuna tawali’u da girmamawa ga ilimi, Dr Matawalle ya gayyaci fitattun malamai kamar Malam Aminu Daurawa da Farfesa Isa Ali Ibrahim Pantami domin kaddamar da sabon ofishin malamai, alamar da ta nuna jajircewarsa wajen inganta ilimin addini, zaman lafiya da kyakkyawan shugabanci a jihar Zamfara.

Sai dai bayan Gwamna Dauda Lawal Dare ya hau mulki, ya rusa wannan ginshikin alheri ta hanyar korar malamai daga ofishinsu a gidan gwamnati, sannan ya mayar da wurin ofishin uwargidan gwamna. Rahotanni sun nuna cewa an kashe miliyoyin kudaden jama’a wajen sake gyaran ofishin domin nuna alfarma da jin dadi, abin da ya zubar da mutuncin malamai da kuma tarihi na addini a jihar.

Yanzu kuma, wannan gwamna da ya raina malamai da ayyukansu shi ne yake sake gayyatarsu domin yin addu’a ga jihar, abin da kungiyar ta bayyana a matsayin wani yunkuri na siyasa domin amfani da tasirin malamai wajen neman goyon bayan jama’a kafin zaben 2027.

Kungiyar ZGGF ta bukaci malamai su tuna bambanci tsakanin gaskiya da nuna sha’awa ta siyasa. Dr Bello Matawalle ya kula da su cikin mutunci da girmamawa a matsayin abokan tafiya wajen kyautata shugabanci, ba kayan amfani a siyasance ba.

A cewar kungiyar, jama’ar Zamfara har yanzu suna tuna zamanin da girmamawa, zaman lafiya da hadin-kai na addini s**a mamaye gwamnatin Matawalle.

Daga karshe, kungiyar ta ce, Zamfara tana bukatar shugabanci na gaskiya, girmamawa da mutunci ba na yaudara, girman kai da son kai ba.

Comr Anas Kaura ya raba motoci, babura, kekunan dinki, Filayen Dan Gina muhalli, kadda mar da ginin islamiyya da injin n...
19/10/2025

Comr Anas Kaura ya raba motoci, babura, kekunan dinki, Filayen Dan Gina muhalli, kadda mar da ginin islamiyya da injin nika da kudi tsaba Naira milyan 30 ga al'ummominsa

Fitaccen dan siyasa Kuma na hannun damar minister tsaro Bello matawalle da jihar Zamfara, Comr Anas Abdullahi Kaura, ya bayyana cewa zai ci gaba da tallafa wa jama’ar yankin Kaura Namoda da kewaye domin inganta rayuwar matasa, mata da marasa karfi, tare da karfafa su wajen dogaro da kai.

Comr Anas, wanda shi ne Madakin Kaura, ya bayyana hakan ne a lokacin da ya kaddamar da rabon kayan tallafi ga al’ummar yankin, inda ya bayar da babura kirar Bajaj, da kuma roba-roba masu yawa, motoci, keken dinki na zamani masu yawa, injinan nika masu yawa, Filin domin Gina muhalli ga mutun biyar, kaddamar da ginin makarantar islamiyya.

Kazalika, Comr Anas Kaura da ya raba kudi tsaba Naira miliyan 30 domin tallafar masu kananan sana'o'i da ma waɗanda za su fara domin dogaro da kansu.

Wannan rabon kayan ya gudana ne a garin Kaura Namoda, jihar Zamfara.

A cewar, Mai magana da yawun sa Suleiman yusuf Usman sketch Kaura, Anas kaura shi ne na hannun daman ministan kasa a ma’aikatar tsaron Nijeriya, Dr. Bello Muhammad Matawalle, ya ce wannan tallafi wani bangare ne na jajircewarsa wajen ganin matasa da marasa karfi sun samu abin dogaro.

“Wannan shiri ne na ci gaba da taimaka wa jama’a don su sami sana’a ta hannunsu. Zan ci gaba da irin wannan tallafi a cikin al’umma, domin mu gina rayuwar matasanmu da kananan ‘yan kasuwa su dogara da kansu.”

Suleiman sketch Wanda shine Mai Kula da harkar media ta Anas Ya kuma yi kira ga al'ummar jihar Zamfara da su kara hakuri da halin da suke ciki a karkashin gwamnatin PDP, yana mai cewa jam’iyyar ta gaza samar da cigaba da tsaro ga al’umma.

Suleiman sketch yace comrade Anas kaura yayi kira ga al'ummar jihar Zamfara da su zabi jam’iyyar APC a zaben mai zuwa domin dawo da zaman lafiya, da tabbatar da gwamnati mai kishin al’umma,” in ji shi.

Rahotanni sun bayyana cewa wannan ba shi ne karo na farko da Madakin Kaura ke yin irin wannan agaji ba, domin ya saba raba tallafi ga marasa karfi musamman a lokutan sallah da azumi, tare da taimaka wa matasa da kananan ‘yan siyasa domin samun damar ci gaba a harkokin rayuwa da siyasa.

Yazid Danfulani na jagorantar gyaran tsarin inshorar noma da Shugaba Tinubu ya bullo da shi — In ji wata ƙungiyaShugaban...
19/10/2025

Yazid Danfulani na jagorantar gyaran tsarin inshorar noma da Shugaba Tinubu ya bullo da shi — In ji wata ƙungiya

Shugaban Hukumar Inshorar Manoma ta Ƙasa NAIC, Dr. Yazid Shehu Umar Danfulani, ya samu yabo bisa jagorantar abin da da dama ke kira daya daga cikin manyan gyare-gyare masu cike da tarihi da hukumar ta taɓa gudanarwa.

A wata sanarwa da Ƙungiyar Matasan manoma Youth Association of Agriculture Forum – YAA ta fitar a ranar Talata, jagoran ƙungiyar, Dr. Yusuf Adams, ya yaba da ƙoƙarin Dr. Danfulani na gina cikakkiyar katangar da za ta ba da kariya ga sashen noma a Nijeriya.

A cewar Dr. Adams, Hukumar Inshorar Manoma ta Ƙasa NAIC tana fuskantar sauyi mai ma’ana a ƙarƙashin “jagoranci mai hangen nesa da son gyara” na Danfulani, wanda yake daidai da shirin Shugaba Bola Ahmed Tinubu na farfaɗo da harkar noma.

Tun bayan da ya hau kujerar shugabanci a watan Mayun 2025, Danfulani ya ƙaddamar da jerin matakai domin ƙarfafa wadatar abinci, ƙara juriyar yanayi, da buɗe sabbin damarmakin kasuwanci a fannin noma.

Ƙungiyar YAA ta bayyana cewa waɗannan gyare-gyare suna nuna yadda shirin Tinubu ke nufin bunƙasa yankunan karkara ta hanyar ingantaccen tsarin inshorar noma da ya haɗa da amfanin gona, dabbobi da kayan aikin gona.

A karkashin jagorancin Danfulani, hukumar NAIC ta faɗaɗa inshorar zuwa ƙananan ƙauyuka da ƙungiyoyin manoma da ba su taɓa amfana ba a da. Haka kuma hukumar ta ƙaddamar da sabbin hanyoyin kimanta hadurra ta hanyar fasaha domin hanzarta biyan asarar da manoma s**a yi cikin lokaci.

Bugu da ƙari, hukumar NAIC ta fara haɗin gwiwa da gwamnatocin jihohi da masu ruwa da tsaki na kamfanoni masu zaman kansu domin faɗaɗa tasirin ayyukanta, tare da shirya horon manoma don ƙara wayar da kai kan muhimmancin inshora a matakin ƙasa.

Dr. Adams ya ce waɗannan matakai sun nuna canji daga kalaman manufofi zuwa ayyuka na zahiri, inda ya jaddada cewa jagorancin Danfulani “yana mayar da hangen nesa na Shugaba Tinubu kan inshorar noma zuwa ainihin ci gaba mai auna sakamako.”

Ya ƙara da cewa, “Yayin da Nijeriya ke tunkarar sabon salo na ingantaccen noma da masana’antu, Dr. Yazid Danfulani yana zama ginshiƙi wajen fassara shirin ‘Sabon Fata na Renewed Hope’ na Shugaba Tinubu zuwa ci gaban yankunan karkara mai dorewa — gona ɗaya, manufa ɗaya, makoma ɗaya.”

Kungiyar Zamfara rajin samar da shugabanci na gari Good Governance Forum ta yaba wa Minista Bello Matawalle bisa kafa ta...
18/10/2025

Kungiyar Zamfara rajin samar da shugabanci na gari Good Governance Forum ta yaba wa Minista Bello Matawalle bisa kafa tarihin sabunta tattalin arzikin jihar Zamfara da samar da ci-gaba wajen samar da kudaden shiga a jihar

Kungiyar rajin kyakkyawan shugabanci ta jihar Zamfara Zamfara Good Governance Forum ta sake yabawa da jagorancin tsohon gwamnan jihar kuma Ministan kasa a ma'aikatar tsaron Nijeriya, Dr. Muhammad Bello Matawalle, MON, tana mai bayyana mulkinsa a matsayin wani “zamani mai armashi” na gyara tattalin arziki, gaskiya da rikon amana, wanda ya dora jihar Zamfara bisa turbar tattalin arzikin Nijeriya.

A wata sanarwa da sakataren ƙungiyar, Muhammad Ibrahim Marafa, ya fitar, ta bayyana cewa a lokacin mulkin Matawalle, jihar Zamfara ta samu ƙaruwar kashi 171 na kudaden shiga da take tarawa IGR, wanda hakan ya sanya ta zama jihar da ta fi kowace jiha ci-gaba a fannin tara kudaden shiga kamar yadda rahoton hukumar kididdiga ta kasa (NBS) na shekarar 2019 ta bayyana.

Marafa ya ce wannan nasara ba ta samu da sa’a ba ko kuma farfaganda, illa sakamakon shugabanci mai cike da hangen nesa, gaskiya da jajircewa wajen gudanar da al’amurra cikin gaskiya da rikon amana.

Ya kara da cewa, Matawalle ya nuna shugabanci na gaskiya ta hanyar inganta sana’o’in matasa, karfafa kananan ’yan kasuwa da kuma jan hankalin masu zuba jari a fannoni daban-daban na tattalin arzikin jihar.

Sanarwar ta ƙara da cewa, a lokacin mulkin Matawalle, Zamfara ta yi aiki, kuma alkalumma ne s**a tabbatar da hakan. Mulkinsa ya nuna cewa da kyakkyawar niyya, da da’a da tausayi, jihar da aka raina a baya na iya zama abin koyi a kasa baki ɗaya.

Kungiyar ta kuma yi kira ga shugabanni na yanzu da masu tasowa da su yi koyi da tsarin shugabanci na Matawalle, wanda ya gina ta da ayyuka, ba farfaganda ba.

Tarihi ba zai manta da Bello Matawalle a matsayin gwamnan da ya sauya damarmakin Zamfara zuwa ainihin ci-gaba, ya fifita jama’a fiye da siyasa, kuma wanda ya tabbatar da cewa shugabanci na gaskiya ana auna shi ne da sakamako, ba da hayaniya ba.

17/10/2025

Sanarwar wayar dakan Al'ummah akan jita-jitar cewar Gwamnah Dr Dauda Lawal na jihar Zamfara zai koma APC

16/10/2025

Duk Apcn Zamfara babu wanda ya Kai kima da Darajar Gwamna Dauda Lawal, shi ya sa 'ya'yan su ke Neman ya dawo jam'iyarsu

Kungiyar Zamfara Good Governance Forum ta zargi Gwamnan jihar da tauye hakki kan kin biyan ma’aikata albashi na watanni ...
15/10/2025

Kungiyar Zamfara Good Governance Forum ta zargi Gwamnan jihar da tauye hakki kan kin biyan ma’aikata albashi na watanni takwas

Wata kungiya mai rajin samar da kyakkyawan shugabanci a jihar Zamfara, wato Zamfara Good Governance Forum, ta yi kakkausar s**a ga Gwamna Dauda Lawal Dare bisa abin da ta kira “zalunci da rashin tausayi da rashin imani ” ga ma’aikatan jihar, bayan kin biyan su albashi na tsawon watanni takwas tare da sallamarsu daga aiki.

Sakataren kungiyar, Muhammad Ibrahim Marafa, ne ya bayyana hakan cikin wata sanarwa, inda ya bayyana matakin gwamnan a matsayin abin kunya da bai dace da kowace al’umma mai mutunci da bin doka ba.

Muhammad ya ce “wannan ba shugabanci ba ne, tsantsar mugunta ce, ta yaya gwamna zai hana ma’aikata albashin da s**a yi aikinsa har tsawon watanni takwas, sannan maimakon ya tausaya musu sai ya kore su daga aiki? Wannan zalunci ne da aka lullube da sunan shugabanci.”

Hakazalika, ya siffanta wannan matsala da ibtila’i na rashin jin kai da rashin tausayi daga gwamnatin jihar, inda mutane ke fama da yunwa, yara sun daina zuwa makaranta, ga mutane da dama na kamuwa da cututtuka saboda tsare-tsaren da babu tausayi a cikin su.

Sakataren kungiyar ya cigaba da cewa, wannan gwamnati ta jefa jama’a cikin wahala mara misaltuwa. Mutanen da aka kora ‘yan Adam ne, ba kayan da za ka yi amfani ka yar ba. Duk wani shugaba mai imani ba zai bari jama’arsa su shiga irin wannan halin ba.

Kungiyar ta roki gwamnatin Nijeriya, ƙungiyoyin kwadago da masu kare haƙƙin jama’a da su shiga cikin lamarin, domin tilasta wa gwamnatin jihar ta biya duk albashin da ake bin su tare da dawo da ma’aikatan da aka kora.

Marafa ya ƙara da cewa, Gwamna Dauda Lawal ya gaza wajen tausayi da kishin jama’a.

A cewarsa, shugabanci ba ana yin sa don nuna isa da danniya ba ne, sai dai domin kula da jama’a da nuna tausayi gare su. Jihar Zamfara ta cancanci shugabanci mai adalci da tausayi, ba irin wannan ba.

Kungiyar ta kuma tabbatar da aniyarta na ci-gaba da kare haƙƙin talakawa da tsayawa tare da jama’a har sai an dawo da adalci, gaskiya, da daidaito a jihar ta Zamfara.

13/10/2025

Muddun Matawalle ya ce bai takarar gwamna a 2027 ni zan jagoranci kai kararshi kotu- Hon. Anas Abdullahi kaura

Ficewar ‘ya'yan PDP masu tarin yawa a jihar Zamfara: Dan takarar zaben cike gurbi na PDP Muhammad Kurya da magoya bayans...
13/10/2025

Ficewar ‘ya'yan PDP masu tarin yawa a jihar Zamfara: Dan takarar zaben cike gurbi na PDP Muhammad Kurya da magoya bayansa sun koma APC,
..... Tsohon dan takarar na zargin gazawar jagoranci da rashin tsari a PDP karkashin jagorancin Gwamna Dauda

Jam’iyyar PDP ta sake fuskantar babbar koma baya a jihar Zamfara, bayan da Muhammad Kurya, dan takararta a zaben cike gurbin majalisar jiha na mazabar Kaura Namoda ta Kudu da aka gudanar a watan Agustan 2025, ya sanar da ficewarsa daga jam’iyyar tare da komawa jam’iyyar APC.

Jam'iyyar PDP dai ce ke mulki a matakin jihar Zamfara, yayin da APC take matsayin babbar jam'iyyar adawa.

A cikin wata doguwar sanarwa da ya fitar wa manema labarai a Gusau, Kurya ya bayyana cewa matakin da ya dauka ya samo asali ne daga rashin tsarin jam'iyyar PDP da kuma gazawa ta fuskar jagoranci, kawuna sun rarrabu, da kuma halin yaudara da s**a durkusar da ita karkashin Gwamna Dauda Lawal Dare.

Ya zargi gwamnan da mayar da jam’iyyar da a da ta kasance kafar siyasa mai karfi a baya ya zuwa wani kamfani nasa na kashin kansa da yake jagoranta da izza da isa da girman kai, son kai, da cin amana.

Kurya ya koka cewa duk da fatar alheri da jajircewar ‘ya’yan jam’iyyar na gaskiya na asali, Gwamna Dauda ya ware wasu shafaffu da mai, ya manta da alkawuran da ya dauka lokacin kyamfe, sannan ya kasa magance matsalar tsaro da ta kara ta’azzara a karkashin mulkinsa. A cewarsa, jam'iyyar PDP a jihar Zamfara ta rasa tsari da manufa, abin da ya bar jiga-jiganta da dama cikin takaici.

“PDP a jihar Zamfara a yau ba jam’iyyar talakawa bace. Ta zama jam’iyyar mutum daya wadda son kai da girman kai ke tafiyar da ita. Gwamna Dauda Lawal ya maida matsalar tsaron da ke addabar jiharmu siyasa, ya ki tuntubar masu ruwa da tsaki, ya kuma yi watsi da halin kuncin da talakawa ke ciki. Ba zan ci gaba da kasancewa cikin tsarin da ya rasa mutunci da tausayi ba,” in ji Kurya.

Tsohon dan takarar PDP din ya bayyana matukar girmamawarsa ga jajircewar Ministan kasa a ma'aikatar tsaron Nijeriya, Hon. Bello Muhammad Matawalle, da kuma Sanata Abdulaziz Yari Abubakar, wadanda ya bayyana a matsayin nagartattun ‘yan siyasa masu kishin kasa da kare muradun al’ummar jihar Zamfara.

“Matawalle da Yari na da tausayin talakawa a ransu, suna son zaman lafiya da ci gaba. Sadaukarwarsu wajen tabbatar da tsaro, hadin kai da tallafa wa jama’a na ci gaba da zama abin koyi gare mu. Komawa ta cikin APC karkashinsu mataki ne na sake gina jiharmu da dawo da amincin jama’a ga gwamnati,” in ji shi.

Kurya ya sake jaddada cikakkiyar biyayyarsa ga jam’iyyar APC tare da alwashin bayar da gudunmawa wajen karfafa jam’iyyar kafin manyan zabubbuka masu zuwa. Ya ce matakin da ya dauka na nuna yadda jama’ar jihar Zamfara ke kara fahimtar cewa APC ce kadai jam’iyyar da ke da nagartaccen shugabanci da jajircewa wajen kai jiharsu ga zaman lafiya, ci gaba da gaskiya.

12/10/2025

Yadda matashin dan siyasa ya bayar da mamaki tare da girgiza yan siyasa da al'ummar Zamfara ta hanyar yin abin alherin da wani dan siyasa bai taba yinsa ba

Address


Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Zamfara Online posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Zamfara Online:

  • Want your business to be the top-listed Media Company?

Share