24/05/2026
YANZU-YANZU: Ɗan Takarar Sanata na ADC Ya Tsallake Rijiya da Baya a Abuja, Ya Musanta Hannu a Rikicin Zaɓen Fidda Gwani
Ambasada Dakta Mubarak Ahmad Tijjani, ɗan takarar kujerar Sanata a ƙarƙashin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) a Babban Birnin Tarayya (FCT), ya musanta zarge-zargen da ke danganta shi da tada hankali yayin rikicin zaɓen fidda gwani na jam’iyyar, yana mai bayyana zarge-zargen a matsayin “ƙarya, yaudara, da siyasa.”
A cikin wata sanarwa da ya fitar ranar Lahadi, Tijjani ya ƙaryata rahotannin da ke yawo ƙarƙashin taken “Allah-wadai da Tada Hankali a Sakatariyar ADC ta FCT,” yana mai jaddada cewa lamarin bai faru a kowace hukuma ta ADC ba.
A cewarsa, lamarin ya faru ne a ofishin mazabar Sanata Ireti Kingibe da ke Gudu, Abuja, inda ya zargi mambobin Kwamitin Zaɓe na jam’iyyar da karkatar da muhimman kayan zaɓe maimakon kai su cibiyoyin zaɓe na unguwanni kamar yadda aka tsara.
Dan takarar ya ce dubban wakilai da magoya baya sun tsaya suna jira a wurare daban-daban ba tare da tantancewa ko kayan zaɓe ba, lamarin da ya haifar da gazawar gudanar da sahihin zaɓen fidda gwani.
Tijjani ya kuma yi zargin cewa Shugaban Kwamitin Zaɓen ne ya gayyace shi zuwa wurin taron da ke Gudu domin abin da aka bayyana a matsayin “taron masu neman takara,” amma da isarsa ba a ba shi damar bayyana ra’ayinsa ba, sannan aka kai masa hari.
“Ban zo tare da ‘yan daba ba, kuma ban kai wa kowa hari ba,” in ji shi, yana mai cewa shi ne aka kai wa hari kuma daga baya aka kwantar da shi a asibiti sakamakon raunukan da ya samu.
Ya ce rahotannin likitoci daga Asibitin Cairo da sakamakon gwajin CT scan daga Everight Diagnostics sun tabbatar da cewa ya samu mummunan rauni a kai, raunuka a jiki, tangarɗar hankali, da kuma zubar jini a kwakwalwa.
A cewarsa, an riga an miƙa rahotannin likitocin ga shugabancin ADC na ƙasa da kuma hukumomin tsaro da s**a dace.
Tijjani ya zargi wasu da ake zargin suna da hannu wajen karkatar da kayan zaɓe da lalata tsarin zaɓen fidda gwani da ƙoƙarin yaudarar jama’a ta hanyar yaɗa bayanai a kafafen sada zumunta.
Ya buƙaci mambobin jam’iyyar da jama’a su mai da hankali kan tambayoyin da har yanzu ba a amsa ba game da lamarin, ciki har da dalilin da ya sa aka kai kayan zaɓe zuwa wani ofishi mai zaman kansa, dalilin da ya sa aka bar wakilai a cibiyoyin zaɓe, da kuma rashin wata hujja da ke nuna cewa ya kai wa wani hari.
Dan takarar na ADC ya ce yanzu haka lamarin yana gaban shugabancin jam’iyyar na ƙasa da hukumomin tsaro, yana mai nuna kwarin gwiwar cewa “adalci, gaskiya, da riƙon amana za su yi nasara.”
Ya kuma buƙaci magoya bayansa da jama’a su kwantar da hankalinsu, su guji yaɗa ƙarya, kuma su goyi bayan dimokuraɗiyya.