Karamchi

Karamchi Gudan Labarai

YANZU-YANZU: Ɗan Takarar Sanata na ADC Ya Tsallake Rijiya da Baya a Abuja, Ya Musanta Hannu a Rikicin Zaɓen Fidda GwaniA...
24/05/2026

YANZU-YANZU: Ɗan Takarar Sanata na ADC Ya Tsallake Rijiya da Baya a Abuja, Ya Musanta Hannu a Rikicin Zaɓen Fidda Gwani

Ambasada Dakta Mubarak Ahmad Tijjani, ɗan takarar kujerar Sanata a ƙarƙashin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) a Babban Birnin Tarayya (FCT), ya musanta zarge-zargen da ke danganta shi da tada hankali yayin rikicin zaɓen fidda gwani na jam’iyyar, yana mai bayyana zarge-zargen a matsayin “ƙarya, yaudara, da siyasa.”

A cikin wata sanarwa da ya fitar ranar Lahadi, Tijjani ya ƙaryata rahotannin da ke yawo ƙarƙashin taken “Allah-wadai da Tada Hankali a Sakatariyar ADC ta FCT,” yana mai jaddada cewa lamarin bai faru a kowace hukuma ta ADC ba.

A cewarsa, lamarin ya faru ne a ofishin mazabar Sanata Ireti Kingibe da ke Gudu, Abuja, inda ya zargi mambobin Kwamitin Zaɓe na jam’iyyar da karkatar da muhimman kayan zaɓe maimakon kai su cibiyoyin zaɓe na unguwanni kamar yadda aka tsara.

Dan takarar ya ce dubban wakilai da magoya baya sun tsaya suna jira a wurare daban-daban ba tare da tantancewa ko kayan zaɓe ba, lamarin da ya haifar da gazawar gudanar da sahihin zaɓen fidda gwani.

Tijjani ya kuma yi zargin cewa Shugaban Kwamitin Zaɓen ne ya gayyace shi zuwa wurin taron da ke Gudu domin abin da aka bayyana a matsayin “taron masu neman takara,” amma da isarsa ba a ba shi damar bayyana ra’ayinsa ba, sannan aka kai masa hari.

“Ban zo tare da ‘yan daba ba, kuma ban kai wa kowa hari ba,” in ji shi, yana mai cewa shi ne aka kai wa hari kuma daga baya aka kwantar da shi a asibiti sakamakon raunukan da ya samu.

Ya ce rahotannin likitoci daga Asibitin Cairo da sakamakon gwajin CT scan daga Everight Diagnostics sun tabbatar da cewa ya samu mummunan rauni a kai, raunuka a jiki, tangarɗar hankali, da kuma zubar jini a kwakwalwa.

A cewarsa, an riga an miƙa rahotannin likitocin ga shugabancin ADC na ƙasa da kuma hukumomin tsaro da s**a dace.

Tijjani ya zargi wasu da ake zargin suna da hannu wajen karkatar da kayan zaɓe da lalata tsarin zaɓen fidda gwani da ƙoƙarin yaudarar jama’a ta hanyar yaɗa bayanai a kafafen sada zumunta.

Ya buƙaci mambobin jam’iyyar da jama’a su mai da hankali kan tambayoyin da har yanzu ba a amsa ba game da lamarin, ciki har da dalilin da ya sa aka kai kayan zaɓe zuwa wani ofishi mai zaman kansa, dalilin da ya sa aka bar wakilai a cibiyoyin zaɓe, da kuma rashin wata hujja da ke nuna cewa ya kai wa wani hari.

Dan takarar na ADC ya ce yanzu haka lamarin yana gaban shugabancin jam’iyyar na ƙasa da hukumomin tsaro, yana mai nuna kwarin gwiwar cewa “adalci, gaskiya, da riƙon amana za su yi nasara.”

Ya kuma buƙaci magoya bayansa da jama’a su kwantar da hankalinsu, su guji yaɗa ƙarya, kuma su goyi bayan dimokuraɗiyya.

DA DUMI-DUMI: Kwankwaso Ya Yafe Bayan Hon Fahad Dankabo Ya Kai Ziyarar Neman Afuwa Kan Wani Bidiyon BatanciA daren jiya ...
22/05/2026

DA DUMI-DUMI: Kwankwaso Ya Yafe Bayan Hon Fahad Dankabo Ya Kai Ziyarar Neman Afuwa Kan Wani Bidiyon Batanci

A daren jiya Alhamis, matashin ɗan siyasa, Hon Fahad Dankabo, tare da tawagarsa sun kai ziyarar girmamawa da neman afuwa ga madugun Dariqar Kwankwasiyya, Injiniya Rabi’u Musa Kwankwaso, bisa wani lamari da ya faru a yayin gangamin siyasa da aka gudanar a Karamar Hukumar Kabo, Jihar Kano.

Ziyarar ta biyo bayan wani abu da ya faru a ranar Talata, 19 ga Mayu, 2026, lokacin da wata yarinya da ta halarci gangamin siyasar Dankabo tare da jama’a daga Kabo ta yi wani furuci da ya ci mutuncin Jagoran Kwankwasiyya, lamarin da ya janyo ce-ce-ku-ce a tsakanin al’umma da ‘yan siyasa.

Da yake jawabi a yayin ziyarar, Fahad Dankabo wanda ya yi takarar kujerar Majalisar Tarayya ta Gwarzo/Kabo a ƙarƙashin jam’iyyar APC ya bayyana cewa ya barranta kansa gaba ɗaya daga wannan lamari. Ya ce ba zai taɓa amincewa da amfani da siyasa wajen cin mutuncin manya, iyaye da dattawan siyasa a Najeriya ba, musamman a Jihar Kano.

Ya ƙara da cewa irin wannan ɗabi’a ta sabawa tarbiyya, tsari da kuma siyasar tsafta da yake yi. A cewarsa, ganin irin tarbiyyar da ya samu da gidan da ya fito, ba zai yiwu ya zuba ido a fake da siyasa ana cin mutuncin masu mutunci a Arewa da Jihar Kano ba.

A nasa jawabin, Jagora Rabi’u Musa Kwankwaso ya bayyana farin cikinsa kan wannan mataki na ladabi da Fahad Dankabo ya ɗauka. Ya ce, ko ya san lamarin ko bai sani ba, ya yafe a madadin kansa da kuma mabiya Dariqar Kwankwasiyya, yana mai jaddada cewa siyasa gado ce, kuma ya dace a tafiyar da ita cikin mutunta juna, fahimta da lumana.

📸 Aliyu Maiwake Garo

Hon. Fahad Dankabo Ya Jaddada Tsayuwarsa Daram a APC Duk da Janyewa daga TakaraMatashin ɗan siyasa mai dimbin magoya bay...
19/05/2026

Hon. Fahad Dankabo Ya Jaddada Tsayuwarsa Daram a APC Duk da Janyewa daga Takara

Matashin ɗan siyasa mai dimbin magoya baya a Jihar Kano, Hon Fahad Dankabo, ya bayyana a fili cewa har yanzu yana nan daram a Jam’iyyar APC, duk da matakin da ya ɗauka na janyewa daga takarar Ɗan Majalisar Tarayya ta Kabo/Gwarzo a Jihar Kano.

Hon. Fahad Dankabo ya bayyana hakan ne yayin da yake mayar da martani ga tambayoyi daga jama’a da magoya bayansa, inda ya tabbatar da cewa janyewarsa daga takarar ba tana nufin ficewa daga jam’iyyar APC ba, illa biyayya ga tsari, shugabanci da muradun jam’iyyar.

Ya jaddada cewa APC ce jam’iyyarsa ta siyasa, kuma zai ci gaba da mara mata baya tare da aiki kafada da kafada da shugabanni da ‘ya’yan jam’iyyar domin tabbatar da nasararta a dukkan matakai.

Hon. Dankabo ya kuma bai wa al’ummar Kabo da Gwarzo tabbacin cewa duk da janyewarsa daga takara, zai ci gaba da hidimtawa jama’a, musamman a fannoni da s**a shafi cigaban matasa, ilimi da walwalar al’umma baki ɗaya.

Masu sharhi na siyasa na ganin wannan mataki a matsayin nuna balaga da biyayya ga jam’iyya, tare da ƙara ƙarfafa matsayinsa a siyasar Jihar Kano.

DA DUMI-DUMI: Babban Ƙanin Shugaban Tallata Tinubu, Dr. Zangina Ya Fice Daga APC Zuwa NDC, Ya Nemi Kujerar Majalisar Tar...
17/05/2026

DA DUMI-DUMI: Babban Ƙanin Shugaban Tallata Tinubu, Dr. Zangina Ya Fice Daga APC Zuwa NDC, Ya Nemi Kujerar Majalisar Tarayya

Hon. Zaharaddeen Ahmad Zangina, wanda yake babban ƙanin Dr. Sani Ahmad Zangina, shugaban masu tallata gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu, ya fice daga jam’iyyar APC tare da komawa jam’iyyar NDC domin neman takarar kujerar Majalisar Tarayya a Jihar Nasarawa.

Rahotanni sun bayyana cewa Hon. Zaharaddeen ya bayyana aniyarsa ta tsayawa takara domin wakiltar mazabar Keffi/Kokona/Karu a zaɓen Majalisar Tarayya mai zuwa ƙarƙashin inuwar jam’iyyar NDC.

Wannan sauyin sheƙa da ya yi na ɗaya daga cikin abubuwan da s**a ɗauki hankulan mutane a siyasar jihar Nasarawa, musamman ganin alaƙarsa da fitaccen mai tallata gwamnatin tarayya, Dr. Sani Ahmad Zangina.

Masu sharhi kan siyasa na ganin wannan mataki na iya haifar da sabon salo da sauyi a yanayin siyasar yankin, yayin da ake ci gaba da shirye-shiryen zaɓe a jihar.

16/05/2026

YANZU-YANZU: Waya Tsakanin Mataimakin Gwamnan kano Murtala Sule Garo, da Dan takarar Majalisar Tarayya Kabo da Kwarzo, Hon Fahad Dan kabo.

Saurari yanda jama'a suke murna.

‎Zargin yin amfani da Musa kamarawa wajen Musgunawa ƴan siyasa da Jami'ai na kara fito fili. ‎‎An samu Shakku kan kalama...
16/05/2026

‎Zargin yin amfani da Musa kamarawa wajen Musgunawa ƴan siyasa da Jami'ai na kara fito fili.

‎An samu Shakku kan kalaman Musa kamarawa kan kisan Dadiyata.

‎ Wasu masu bibiyar al’amuran siyasa da harkokin tsaro sun bayyana cewa akwai buƙatar a yi taka-tsantsan wajen karɓar irin waɗannan zarge-zarge ba tare da hujjoji sahihai ba. Sun ce babu wani mutum mai hankali da zai amince da zargi kai tsaye idan ba a gabatar da kwararan hujjoji ba.

‎A watannin baya, Musa Kamarawa ya taba yin zarge-zarge kan tsohon gwamnan jihar Zamfara kuma ministan tsaro, Bello Matawalle, inda ya danganta shi da wasu matsalolin tsaro a lokacin mulkinsa. Sai dai babu wata hukuma da ta tabbatar da waɗannan zarge-zarge.

‎Haka kuma, a baya-bayan nan, Kamarawa ya sake yin ikirarin cewa ɗan sanda Hassan Gimba yana da alaƙa da batun mutuwar ko ɓatan Dadiyata. Wannan magana ta haifar da martani daga mutane da dama.

‎Babban lauya mai kare haƙƙin bil’adama a Najeriya, Abba Hikima, ya bayyana cewa ya gudanar da bincike kan kalaman Musa Kamarawa, inda ya nuna akwai shakku da tambayoyi masu yawa da ke tattare da ikirarin nasa.

‎Haka zalika, fitaccen ɗan jarida daga jihar Kano, Nasiru Zango, ya bayyana shakku kan sahihancin wasu daga cikin kalaman da Musa Kamarawa ke yi, yana mai kira da a dogara da hujjoji da bincike mai zaman kansa kafin yanke hukunci.

‎Masu sharhi kan harkokin tsaro sun kuma bayyana cewa a lokutan rikice-rikice ko ta’addanci, ana iya amfani da bayanan karya ko zarge-zargen da ba su da tushe domin ramuwar gayya ko bata sunan wasu mutane.

16/05/2026

DA DUMI-DUMI: Yadda Al'ummar Gwarzo Da Kabo S**a Nuna Kin Amincewar Su Ga Fahad Dankabo Da Ya Janyewa Kowanne Dan Takara, Na Kujerar Majalisar tarayya Ta Kabo Da Gwarzo Dake Jahar Kano

10/05/2026

TIRKASHI: Dan Takarar Majalissar Tarayya Na Gwarzo/Kabo A Jam’iyyar APC Hon Fahad Dankabo Ya Bayyana Gwamna Abba Kabir Yusuf A Matsayin Shugaba Adali.

DA DUMI-DUMI: Manyan Alkalai, Sarakuna da Jami’an Jami’a Sun Halarci Daurin Auren Ɗan Fitaccen Lauya Muhammad DifaAn dau...
10/05/2026

DA DUMI-DUMI: Manyan Alkalai, Sarakuna da Jami’an Jami’a Sun Halarci Daurin Auren Ɗan Fitaccen Lauya Muhammad Difa

An daura auren Abdulbasit Muhammad Difa da amaryarsa Nusaiba Ibrahim Difa a ranar Asabar da ta gabata cikin wani gagarumin biki da ya samu halartar manyan baki daga sassa daban-daban na ƙasar nan.

Angon, Abdulbasit Muhammad Difa, ɗa ne ga fitaccen lauya kuma shugaban rukunin lauyoyi masu zaman kansu na SHETTIMAN LAW FIRM, Barrista Muhammad Difa, wanda ke da babban ofishi a jihar Bauchi tare da rassa a Abuja da Gombe.

Ita kuwa amaryar, Nusaiba Ibrahim Difa, ɗiya ce ga Malam Ibrahim Abubakar Difa, Babban Mukaddashin Magatakardan Jami’ar Gombe (Gombe State University), jami’ar gwamnatin jihar Gombe da ke cikin birnin Gombe.

Bikin daurin auren ya samu halartar manyan alkalai, wakilan manyan jami’an shari’a, shugabannin jami’o’i, sarakuna, hakimai sama da goma da sauran fitattun mutane daga ciki da wajen jihar.

Al’umma da dama sun shaida bikin tare da yi wa ma’auratan addu’ar samun zaman lafiya, soyayya, ɗorewar aure da albarka a rayuwarsu.

07/05/2026

RA’AYI: "Ina Da Tabbacin Shugabannin Mu Zasu Yi Mana Adalci, Kuma Da Yaddar Allah Zamu Samu Nasara Insha Allahu" Inji Dan Takarar Majalisar tarayya Ta Gwarzo/ Kabo Hon Fahad Dankabo Bayan Fitowarsa Daga Ofishin Jam’iyyar APC Ta Kasa

Address

Gwarinpa

Telephone

+2348187689638

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Karamchi posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share

Category