ABUU ASAM

ABUU ASAM الله
The only way to stop pain in your life is to accept the fact that nothing is yours, nothing was yours and nothing will ever be yours.

They are worldly attachments given by Allah, belonging to Allah and returning to Allah

Women will crying 😭😭
21/10/2025

Women will crying 😭😭

🚨 Breaking News🤦‍♂️💔💔

The richest man in Delta State and founder of Gehgeh University has lost his TikTok account with over 3 million followers 😭

There will be no more “classes” — that’s where everything used to happen 🤦‍♂️💔

Bro, it’s just crazy… Gehgeh was making millions there, and boom — it’s all gone. Losing a school, students, and money at once isn’t easy 💔

Moral lesson: Even when the empire falls, we the students will always stand by our lecturer! 🙏

21/10/2025
21/10/2025

With Triple Dollár – I just made it onto their weekly engagement list by being one of their top engagers! 🎉
20/10/2025

With Triple Dollár – I just made it onto their weekly engagement list by being one of their top engagers! 🎉

20/10/2025
20/10/2025
20/10/2025

19/10/2025
19/10/2025

SANNU AHANKALI ASIRIN MASU RURA WUTAR FADAN KABILANCI TSAKANIN HAUSAWA DA FULANI NATA KARA TONUWA

DASUNAN KUNGIYAR HAUSAWA ZALLAH SUNATA YIWA ADDININ MUSULUNCI ZAGON KASA DAYANKIN AREWACIN NIGERIA

1) ZAGI DACIN MUTUNCIN MALAMAN ADDINI
2)YAKAR DUKKAN WANI SARKI KO MAI RIKE DA MADAFUN IKO MUDDIN YANADA ALAKA TA JININ FULANI ATARE DASHI
3) ZAGI DACIN MUTUNCIN MUJADDADI SHEHU USMAN DAN FODIO
4)KIRA DACEWA KADA AZABI FULANI AKOWANE IRIN MATAKIN SHUGABANCI A NIGERIA

TABBAS MUNDADE MUNA ZARGIN KWANGILA S**A KARBO DON RUSA ZAMAN LAFIYAR YANKIN AREWA GASHI GASKIYA TABAYYANA KAMAR YADDA NASIRU ADAMU ELHIKIYA YABAYYANA GAMEDA JAGORANSU DAYAKE DAUKAR NAUYINSU👇👇👇

Abu nusaiba✍️✍️✍️

MU HASKA UBAN ‘YAN KWANGILAR RUSA AREWA OUBA NA KAMARU DON HAR YAU BA MU MANTA DA MARWA MAITATSINE BA!

K**ar yanda na baiyana a rubuce-rubuce na da su ka gabata, ‘yan kwangilar rusa Arewa da yaki da musulmi da musulunci, su na nan a ciki da wajen Najeriya. K**a daga yara ‘yan soshiyal midiya zuwa gagga masu daukar nauyin aikin. Ouba Ali Mohaman jigo ne ko uban gida ne ga ‘yan kwangilar nan na Najeriya. Dan Jamhuriyar K**aru ne da bayanansa su ka nuna ya na zaune a babban birnin kasar Yaounde amma asalinsa daga Tibati ne a nan K**aru. Ya yi tafiye-tafiye kasashe ciki kuwa da Amurka inda a 2018 ma ya shiga Washington DC har ya gana da wasu ‘yan jarida. Tibati da ke zama gida a wajensa na da rinjayen Fulani mazauna sai kabilar da ta yi ruwansa Mbun mai masarautar Bamun. Wannan mutumin shi ke zama babban mai goya ‘yan kwangilar rusa Arewa da amfani da bakaken maganganu wajen zagin Shehu Mujaddadi da kalmomin ingiza al’ummar Arewa su shiga yakin kabilanci. In ka bi sawun ‘yan kwangilar nan su kan shiga K**aru kuma ina ganin biri ya yi k**a da mutum don su na da Kartagi uban ‘yan c**a.

Abun da ya fi daukar hankalina shi ne Marwa ko Maroua Maitatsine daga K**aru da ya shigo Najeriya ya haddasa kisan gilla ga mutane bila-adadin wasu ma ta hanyar yankan rago. Kanawa, Barnawa, Adamawa da Gwambawa za su fi sanin labarin wanda mugun mutumin mai wa’azin kala-kato da ya jagoranci ta’addanci a garuruwanmu na Arewa. Akasari yara ‘yan bana bakwai ba su san me ya faru ba, amma an zo a na murde wuyan tarihi a soshiyal midiya inda kowane zindiki zai hau ya rubuta abun da ya ga dama. Ouba Ali Mohaman na layi mai hatsarin gaske don irin bayanan da ya ke yadawa. Mutumin da ke da’awar shi farfesa ne amma ba shi da aiki sai daurewa masu kunna wutar kabilanci baya da iza wutar aibanta jagorori masu daraja a Najeriya irin Shehu Mujaddadi, Sir Ahmadu Bello da sauran manyan malaman Islama. Mutumin nan da ke K**aru amma hankalinsa ya na kan arewacin Najeriya da ya ke aikin kunna wutar fitinar kabilanci. Hakika tamkar ga masu tattara kirare a Arewa amma ga mai ashana can a K**aru. Kafin ashana ta iso, ya dace hukumomi su taka ma ta birki.

Har wata kungiya ta farafganda ya ke kanbamawa wai “Hausa Hackathon” da ke da lambar sadarwar salula ta kasar Faransa. Mun san cewa Faransa ta mara baya lokacin da Odumegwu Ojukwu ya aiyana kafa kasar Biyafara a 1967. Don haka ba mamaki ka ga ‘yan kwangilar nan na kururuwar lallai sai a sake Nnamdi Kanu mai IPOB da a ke zargi da cin amanar kasa da ta’addanci. Hausa Hackathon har lambar yabo ta ke damkawa wanda ya tsine a harkar kwangilar rusa Arewa.

Ouba har kartar kasa ya ke yi ta rashin kunya ga shugaba Bola Ahmed Tinubu wai ya biya diyya ga wadannan masu ikirarin karyar kare Hausawa Naira tiriliyan 900!. In mun yi lissafi da kasafin kudin Najeriya na bana Naira tiriliyan 54.9 a matsayin mizani, ya nuna diyyar za ta kai kimanin kasafin kudin Najeriya na shekaru 17. Tun da Ouba ya dau kan sa a matsayin madugu na wadannan ‘yan kwangila har ya na maganar diyya, sai ya baiyana ma na shin shi za a ba wa diyyar ya raba ko zai zo a tawagar su kanwa uwar gami don karbar makudan kudin nan.

Zan yi amfani da wannan dama wajen kira ga gwamnatin Najeriya ta bukaci gwamnatin Jamhuriyar K**aru ta miko ma ta wannan mutumin don gudanar da bincike kan aiyukan ingiza matasa da ya ke yi da ka iya kunna gagarumar fitina a Arewa. Na tabbata akwai bayanai a kan Ouba da wadanda ya ke hulda da su a nan Najeriya. In ba mugunta ba, me zai sa wani da ke zaune a K**aru ya rika cillo harshen wuta cikin Najeriya. Ba mu son fitina da kowa. Najeriya uwa ce a Afurka kuma duk wani dan Afurka musamman a Afurka ta yamma ya san zaman lafiyar Najeriya salama ne ga daukacin yankin ECOWAS/CEDEAO mai kasashe 15 gabanin ballewa a siyasance ta Nijar, Mali da Burkina Faso.

A karshe kowa ya zauna lafiya shi ya so. Kar wani ya ga ya na hawa soshiyal midiya ya na zage-zage kuma ya kwana lafiya, hakika wataran mai karambani zai gamu da hushin hukuma. Ai ba wani ‘yancin fadar ra’ayi da ya ba wa wani dama ya muzanta wani shugaba da bakin fenti kuma ya yi tunanin banza ta sha. Ba wanda ya hana kowa fadar ra’ayinsa amma ba ta hanyar cin mutunci ko iskanci ba. Duk wanda bai san haka ba, ya tambayi masana shari’a da ya yarda da su, su yi ma sa bayani na iyakokin hurumin fadar ra’ayi. Ko dai jagororin wadannan ‘yan kwangila su ja birki ga karnukan farautarsu ko kuma doka ta yi aikinta.

Gani ga wane ya ishi wane tsoron Allah kuma ko bai san Allah ba ya san tsumagiya.

Nasiru Adamu El-hikaya

Address

Rainbow Town 23 Ibro Avenue
Hadejia

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when ABUU ASAM posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share