kurmin KOGI MEDIA

kurmin KOGI MEDIA wannan shafi ne dazai ke, kawo muku labaran harkar musulunci, da sayyid zakzaky (H) yake Jagoranta. Shafin yankin gabas zaria, kurmin kogi kogi.

Kuyi joined da telegram channel namu.

Labari cikin hutuna yayin gudanar da aikin daren 21 ga watan ramadan a garin kurmin kogiallah yakarbi ibadunmu
20/03/2025

Labari cikin hutuna yayin gudanar da aikin daren 21 ga watan ramadan a garin kurmin kogi

allah yakarbi ibadunmu

Yadda taron bikin mauludin Imam Ali (ع) ya gudana a da'irar kurmin kogi. Labari cikin hotuna. 27/02/2025Photos: Aliyu ha...
27/02/2025

Yadda taron bikin mauludin Imam Ali (ع) ya gudana a da'irar kurmin kogi. Labari cikin hotuna.

27/02/2025
Photos: Aliyu haidar last done

GAGARUMIN TARON NISFU SHA'ABAN A ABUJANISFU SHA'ABAN 1446AH/2025Taken Taro:- Ma'anar Intizar :- Nauyin daya hau kan masu...
11/02/2025

GAGARUMIN TARON NISFU SHA'ABAN A ABUJA

NISFU SHA'ABAN 1446AH/2025

Taken Taro:- Ma'anar Intizar :- Nauyin daya hau kan masu jiran Imam Mahdi (atfs) domin yaqar zalunci da tabbatar da adalci

Harkar Musulumci karkashin jagorancin Sheikh Ibraheem Ya'qoub El-Zakzaky (H)

Tana farin cikin gayyatar daukacin al'ummar Musulmai zuwa wajen gagarumin taron tunawa da ranar da aka haifi SAHIBUL ASAR (Imam Al-Mahdi A.S) da JAGORAN MU (Sheikh Ibraheem Ya'qoub El-Zakzaky H)
Taron Wanda aka Saba gudanarwa duk shekara, a wannan shekarar ma insha Allah za'a gabatar da taron ne a Babban Birnin Tarayyar Nigeria.

Taron zai gudana ne, kamar haka :-

Rana Ta farko: 14th Sha'aban 1446 daidai da
13th February 2025

Display da kacici kacici
Tare da Majalisin mawaqa.
Lokaci: 4:00pm

Rana Ta Biyu :- 15th Sha'aban 1446AH dai dai da 14th February, 2025

Lokaci :- karfe Biyu na rana (2:00pm)

Wuri :- ABUJA.

Allah ya bada Ikon halarta

Sanarwa daga
Sisters Forum, Academic Forum da Mu'assasatu Abul-Fadl Abbas karkashin jagorancin Sheikh Ibraheem Ya'qoub El-Zakzaky (H)

JAWABIN H-C A YAYIN GANAWA DA JAGORA (H) DA HARISAWA. ADUBA KASAN COMMENT.
06/02/2025

JAWABIN H-C A YAYIN GANAWA DA JAGORA (H) DA HARISAWA.

ADUBA KASAN COMMENT.

LABARI CIKIN HOTUNA DAGA IKARA.Yadda muzaharar IKara LGEA ta guna yau, acikin garin ikaran, Ba laifi an samu halartar mu...
05/02/2025

LABARI CIKIN HOTUNA DAGA IKARA.

Yadda muzaharar IKara LGEA ta guna yau, acikin garin ikaran,
Ba laifi an samu halartar mutane maza da mata, da yara da kuma yan fareti. Allah ya karbi sa'ayi.

Daukar hoto 📸 and
Wallafawa da'irar kurmin KOGI yankin gabas.

Hiz*bul*lah sunyi kakkausan s**a akan matakin gwamnatin Australia na ƙaƙabawa shugaban ta Sheikh Naem Qassem takunkumi, ...
05/02/2025

Hiz*bul*lah sunyi kakkausan s**a akan matakin gwamnatin Australia na ƙaƙabawa shugaban ta Sheikh Naem Qassem takunkumi, tana cewa wannan yana nuna yadda ake amfani da Australia wajen cimma manufofin Amurka da Israel.

kasuwar baje-koli ta Haramin Imam Hussain (A.s.) Sun saka Wani littafi na tarihin Jagora  Sayyid Zakzaky (H) mai suna *A...
05/02/2025

kasuwar baje-koli ta Haramin Imam Hussain (A.s.) Sun saka Wani littafi na tarihin Jagora Sayyid Zakzaky (H) mai suna *Al-Abdus-Salih* na wani Marubuci Malami a hauzar Qom dake Ƙasar Iran *Sheikh Iman Noorazy*

kurmin KOGI MEDIA
Mairauny zainul

Mauludin Gwarazan Karbala: JAGORA YA GANA DA ‘YAN MU’ASSASATU ABUL FADL ABBAS (AS)Daga Ofishin Jagora Shaikh Ibraheem Za...
05/02/2025

Mauludin Gwarazan Karbala: JAGORA YA GANA DA ‘YAN MU’ASSASATU ABUL FADL ABBAS (AS)

Daga Ofishin Jagora Shaikh Ibraheem Zakzaky (H)

Da yake ganawa da mambobin Mu’assasatu Abul Fadl Abbas, wanda s**a hada har da bangarorinta irin su Kasshafa, Intizar da JASAZ, a ranar Talata 5 ga watan Sha’aban 1446 (4/2/2025), Jagora Shaikh Ibraheem Zakzaky (H) ya jaddada bukatar sadaukarwa ga addini saboda Allah.

Jagoran, ya fara jawabinsa ne da taya ‘yan uwa murna da zagayowar kwanukan haihuwan gwarazan Karbala, wanda yace, ba zai zama a bisa hadari ba ne haihuwarsu ya zo a jere. “Na farkonsu Abi Abdullahil Husain (AS) wanda aka haifa ranar 3 ga watan Sha’aban; Sai kuma na biyunsu, dan uwansa wanda ya ba da ransa wajen kare shi, Abul Fadl Abbas, haihuwarsa ta kasance ranar 4 ga wata. Sai kuma Imam Zainul Abidin, wanda muna iya cewa shi ma ya fi kowa shan wahalar Karbala, don akan idonsa aka yi komai, shi kuma haihuwarsa ta zo ranar 5 ga wata.”

Yace: “Duk wadannan gwaraza, duk cikansu ‘rumuz’ (alamomi) ne na sadaukarwa, kowannensu an haife shi a gwagwarmaya, ya bar duniya a gwagwarmaya.”

Jagora ya bayyana yadda mahaifiyar Sayyid Abbas ta yi masa tare da ‘yan uwansa tarbiyar girmama ‘ya’yan Sayyida Zahra (SA), wanda haka yasa ko da suke uba daya, amma basu ganin ‘ya’yan Sayyida Fatima a matsayin ‘yan uwansu, face a matsayin shugabanninsu.

Yace: “Sayyida Ummul Banin, mahaifiyar Sayyid Abbas bata taba daukan Sayyida Zahra a matsayin kishiyarta ba, tana ganinta a matsayin shugabarta ne, kuma tace ma danta Abul Fadl Abbas, na haneka, kar ka kuskura kace ma Husaini ‘akhiy’ (dan uwana), kace masa ‘Sayyidiy wa maulaya’, domin Sayyidinka ne kuma Maulanka, shi shugabanka ne.”

Ya cigaba da cewa: “Saboda haka kullum shi Abul Fadl Abbas abin da yake kiran Imam Husaini shi ne ‘Sayyidi wa Maulaya’, sai sau daya rak ya taba kiransa da ‘dan uwansa, shi ne ranar Shahadarsa bayan an harbe shi da kibiya a wajen debo ruwa.”

Aduba comment

Yadda Mauludin imam hussain (AS) dana dansa imam Aliyu Zainul abideen (AS).  Ya Gudana a da'irar kurmin kogi,  an fara g...
04/02/2025

Yadda Mauludin imam hussain (AS) dana dansa imam Aliyu Zainul abideen (AS). Ya Gudana a da'irar kurmin kogi, an fara gudanar da taron da karatun qur'ani mai girma, sai fagen mawaqa dasu gwangwaje da baitoci na hikima.

Taron yaci gaba da Tafiya yadda aka tsarashi, inda malam Usman abdullahi wakilin yan Uwa na, kurmin kogi ya gudanar da jawabai na duka bangarorin.

An kammala taron da rufeshi da addua, yan Uwa sun samu halarta, maza da Mata.

Masha Allah

Muna taya al'ummar Musulmi murnar zagayowar ranar haihuwar Imam Zainul Abideen (AS) ranar 5 ga watan Sha'aban. السلام عل...
04/02/2025

Muna taya al'ummar Musulmi murnar zagayowar ranar haihuwar Imam Zainul Abideen (AS) ranar 5 ga watan Sha'aban.

السلام عليك يا زين العابدين وسيد الساجدين وقرة عين العابدين.

Address

Kaduna
Ikara
801126

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when kurmin KOGI MEDIA posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share