Arewa Content

Arewa Content Domin tallata kasuwancin ku' ko mu'amala damu, ku tuntuɓe mu ta wannan number 07012613017

I am Prince Auwal Hdgg, a
Social media King, Experienced,Researcher, motivational speaker and more.

Bari muyi musu adalci dukkanin suA zahirin Gaskiya tabbas Kannywood ta taimaki Alhikima domin dalilin ta aka sanshi ga b...
02/07/2025

Bari muyi musu adalci dukkanin su

A zahirin Gaskiya tabbas Kannywood ta taimaki Alhikima domin dalilin ta aka sanshi ga bunƙasar kasuwanci dama samun cigaba da alfarma da yake dashi, wanda bai samu ba saida ya fara sanya tallan sa a Fina Finai.

Ta bangare guda kuma shima ya taimaki Kannywood domin shi ya fara bada tallan maganin sa da gaske, saida ya zama yana bada tallan sa a manya fina finan Kannywood, wanda ke samar musu da kudaden shiga.

Shi ya buɗe wa Kannywood kasuwa na karɓar talluka, musamman daga masu magunguna, inda masu magunguna s**a bazo Kannywood domin suma su tallata hajar su, duba da sun lura lallai hakan yana da anfani domin sun gani a tare da Alhikima.

Wanda hakan ya samarwa da masu shirya finafinan maƙudan kuɗaɗe koma ince suke samu, wanda har wasu masu shirin ke bugar ƙirjin cewa tun a talla da ake basu suke maida kudin film, kai akwai finafinan ma da in babu talla kudin su bazai dawo har su maida riba ba.

Tabbas Kannywood ta taimaki Alhikima shima kuma ya taimake ta.

Amma mu jama'ar gari bai taimake mu ba, kuma bai duba mana ba, domin shi ya buɗe kofar Tallan Maganin Istimna'i da karfin mutane.

Da wannan muke Allah wadai da wannan cigaban mai haƙan rijiya da ya kawo ba dama ka kunna film a gaban yaro sai yace meye Istimna'i meye Karfin Mutane.

Salisu Editor ✍️

02/07/2025

Yau waazin Nalam kan Tinibu da Rarara ne😂

Ina bawa yan Kannywood hakuri kan s**ar su da nai sam bai dace ba, kuma ba haka ya kamata nayi ba, musamman masu kyakkya...
02/07/2025

Ina bawa yan Kannywood hakuri kan s**ar su da nai sam bai dace ba, kuma ba haka ya kamata nayi ba, musamman masu kyakkyawar mu'amala da Rarara.

Ina tabbatar muku cewa ba Rarara ne ya sani ba, nine nai Maganar da raɗin kaina.

~ Cewar Alhikima yayin da yake janye kalaman sa

DA ƊUMI-ƊUMI: An kwantar da Buhari a ICU a Landan - Rahoto Tsohon Shugaban Kasa Muhammadu Buhari na fama da rashin lafiy...
02/07/2025

DA ƊUMI-ƊUMI: An kwantar da Buhari a ICU a Landan - Rahoto

Tsohon Shugaban Kasa Muhammadu Buhari na fama da rashin lafiya, kuma rahotanni sun ce kwanan nan aka sallame shi daga dakin kula da masu matsananciyar rashin lafiya (ICU) a wani asibiti da ke Landan a kasar Birtaniya.

Jaridar TheCable ta rawaito daga Empowered Newswire, wani makusancin tsohon shugaban ya bayyana cewa Buhari ya kamu da rashin lafiya ne a Landan yayin da ya je don duba lafiyarsa.

Rahoton ya ce an kwantar da Buhari a dakin ICU, amma daga bisani aka sallame shi makon da ya gabata.

Ko da ya ke ba a bayyana irin cutar da ke damunsa ba, rahotanni sun nuna cewa yana samun sauki a Landan, kuma ana sa ran zai dawo Najeriya da zarar ya warke gaba ɗaya.

Empowered Newswire ta kara da cewa, bisa bayanan da s**a samu daga wasu majiyoyi masu tushe, Mamman Daura – kawun Buhari kuma amintaccensa – shima yana samun sauki daga rashin lafiya a kasar Birtaniya.

Buhari bai halarci bikin cika shekaru 50 da kafuwar Kungiyar raya Tattalin Arzikin Kasashen Yammacin Afrika (ECOWAS) da aka gudanar a Legas ranar 28 ga Mayu ba.

A wata wasika da ya aika wa Shugaba Bola Tinubu, Buhari ya bayyana cewa rashin halartar sa taron ya samo asali ne daga tafiyarsa ta duba lafiya a Birtaniya.

Daily Nigerian ✍️

TIRƘASHI: Ƴan Kannywood sun tono tsohon hoton Alhikima lokacin da ya fara tallan magani.A cewar su lokacin binsu yake ya...
01/07/2025

TIRƘASHI: Ƴan Kannywood sun tono tsohon hoton Alhikima lokacin da ya fara tallan magani.

A cewar su lokacin binsu yake yana su sanya masa talla bashi zai biya su, kamar yadda Hamza Talle Maifata ya faɗi, yace amma yanzu yayi musu butulci.

Meye ra'ayin ku?

HOTUNA: Yadda al'ummar s**a halarci sallar Jana'izar Marigayi Alhaji Aminu Dantata a birnin Madina.An binne marigayi Alh...
01/07/2025

HOTUNA: Yadda al'ummar s**a halarci sallar Jana'izar Marigayi Alhaji Aminu Dantata a birnin Madina.

An binne marigayi Alhaji Aminu Ɗantata a maƙabartar Baqi’a da ke Madina.

Ba kowa ne ya turo Alhikima yayi kalaman nan kan Kannywood ba illa Rarara, kuma su sani Kannywood tayi kusu komai~ Marta...
01/07/2025

Ba kowa ne ya turo Alhikima yayi kalaman nan kan Kannywood ba illa Rarara, kuma su sani Kannywood tayi kusu komai

~ Martanin Baana Maiduguri

Har yanzu hukumomin masallacin Madina basu tabbatar da lokacin Jana'izar Dantata baTun da fari iyalan marigayi Alhaji Am...
01/07/2025

Har yanzu hukumomin masallacin Madina basu tabbatar da lokacin Jana'izar Dantata ba

Tun da fari iyalan marigayi Alhaji Aminu Dantata sun sanar da cewa za a gudanar da jana'izar bayan la'asar a ƙasar Saudiyya, wanda yayi daidai da karfe 1:30 a agogon Najeriya.

Sai dai har kawo yanzu ba a gudanar jana'izar ba, inda ake dakon hukumomin masallacin Madina su sanya lokaci,

Ana sa ran gudanar da jana'izar zuwa bayan Magariba.

Premierradio

Kwankwaso na da yancin shigowa tafiyar mu ayi aiki tare ~ Sakataren APCJam’iyyar APC ta ce Rabiu Kwankwaso na da ‘yancin...
01/07/2025

Kwankwaso na da yancin shigowa tafiyar mu ayi aiki tare ~ Sakataren APC

Jam’iyyar APC ta ce Rabiu Kwankwaso na da ‘yancin dawowa cikin jam’iyyar tare da yin aiki da Shugaba Bola Ahmed Tinubu Daraktan yada labaran APC, Felix Morka, ya ce kofa a bude take ga kowa da kowa ciki har da tsohon gwamnan Kano An fara rade-radin dawowarsa ne bayan Abdullahi Ganduje ya sauka daga shugabancin jam’iyyar APC bisa wasu dalilai.

Jam’iyyar APC ta ce kofofinta a buɗe suke ga tsohon gwamnan Kano, Rabiu Musa Kwankwaso, idan yana da niyyar dawowa domin yin aiki da shugaba Bola Ahmed Tinubu.

Wannan na zuwa ne a daidai lokacin da ake ci gaba da hasashen cewa Kwankwaso zai iya komawa jam’iyyar, musamman bayan saukar Abdullahi Ganduje daga shugabancin APC.

Daraktan yada labaran APC, Felix Morka ne ya bayyana haka a wata hira da aka yi da shi a tashar Channels Television.

GWANIN SHAAWA: Yadda wani matashi a jihar Katsina kenan ya kera mashin mai anfani da Chaji📷 Mobile Media Crew
01/07/2025

GWANIN SHAAWA: Yadda wani matashi a jihar Katsina kenan ya kera mashin mai anfani da Chaji

📷 Mobile Media Crew

"Ku daina hada ni da Sayyada Sadiya Haruna. Ba matata bace kuma kamar yadda kowa ya sani, duk wanda ya yi hulɗa da ita a...
30/06/2025

"Ku daina hada ni da Sayyada Sadiya Haruna. Ba matata bace kuma kamar yadda kowa ya sani, duk wanda ya yi hulɗa da ita a ƙarshe sai ta fara rigima da shi a kafafen sada zumunta.

Amma ni, kamar yadda kuke gani, na san kaina kuma bana da lokacin wannan wauta."

Inji tsohon mijin Sadiya Haruna Babagana Audu Grema

Tanada kyau?
30/06/2025

Tanada kyau?

Address

Ikeja Industrial Area
100001

Telephone

+2347012613017

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Arewa Content posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share