Hausa online journalist

  • Home
  • Hausa online journalist

Hausa online journalist Journalist

Game da saukar Shaikh Ibrahim Daurawa daga mukamin Shugaban hisba a Jihar Kano wasu malamai sun tofa albarkacin bakinsu,...
03/03/2024

Game da saukar Shaikh Ibrahim Daurawa daga mukamin Shugaban hisba a Jihar Kano wasu malamai sun tofa albarkacin bakinsu, in da suke nuna rashin jin dadinsu da amincewar su ga haka.

Daga cikin waɗannan malamai akwai SHEIKH DR. ABDULLAH GADON KAYA in da yake cewa:
Bamu aminta da saukar Sheikh Daurawa daga mukamin Hukumar Hisbah ba, ya kamata gwamna ya nemi Malam ya ba shi hakuri don ya ci gaba da tsabtace Kano daga badala.

Sheikh Abdullah Usman Gadon Kaya, ya bayyana haka cikin wani bidiyo mai mintuna 18 da ya wallafa a shafinsa na Facebook da safiyar jiya Juma'a.

Dr. Gadon Kaya, ya bayyana irin tasirin da jagorancin Sheikh Daurawa ke da shi wajen yakar ayyukan sabo da badala a jihar Kano, da irin kokari da yake a shugabancin dukda rashin kudi da hukumar ke fama da shi.

Malamin ya bukaci gwamna da ya nemi Malam Daurawa ya a ba shi hakuri, ya kuma duba irin alherinsa a hukumar.

Haka zalika shima DR. SANI UMAR RIJIYAR LEMU yake cewa: Ana nema a mayar da Kano dandalin badala da fajirci, ana tasowa daga gari-gari da kasashe a zo Kano saboda badala.

Sheikh Dr. Muhammad Sani Umar R/Lemo ya bayyana haka yayin gabatar da hudubarsa ta Juma'a a masallacin Al'muntada na marigayi Sheikh Ja'afar Mahmoud Adam da ke Dorayi.

Malamin ya yi tsokaci dangane da irin kokarin da Hukumar Hisbah take na tsabtace Kano daga rashin tarbiyya, da bukatar goya wa hukumar baya kan irin aikace-aikacenta na alheri da umarni da kyakkyawa da hani da mummuna.

Jerin farashin motocin sufuri mallakar Gwamnatin jihar Gombe...Anyi ittifakin Motocin, sunfi na kowace jiha arha da kuma...
03/03/2024

Jerin farashin motocin sufuri mallakar Gwamnatin jihar Gombe.
..Anyi ittifakin Motocin, sunfi na kowace jiha arha da kuma kyau a kaf yankin Arewa.

Bauchi: N2,500
Kano: N6,000
Maiduguri: N7,000
Jos: N4,500
Yola: N3,500
Katsina: N8,500
Minna: N12,000
Makurdi: N10,000
Jalingo: N5,000
Zariya: N8,000
Sokoto: N14,000
Gusau: N11,000
Lafiya: N8,000
Jalingo: N5,000
Abuja: N10,000
Kaduna: N10,000
Dukku: N1,000
Bajoga: N1,000
Nafada: N1,600
Dadinkowa/Hinna: N500.

Suna da motoci guda 92 da ke bin hanyoyi 17 a kowace rana.

Shin nawane farashin motoci mallakar Gwamnatin jihar ku?

Comr Abba Sani Pantami

Likitoci A Riyadh Sun Sami Nasarar Raba Tagwayen Da Aka Haifa A Manne Da Juna 'Yan Asalin Najeriya.Bayan tiyatar da ta ɗ...
01/03/2024

Likitoci A Riyadh Sun Sami Nasarar Raba Tagwayen Da Aka Haifa A Manne Da Juna 'Yan Asalin Najeriya.

Bayan tiyatar da ta ɗauki tsawon sa'o'i 16 da rabi, tawagar ƙwararrun likoci da ma'aikatan jinya 38 sun samu nasarar raba tagwayen nan da suke a manne da juna 'yan asalin Najeriya, Hasna da Hasina.

Tagwayen masu kimanin shekaru biyu da rabi da likitocin Najeriya sun kasa yi musu tiyata saboda sun gano cewar idan aka raba su za a iya rasa ɗaya daga cikinsu, ko kuma a nakasa ɗaya.

Daga bisani ne kuma gidauniyar Sarki Salman na Saudi Arabia ta ɗauke su zuwa birnin Riyadh, inda aka raba su, a halin yanzu dai an yi nasara.

Haka zalika gidauniyar ta Sarki Salman ta tabbatar mana cewa a duk lokacin da aka sami irin waɗannan a shirye suke da ɗaukar nauyin raba su ba tare da iyayen su sun kashe ko sisi ba.

Domin neman ƙarin bayani, a tuntubi Malam Sabiu Danmudi 08095882212

YANZU YANZU: Wani dan kasuwa a jihar Taraba, ya rage farashin Taliya daga Naira 600 zuwa 250. Sunan dan kasuwar Alhaji I...
17/02/2024

YANZU YANZU: Wani dan kasuwa a jihar Taraba, ya rage farashin Taliya daga Naira 600 zuwa 250.

Sunan dan kasuwar Alhaji Ibrahim Iro, yana zaune a karamar hukumar Bali dake jihar Taraba, tuni talakawan garin s**a yi dafifi zuwa shagon domin samun sauki.

Muna Addu'ar Allah ya yiwa wannan dan kasuwar Albarka. Allah ya karo mana irinsu masu tausayin talakawa.

Wane Fata Zakuyi masa?

©Nigeria Reporters Hausa

10/02/2024

Buhun Masara ta fara karye wa a Wasu Kasuwannin Nijeriya “inda yanzu haka ana iya Samun ta kan ₦50,000 zuwa ₦45,000.

Labari: Gwamnonin Jahohin Najeriya wadanda ke Jam'iyya mai mulki APC sun baiwa tawagar Super Eagles kyautar Naira Miliya...
07/02/2024

Labari: Gwamnonin Jahohin Najeriya wadanda ke Jam'iyya mai mulki APC sun baiwa tawagar Super Eagles kyautar Naira Miliyan dari biyu (N200m).

Kashim Shettima, mataimakin shugaban kasar Najeriya ya taya tawagar Super Eagles murnar yin nasara kan Africa ta Kudu a ...
07/02/2024

Kashim Shettima, mataimakin shugaban kasar Najeriya ya taya tawagar Super Eagles murnar yin nasara kan Africa ta Kudu a gasar AFCON da ke gudana a yanzu.

Allhammdulillah Nigeria Takai Wasan Karshe 🙏
07/02/2024

Allhammdulillah Nigeria Takai Wasan Karshe 🙏

Shugaban kwamatin wasanni na kasa Sen. Kawu Sumaila OFR tare da ‘yan wasan Super Eagles Ahmed Musa da kuma haifaffen Jih...
07/02/2024

Shugaban kwamatin wasanni na kasa Sen. Kawu Sumaila OFR tare da ‘yan wasan Super Eagles Ahmed Musa da kuma haifaffen Jihar Kano Alhassan Yusuf suke taya juna murna daga kasar Ivory Cost bisa nasarar da Nigeria 🇳🇬 ta samu na zuwa zagayen karshe na wasan AFCON.

Yau an gudanar da zaben Inconclusive a wasu jihohi, sai gashi talakawa sun sake karban Taliya irin wanda s**a karba a za...
04/02/2024

Yau an gudanar da zaben Inconclusive a wasu jihohi, sai gashi talakawa sun sake karban Taliya irin wanda s**a karba a zaben 2023

Tsakani da Allah nayi zaton cewa talaka munyi hankali, ba zamu sake yarda a yaudaremu da Taliya ba

Ba shakka Talaka bai shirya kwatan 'yanci daga cikin mawuyacin hali da aka jefa shi ba

Don haka zafafawa da muke don 'yan uwa talaka bata lokaci ne

04/02/2024

An sako ɗalibai da malaman jihar Ekiti da aka yi garkuwa da su.

Gwamnan jihar Jigawa ya karawa ma'aikatan jihar Naira dubu 10k ga kowane ma'aikaci, domin rage musu radadin halin da ake...
04/02/2024

Gwamnan jihar Jigawa ya karawa ma'aikatan jihar Naira dubu 10k ga kowane ma'aikaci, domin rage musu radadin halin da ake ciki.

Muhammad Isma'el
SA Publication and Photography.

04/02/2024

Ecowas ta nuna damuwa kan ɗage zaɓen Senegal.

HOTO: Gwamnan jihar Kano Engr Abba Kabir A jiya lokacin da Kai ziyarar ta'aziyya Maiduguri domin jajantawa mataimakin sh...
04/02/2024

HOTO: Gwamnan jihar Kano Engr Abba Kabir A jiya lokacin da Kai ziyarar ta'aziyya Maiduguri domin jajantawa mataimakin shugaban kasa Alh. Kashim Shettima, bisa rasuwar Uwa a gare sa, Hajja Hauwa Abba Kormi.

Rasuwar Hajja Kormi a ranar Alhamis, babban rashi ne, ba ga danginta kadai ba, har ma da kasar baki daya Inji Gwamna Abba Kabir Yusuf.

📷Abba Kabir Yusuf

Ƴan kasuwar Kantin Kwari sun yi addu'a kan matsin rayuwa a Najeriya
01/02/2024

Ƴan kasuwar Kantin Kwari sun yi addu'a kan matsin rayuwa a Najeriya

Albishir ga iyaye da Dalibai masu jarrabawar karshe na ajin Sakandire.A jihar Bauchi. SSS 3/2024 Gwamnatin jihar Bauchi ...
01/02/2024

Albishir ga iyaye da Dalibai masu jarrabawar karshe na ajin Sakandire.
A jihar Bauchi. SSS 3/2024

Gwamnatin jihar Bauchi zata biya kudin jarraba ma dukkanin yara yan aji shida da zasu zana jarrabawar karshe ba tare da warewaba.

Sannan kuma wannan karon za'ayi biya Jamb kyauta ga Dalibai masu kokari. Wannnan wani karin tagomashi ne domin karfafa ilimi a jihar Bauchi.

Komitin ilimi ta jihar Bauchi Dr Jamila Muhammad Dahiru ce ta bayyana haka a safiyar yau Alhamis
01/February /2024.

PRIME MINISTER LAMINE ZEINE DA SHUGABAN KASAR TURKIYYA RECEP TAYYIB ERDOGAN SUN FARA TATTAUNAWA A YAU.🇳🇪🇹🇷
01/02/2024

PRIME MINISTER LAMINE ZEINE DA SHUGABAN KASAR TURKIYYA RECEP TAYYIB ERDOGAN SUN FARA TATTAUNAWA A YAU.🇳🇪🇹🇷

Mataimakin Shugaban Kasar Najeriya ya kaddamar da Gwamna Dikko Radda da wasu 36 a matsayin kwamitin samar da sabon mafi ...
01/02/2024

Mataimakin Shugaban Kasar Najeriya ya kaddamar da Gwamna Dikko Radda da wasu 36 a matsayin kwamitin samar da sabon mafi kankantar albashi a Najeriya

Mataimakin shugaban kasar Najeriya Kashim Shettima ya kaddamar da kwamitin mutum 37 da zai bayar da shawara kan sabon mafi kankantar albashi a kasar.

An rantsar da kwamitin ne wanda yake karkashin jagorancin tsohon shugaban ma'aikata na kasar, Bukar Aji , a fadar shugaban kasa da ke Abuja ranar Talata, 30 ga watan 2024.

A jawabin da ya gabatar a wurin mataimakin shugaban kasar ya ce, kaddamar da kwamitin abu ne da ya tabbatar da alkawarin da gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu ta yi na inganta jin dadin ma'aikata.

Kwamitin wanda ya kunshi bangaren gwamnatin tarayya da gwamnatocin jihohi da 'yan kwasuwa da kuma kungiyoyin kwadago zai bayar da sahawara ne kan abin da ya kamata a tsayar a matsayin sabon albashi mafi kankanta a kasar, inda a yanzu naira 30,000 ne.

Idan kwamitin ya mika shawararsa bangaren zartarwa zai mika ta a matsayin kudurin doka ga majalisar dokokin kasar domin samun amincewa.

Address

JAHUN

Telephone

+2349012606028

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Hausa online journalist posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Hausa online journalist:

Shortcuts

  • Address
  • Telephone
  • Alerts
  • Contact The Business
  • Claim ownership or report listing
  • Want your business to be the top-listed Media Company?

Share