23/08/2026
Ƙungiyar Izala Reahen Jos Ta Yi Kira Ga Musuĺmai Su Ƙara Shiga Siyasa, Ta Kuma Goyi Bayan Matsayar Sheikh Jingir Kan Muslim-Muslim
Ƙungiyar Jama’atu Izalatil Bid’ah Wa Iqamatis-Sunnah (JIBWIS), Hedikwatar Ƙasa da ke Jos, ta yi kira ga Musulmi da sauran ’yan Najeriya da su ƙara shiga harkokin siyasa cikin lumana da kishin ƙasa, tare da fifita adalci, amana, ƙwarewa da kishin al’umma.
Kiran ya fito ne a ƙarshen taron ƙasa kan “Ƙara Shiga Siyasa da Adalci a Matsayin Mafita ga Haɗin Kan Ƙasa da Ci Gaban Najeriya”, wanda JIBWIS ta gudanar a yau 23 ga Agusta 2026 a Saddeqa Event Centre, Jos, inda sama da mutane 350 s**a halarta daga sassan Najeriya.
A cikin sanarwar da ƙungiyar ta fitar, ta bayyana damuwarta kan matsalolin tsaro da s**a addabi ƙasar, ciki har da ta’addanci, garkuwa da mutane da ’yan bindiga, tare da kira ga gwamnati da hukumomin tsaro da su ƙara ƙarfafa tattara bayanan sirri da haɗin gwiwa wajen kare al’umma.
JIBWIS ta kuma jaddada muhimmancin adalci, daidaito, ’yancin addini da faɗin albarkacin baki, tare da yin kira ga ’yan Najeriya su guji ƙiyayyar kabilanci da addini. Ta kuma yi kira ga gwamnati da ta tabbatar da rabon damarmaki da ayyukan ci gaba cikin adalci ba tare da nuna bambanci ba.
A wani muhimmin ɓangare na sanarwar, JIBWIS ta bayyana cewa mambobinta daga jihohi daban-daban na Najeriya suna goyon bayan duk matakin da Shugaban Majalisar Ulama’u ta JIBWIS, Sheikh Muhammad Sani Yahaya Jingir, zai ɗauka dangane da zaɓen ƙasa na 2027, musamman batun taken “Muslim-Muslim”.
Ƙungiyar ta kuma yaba da wasu shirye-shiryen Gwamnatin Tarayya na bunƙasa ababen more rayuwa, ilimi, lafiya, noma da samar da ayyukan yi, amma ta bukaci a aiwatar da su cikin gaskiya da adalci a dukkan sassan ƙasar.
A ƙarshe, JIBWIS ta yi ta’aziyya ga iyalan waɗanda s**a rasa rayukansu sakamakon hare-haren ’yan bindiga da garkuwa da mutane, tare da yin addu’ar Allah Ya kawo zaman lafiya mai ɗorewa a Najeriya.
Daga Lawan Sadik