13/07/2021
Ni ke shugabancin jihata, Zulum ya karyata rade-radin kafa gwamnan Boko Haram a Borno Talata, Yuli 13, 2021 at 5:32 Safiya by Aisha Khalid Farfesa Zulum na jihar Borno ya jaddada cewa shi ke jagorancin jihar Borno Gwamnan ya musanta rade-radin dake yawo na cewa Boko Haram ta nada sabon gwamna A kafafen sada zumunta ake bayyana wani Abba Kaka a matsayin gwamnan da miyagun s**a nada Gwamna Babagana Zulum na jihar Borno ya musanta rahoton dake yawo na nada gwamna a wasu yankunan jihar Borno da Boko Haram tare da ISWAP s**a yi. A makon da ya gabata, bidiyon da ake zargin na nada gwamnan Boko Haram a Borno ne ya dinga yawo a kafafen sada zumuntar zamani, Daily Trust ta ruwaito. Hukumar rikon kwarya ta 'yan ta'addan ta samu shugabancin wani Abba Kaka, wanda aka nada a matsayin shugaban wasu yankunan Borno. KU KARANTA: Bayan Kammala Mukabala, za a Gurfanar da Abduljabbar Kabara Gaban Kotu Ni ke shugabancin jihata, Zulum ya karyata rade-radin kafa gwamnan Boko Haram a Borno. Hoto daga dailytrust.com Source: UGC KU KARANTA: APC ta rushe kwamitin rikon kwaryan jam'iyyarta na jihar Zamfara READ ALSO Gwamnan Gombe ya bayyana matakansa da ya dauka na kare dalibai daga sata a makarantu Amma yayin jawabi ga manema labaran gidan gwamnati bayan taron sirri da shugaban kasa Muhammadu Buhari a ranar Litinin, gwamnan ya karyata wannan labarin, Daily Trust ta wallafa. Ya jaddada cewa "shi ke jagorantar jiharsa." Zulum yace mulkinsa baya bincikar al'amarin "Har yanzu bamu fara bincikar sahihancin rahoton nada gwamnan Borno da 'yan ta'adda s**a yi ba. A matsayina na gwamnan jihar, a tunani na bai dace in yi magana kan abinda bani da iliminsa ba cikakke." Rahoton bashi da sahihanci, a kafar sada zumunta yake A yayin da aka tambaya gwamnan ko zai yi bincike, Gwamna Zulum yace a'a, ya dora laifin rahoton ga kafafen sada zumunta. Ya kara da cewa: "Ba zan yi bincike ba saboda rahoton bashi da sahihanci. Rubutu ne kawai kuka gani a Facebook. Ku 'yan jarida ne, ina tunanin sai mun san ingancin