Dan Modi TV

Dan Modi TV an kirkirane saboda tallata dantakarar gwamna wato namadi Danmodi

30/08/2023

"Gwamnan Jihar Jigawa Mallam Umar A. Namadi FCA ya bada umarnin raba buhunan shinkafa dubu arba'in da biyu (42,000), Gero da Masara buhuna dubu talatin da biyu (32,000), da taliya kwali dubu daya (1,000) ga mabukata a fadin jihar Jigawa"

-Mallam Garba Al-Hadejawy FCAI, FIMC
(Mataimaki na musamman ga mai girma gwamnan Jihar Jigawa a sabbin kafafen sadarwa.)

30/08/2023

"Gwamnan Jihar Jigawa Mallam Umar A. Namadi ya amince da biyan kudin makaranta ga dalibai 'yan asalin jihar Jigawa wadda su ke karatu a jami'ar tarayya ta Dutse (FUD), Jami'ar Bayero da ke Kano (BUK), Jami'ar Kimiyya da fasaha ta Jihar Kano (KUST) da Kuma jami'ar Maiduguri (UNIMAID) a kan kudi Naira Milyan dari da sittin da bakwai, da dubu ashirin da hudu da dari tara da Hamsin (N167,024,950.00). Hakan ya yi biyo bayan rage wa dalibai da iyayensu nauyin biyan kudin karatu duba da yanayin da ake ciki."

-Mallam Garba Al-Hadejawy, FCAI, FIMC
Special Assistant to Jigawa State Governor on New Media.

26/08/2023

Inason jigawa

26/08/2023

Jigawa abar alfaharinmu

 Gov. Mallam Umar Namadi FCA and other Governors at Executive Leadership Retreat under UNDP and Nigeria Governor's Forum...
25/08/2023



Gov. Mallam Umar Namadi FCA and other Governors at Executive Leadership Retreat under UNDP and Nigeria Governor's Forum in Kigali, Ruwanda.

Allah ya ba da saa, ya kuma dawo mana da ku lafiya 🙏🙏🙏


09/08/2023

SAKAMAKON ZAMAN MAJALISSAR ZARTARWA TA JIHAR JIGAWA A YAU LARABA 9 GA WATAN AGUSTA SHEKARAR, 2023.

1. Majalissar zartarwar ta amince da raba tirela biyar ta shinkafa ga kananan hukumomi 27 na jihar Jigawa ta hannun hukumar bayar da agajin gaggawa ta jiha wato SEMA a matsayin shirin somin tabi na shirin rage radadin halin da ake ciki wadda gwamnatin tarayya ta aiko, kamar yadda aka bayar a jihohi 36 da ke fadin tarayyar Najeriya.

1. Majalissar ta amince wa da sake sayo wa karin wasu tirelolin shinkafa guda biyar domin Kara wa a kan wadda gwabnatin tarayya ta bayar a kan kudi Naira milyan dari da talatin da hudu da dari shida da sittin da biyar (N134, 665,000)

3. Sannan a yayin zaman, majalissar ta amince da bayar da jarin N50,000 (empowerment) ga matasan 'yan kasuwa 1,500 a fadin jihar Jigawa a karkashin ma'aiktar yada labarai, matasa da wasanni tare da hadin gwiwar hukumar samar da ayyukan yi da dogaro da kai ta jiha (Directorate of Economic Empowerment).

4.Majalissar ta sake amincewa da bayar da tallafin N100,000 ga kanana da matsakaitan 'yan kasuwa (SMEs) guda 1,000 a fadin jiha wadanda su ke da rejista ta kamfani, lambar aususun banki, sannan s**a cika ka'ida, a karkashin shirin bayar da tallafi na bankin duniya ( J-Cares programme)

Hon. Sagir Musa Ahmad
Kwamashinan yada labarai na Jiha.

BIKIN KADDAMAR DA SAYAR DA TAKIN ZAMANI!Mai girma gwabnan Jihar Jigawa Mallam Umar A. Namadi FCA ya halarci bikin kaddam...
17/07/2023

BIKIN KADDAMAR DA SAYAR DA TAKIN ZAMANI!

Mai girma gwabnan Jihar Jigawa Mallam Umar A. Namadi FCA ya halarci bikin kaddamar da sayar da takin zamani na jihar jigawa wadda aka gababar a harabar hukumar sayar da kayan aikin gona ta jiha.

Tun a wancan satin ne idan ba a manta ba, mai girma gwabnan ya kaddamar da kwamatin rabon takin, wadda shugaban ma'aikata na gudan gwabnatin jihar jigawa shi ne shugaban kwamatin da ke da alhakin sayar da takin zamani Kai tsaye ga manoma a farashi mai ruhusa.

Takin zamanin wadda ake sayar da shi a kan farashin N26,000 a doron Kasuwa; gwabnatin jiha ta saukaka wa manoman wajen sayar da shi a kan N16,000.

Sannan gwabnan ya gargadi jami'an hukumar ta JASCO da kungiyoyin manoma, wajen karkatar da takin ta hanyar da ba ta dace ba ..su tabbatar takin yanke hannun manoma Kai tsaye. Sannan kada a sayar wa da mutum taki sama da buhu biyar. Sannan ya hori jami'an tsaro da su tabbatar da sun sa ido wajen tabbatar da an yi abin da ya kamata wajen sayar da takin.

Taron ya samu halartar mataimakin gwabna, kakakin majalissa, manyan jami'an gwabnati, sakataren gwabnatin jiha, shugaban ma'aikata na gidan gwabnat, 'yan majalissar jiha, shugabannin kananan hukumomi, kungiyoyin manoma, jami'an tsaro da sauran al'umma.

Mallam Garba Al-Hadejawy, FCAI, FIMC
S.A New Media, Jigawa State.

ZA A YI GAGARUMIN DASHEN BISHIYA A JIHAR JIGAWA.Hukumar National Agency for Great Green Wall (NAGGW) ta tabbatar wa da m...
13/07/2023

ZA A YI GAGARUMIN DASHEN BISHIYA A JIHAR JIGAWA.

Hukumar National Agency for Great Green Wall (NAGGW) ta tabbatar wa da mai girma gwabnan Jihar Jigawa Mallam Umar A. Namadi FCA cewar za su gabatar da dashen bishiya domin magance matsalar kwaranyowar hamada da jihar ke fuskanta.

A satin da ya gabata ne mai girma gwabnan Jihar Jigawan ya Kai ziyarar aiki ga wannan gagarumar ma'aikata wadda aka kirkira domin raya dazuka, yakar hamada, samar da ingantaccen guraben kiwo ga makiyaya, Samar da fasahar noma ta zamani, inganta fasahar noman rani ta yadda za su samar da rijiyoyi na bayin ruwa da sauransu.

Shugaban hukumar , Dr. Maina Bukar ya bayyana farin cikinsa bisa wannan ziyara, sannan ya yabawa gwabnan Jigawan bisa saka inganta dazuka a cikin kudurin gwabnatinsa. sannan ya kara da tabbacin da farfado da gandun daji a guraben da ake fuskantar kwaranyowar hamada a jihar jigawa.

GIDAUNIYAR 'QATAR FOUNDATION' ZA TA GINA KATAFARIYAR MAKARANTA TA ZAMANI (MEGA SCHOOL) A JIHAR JIGAWA.Mai girma gwabnan ...
07/07/2023

GIDAUNIYAR 'QATAR FOUNDATION' ZA TA GINA KATAFARIYAR MAKARANTA TA ZAMANI (MEGA SCHOOL) A JIHAR JIGAWA.

Mai girma gwabnan Jihar Jigawa Mallam Umar A. Namadi FCA, ya Kai ziyara ofishin Gidauniyar Qatar Foundation, wadda ta ke da ofishi a Abuja.

Ita wannan Gidauniya wadda ta ke mallakin kasar larabawa ta Qatar ce, ta na gudanarwar da ayyukan cigaba a kasashen duniya, wadda s**a shafi fannin Ilimi, lafiya, addini da sauransu.

Gwabnan Jihar Jigawan ya Kai wannan ziyara ne domin sada zumunci da Kuma gode wa wannan gudauniya a kan irin ayyukan taimako da ta ke yi. Sannan ya bukaci Gidauniyar da ta fadada ayyukanta har zuwa Jihar Jigawa.

Nan take shugaban Gidauniyar reshen Najeriya a yayin mayar da jawabi ya nuna jin dadin ziyarar da gwabnan ya kai masa, sannan ya yi alkawarin fadada ayyukansu, da Kuma samar da katafariyar makaranta (Mega school) tare da katon masallaci a hade.

A lokacin ziyarar, Mai girma gwabnan ya samu rakiyar shugaban hukumar Samar sa ayyukan yi ta jihar Jigawa; Dr. Habeeb Ubale, Chief Press Secretary Mallam Hamisu Gumel da sauransu.

Mallam Garba Al-Hadejawy FCAI, FIMC
Mataimaki na musamman ga gwabnan Jihar Jigawa a fannin sabbin kafafen sadarwa.

Another appointment
05/07/2023

Another appointment

04/07/2023

Address


Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Dan Modi TV posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Dan Modi TV:

Shortcuts

  • Address
  • Telephone
  • Alerts
  • Contact The Business
  • Claim ownership or report listing
  • Want your business to be the top-listed Media Company?

Share