Mahanga TV

Mahanga TV Like my page for more updates

Za muna kawo maku:
●Sharshi akan Siyasar Najeriya.
● Sharshi akan Siyasar Duniya da Gabas ta Tsakiya
● Sharshin Labarai da al'amuran yau da kullum.
● Labaran Al'ajabi.
● Waiwaye akan Tarihin Shahararrun Mutane da su ka yi shuhura a duniya.

Birtaniya ta amince da kafa ƙasar Falasɗinu shekaru 108 bayan sanarwar BalfourWannan mataki da aka sanar tare da ƙasashe...
21/09/2025

Birtaniya ta amince da kafa ƙasar Falasɗinu shekaru 108 bayan sanarwar Balfour

Wannan mataki da aka sanar tare da ƙasashen Kanada da Ostiraliya ya zo ne a daidai lokacin da Isra’ila ke ci gaba da kai hare-haren hallaka a Gaza.

Jami’ar European-American ta nesanta kanta da digirin girmamawa da aka bai wa mawaki RararaJami’ar da ake kira European-...
21/09/2025

Jami’ar European-American ta nesanta kanta da digirin girmamawa da aka bai wa mawaki Rarara

Jami’ar da ake kira European-American University ta ce ba ta da hannu a bikin da aka gudanar a Abuja inda aka ce ta bai wa mawakin siyasar nan, Dauda Kahutu Rarara, digirin girmamawa.

A ranar Asabar aka shirya bikin a otal ɗin NICON Luxury Hotel da ke Abuja, inda danginsa da abokansa s**a halarta domin taya shi murna.

Sai dai jami’ar ta wallafa sanarwa a shafinta na intanet, tana mai bayyana cewa taron yaudara ne da ba ta amince da shi ba.

Ta ce akwai wani mutum da aka bayyana da sunan Musari Audu Isyaku a matsayin wakilin jami’ar a Arewacin Najeriya, jami'ar ta ce ba shi da wani izini daga wurinta.

Haka kuma ta ƙara da cewa Idris Aliyu, wanda aka gabatar a matsayin mamba a majalisar gudanarwar jami’ar, hallau ba shi da wannan matsayin. Jami’ar ta bayyana cewa ba ta da wata “majalisar gudanarwa,” tare da sanar da cewa ta janye duk wani matsayi da ta taɓa ba shi saboda rawar da ya taka a shirya wanna biki.

Tun da farko dai jami’ar ta raba irin wannan digirin girmamawa ga wasu fitattun ’yan Najeriya, ciki har da tsohon gwamnan Jihar Kogi, Yahaya Bello, da kuma Kwamishinan Ayyuka da Gidaje na Jihar Borno, Mustapha Gubio.

Me za ku ce?

📰 Mahanga TV - Sabbin Labaran Duniya📍 Isra’ila & Siriya na kan Teburin SulhuIsra’ila da Siriya sun shiga muhimman tattau...
18/09/2025

📰 Mahanga TV - Sabbin Labaran Duniya

📍 Isra’ila & Siriya na kan Teburin Sulhu
Isra’ila da Siriya sun shiga muhimman tattaunawa kan sabon tsarin tsaro domin kauce wa wani sabon yaƙin. Tsarin ya kasu gida uku, yana hana makaman yaƙi kusantar iyakar Isra’ila, amma Isra’ila ta dage da riƙe Dutse Hermon. Amurka na matsa lamba don kammala tattaunawar kafin taron MDD. Sai dai har yanzu babu wanda ya ambaci batun Tuddan Golan.

📍 Mummunan Hari a Gaza
Isra’ila ta ƙaddamar da hare-hare mafi muni a Gaza cikin sa’o’i 48, ta kai farmaki a wurare fiye da 150. Dubban mutane sun rasa matsugunansu, asibitoci suna maƙare da marasa lafiya, kuma MDD ta tabbatar da kisan kare dangi. Duk da Allah wadai daga ƙasashen duniya, Isra’ila ta ci gaba da samun goyon bayan Amurka. China, Qatar da Paparoma sun yi kira da a kawo ƙarshen yaƙin.

👉 Ku biyo mu don jin cikakkun bayanai, nazari da labaran duniya cikin salo na musamman a Mahanga TV. Ku Duba Comment Section don za mu saka muku link ɗin bidiyon.

🔴 Gaza: Kalmar da ta fi bama-bamai nauyi – Kisan ƙare dangiYaƙin Gaza ya sake shiga wani sabon babi inda Majalisar Ɗinki...
17/09/2025

🔴 Gaza: Kalmar da ta fi bama-bamai nauyi – Kisan ƙare dangi

Yaƙin Gaza ya sake shiga wani sabon babi inda Majalisar Ɗinkin Duniya ta fitar da rahoto mai shafi 72 tana mai tuhumar Isra’ila da aikata kisan ƙare dangi (genocide). Sunayen manyan shugabannin ƙasar kamar su: Netanyahu, Isaac Herzog, da kuma tsohon Ministan Tsaro – sun shiga cikin jerin waɗanda aka ɗorawa alhakin laifin aikata wannan ta'addaci. Amma Isra’ila ta musanta wannan zargi, tana mai ƙiran rahoton na MDD da “ƙarya da farfaganda.”

🌍 Ƙarin matsin lamba daga ƙasashen duniya

Kasashen duniya suna ƙara matsa lamba kan Isra’ila. Afrika ta Kudu ta maka Isra’ila a kotu duniya ta ICJ. Faransa da Saudiya kuma sun shirya taron a New York don kawo ƙudirin mafitar kafa “ƙasashe biyu masu cin gashin kansu” a wannan watan na Satumba. Ƙasashe da dama suna amincewa da kafa ƙasar Palasɗinu a hukumance.

⚔️ Zapad 2025: Rasha, Belarus da rikicin iyaka

A gefe guda kuma, Rasha da Belarus sun gudanar da atisayen soji na Zapad 2025. Amma rikice-rikicen NATO sun ƙara ɗaukar zafi bayan jiragen Rasha sun ketare sararin samaniyar Poland da Romania. Poland ta mayar da martani da rufe iyakarta da Belarus – abin da ya katse jigilar kasuwanci tsakanin Chaina da Turai mai darajar biliyoyin daloli.

👉 Ku kalli cikakken rahoton a Mahanga TV don fahimtar labarin duniya ta wata Mahanga me ma'ana. Link a comment section.

23/08/2025

🇮🇷 Iran ta yi gwajin makamin sojinta
Abokan gabar Iran sun tsorata bayan ta gudanar da atisayen sojinta.

⚔️ Atisayen soja
Iran ta fito da atisayen soji a Tekun Indiya – makamai masu linzami, jiragen ruwa, jiragen nutsewa, drones da cibiyoyin yaƙin lantarki duk sun shiga cikin shirin. Manufarta ita ce ta nuna cewa tana shirye ko da yaushe.

🇺🇸 Barazanar Donald Trump
Shugaban Amurka Donald Trump ya yi gargadin cewa zai sake kai hari idan Iran ta sake buɗe shirin nukiliyarta. Wannan shi ne babban abin da ya sa Tehran ke jan kafa kan tattaunawa.

🇪🇺 Matsin lamba daga Turai
Faransa, Birtaniya da Jamus sun yi barazanar dawo da takunkumin MDD. Saboda haka Iran ta amince ta shiga tattaunawa da Turai, amma ba tare da Amurka ba.

👉 Tambayar ita ce: Shin nuna ƙarfin Iran zai isa idan rikici ya sake tashi?

📺 Ku kalli cikakken labarin a wannan bidiyo, sannan ku bamu ra’ayinku a sashen sharhi 👇

20/08/2025

📰 Babban Labarin Yau a Mahanga TV

📍 Shugabannin Turai a Fadar White House
Shugabannin ƙasashe takwas na Turai sun yi taro da Donald Trump a Washington kan rikicin Ukraine. Sun tattauna kan yiwuwar ganawar Putin da Zelensky, batun tabbacin tsaro ga Ukraine, da kuma yarjejeniyar tsagaita wuta. Trump na neman zaman lafiya kai tsaye, Turai kuma na son a fara da tsagaita wuta tukuna.

⚓ Koriya ta Arewa da sabon jirgin yaƙi
Kim Jong-un ya ƙaddamar da sabon jirgin ruwan yaƙi mai ɗaukar makaman nukiliya – Choe Hyon. Ya soki atisayen Amurka da Koriya ta Kudu, ya kuma yi alƙawarin ƙara yawan makaman nukiliyarsa cikin gaggawa, lamarin da ke ƙara tayar da hankali a tsibirin Koriya.

👉 Ku kalli cikakken bayani cikin salo na musamman a Mahanga TV – inda muke kawo muku labaran duniya cikin hikima da zurfin fahimta.

🔔 Kada ku manta kuyi Subscribe sannan ku danna kararrawa domin samun sabbin rahotanni kai tsaye!

19/08/2025

📰 Mahanga TV | Labaran Duniya a Yau

👉 YARJEJENIYAR TSAGAITA WUTA A GAZA:
Yaƙin Gaza ya shiga rana ta 682, inda aka rasa rayukan Falasɗinawa fiye da 62,000. Yanzu an kawo sabon shirin tsagaita wuta na kwanaki 60, Hamas ta amince, amma Isra’ila ta yi shiru. Masar, Qatar da sauran ƙasashe na matsa lamba domin a kulla yarjejeniya. Tambayar ita ce: Shin Isra’ila za ta bi hanyar diflomasiyya, ko kuma za ta ci gaba da yin ruwan bama-bamai a Gaza?

👉 Trump da Putin a Alaska;
Donald Trump da Vladimir Putin sun gana a Alaska kan rikicin Ukraine. Bayan tattaunawar, rahotanni sun nuna cewa Putin ya fi samun nasara. Duk da barazanar Trump, shugaban Rasha ya tsaya kan matsayarsa ba tare da sassauci ba. Shin wannan na nufin Trump ya sha kaye a fagen diplomasiyya?

📌 Ku biyo mu don cikakken bayani da zurfin nazari akan waɗannan manyan batutuwa na duniya.

Jigawa State
17/08/2025

Jigawa State

Baya ga garin Kano ina ne kuma aka waye da marka-marka a yau Lahadi?

13/08/2025

🔥 Najeriya ta fara Amfana da Rikicin Mai na India–Amurka–Rasha!

🇳🇬 Najeriya ta ga dama ta cike gibin da ya samu bayan Amurka ta matsa wa India lamba da ta rage shigo da mai daga Rasha.

⛽ India ta taba barin Najeriya ta koma siye daga Rasha saboda rahusa, amma yanzu teburin ya juya!

📈 Najeriya na shirin aika wa da gangunan mai fiye da miliyan 2 a kowane wata zuwa India — ba tare da haɗarin takunkumi ba.

📌 A wannan bidiyon za ku ji yadda:

Amurka ke matsa wa India ta daina siyo ɗanyen mai daga Rasha

Najeriya ta dawo da kasuwancin da ta rasa a baya.

💡

Isra’ilawa masu 'yanuwa da ke tsare a Gaza suna yin ƙira da a gudanar da yajin aiki a fadin ƙasar a ranar Lahadi mai zuw...
10/08/2025

Isra’ilawa masu 'yanuwa da ke tsare a Gaza suna yin ƙira da a gudanar da yajin aiki a fadin ƙasar a ranar Lahadi mai zuwa, a matsayin nuna adawa da sabon matakin da majalisar tsaron Isra’ila ta ɗauka na faɗaɗa yaƙi a Gaza kuma mamaye birnin kacokam.

Me za ku ce?.

Shugaban ƙasar Ukraine, Volodymyr Zelenskyy, ya nuna shakku game da taron zaman lafiya da ake shirin gudanarwa tsakanin ...
10/08/2025

Shugaban ƙasar Ukraine, Volodymyr Zelenskyy, ya nuna shakku game da taron zaman lafiya da ake shirin gudanarwa tsakanin shugaban Amurka, Donald Trump, da shugaban Rasha, Vladimir Putin, yana mai gargaɗin cewa duk wata yarjejeniyar zaman lafiya da Ukraine b, to ba za a cimma nasara ba.

Me za ku ce?

06/04/2025

Isra'ila ta tsananta yaƙi a Gaza

Address

Jahun
Jigawa

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Mahanga TV posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Mahanga TV:

Share