Jigawa Online Media

Jigawa Online Media MEDIA/NEWS company

Sanarwa!Hanyar da ta tashi daga Gwaram zuwa Basirka ta tafi har Darazau dai dai babbar gadar da take garin Bagadaza tana...
04/09/2025

Sanarwa!

Hanyar da ta tashi daga Gwaram zuwa Basirka ta tafi har Darazau dai dai babbar gadar da take garin Bagadaza tana gab da ruftawa sakamakon mamakon ruwan sama.

Jami'an tsaro suna kan hanyar don nusar da matafiya inda ya kamata su bi tare da kuma kare rayukan su har ma da dukiyoyinsu.

Matafiya a kiyaye a tsaya idan jami'an tsaro sun tsaida ku domin nusar daku halin da ake ciki, kuma ayi tuki cikin nutsuwa.

PRD Dutse.

02/09/2025

GWANIN SHA'AWA: Shugaban Mulkin Sojin NijarJanar Abdoulramane Tchiani ya tallafa wa jarumin Kannywood Malam Na Tala'ala wanda ke kwance a gadon asibiti.

Jarumin wanda ya tabbatar da hakan a wani bidiyo da ya fitar, ya ce Shugaban Ƙasar ya ƙirashi a waya kuma ya tura masa da kuɗaden da ya ce adadinsu ba zai faɗu ba.

Yace ya tura masa ne saboda kauna domin kuma ya cigaba da shan magani.

Daga Salisu Editor

Kacici-Kacici: Iya Ƴan Shekara 20 zuwa Kasa Ko Kun Mene wannan? In Kun Sani Me Ake Dashi?Ku Rubuta Mana Amsar A Comment ...
02/09/2025

Kacici-Kacici: Iya Ƴan Shekara 20 zuwa Kasa Ko Kun Mene wannan? In Kun Sani Me Ake Dashi?

Ku Rubuta Mana Amsar A Comment Dan Allah.👇

YANZU-YANZU: Ƴan daba s**a far wa mutane da makamai a Kafin Hausa, a wajen taron karramma Zakari Kafin Hausa a Karamar H...
31/08/2025

YANZU-YANZU: Ƴan daba s**a far wa mutane da makamai a Kafin Hausa, a wajen taron karramma Zakari Kafin Hausa a Karamar Hukumar Kafin Hausa Dake Jigawa A Nigeria.

31/08/2025

Ko me yasa Gwamnatin Najeriya tace za ta cire aljihu a kayan 'yan sanda?

YANZU-YANZU: Lauya Ya Maka Gwamnan Gombe da CP a Kotu Bisa Zargin Tauye Haƙƙin Jama’aBarrister Nuhu Dantani, lauya mai r...
31/08/2025

YANZU-YANZU: Lauya Ya Maka Gwamnan Gombe da CP a Kotu Bisa Zargin Tauye Haƙƙin Jama’a

Barrister Nuhu Dantani, lauya mai rajin kare haƙƙin bil’adama, ya shigar da ƙara a Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja, yana zargin Gwamnan Jihar Gombe da Kwamishinan ’Yan Sanda na jihar da tauye ’yancin zirga-zirgar jama’a da cin zarafi.

A cewarsa, matakin na gwamnatin jihar na hana motsi da sanya matsin lamba kan mutane ya saba da kundin tsarin mulki. Ya ce:
"Duk wanda yake take haƙƙin dan Adam, ba za mu bar shi ba har sai inda ƙarfinmu ya kare!"

Barrister Dantani ya bayyana Gwamnan a matsayin mai taurin kai, yana mai jaddada cewa lokaci ya yi da za a kare ’yancin jama’a ta hanyar shari’a. Ana sa ran kotun za ta fara sauraren ƙarar nan bada jimawa ba.

DA DUMI-DUMI: Kowane gida a jihar Sokoto, zasu biya Gwamnatin jihar Sokoto Naira dubu 220k kudin sabunta takaddar mallak...
27/08/2025

DA DUMI-DUMI: Kowane gida a jihar Sokoto, zasu biya Gwamnatin jihar Sokoto Naira dubu 220k kudin sabunta takaddar mallakar fili da gonaki, wuraren kasuwanci kuma Naira dubu 400k zasu biya, ga account number cikin takadda don kowane Basakwace ya tura nashi.

YA ZAMA WAJIBI AL'UMMAR JAHAR JIGAWA SU JIN-JINAWA GWAMNONIN SU TIN DAGA SAMUN YANCIN KAI ZUWA YAU DA JAHAR TAKE CIKA SH...
27/08/2025

YA ZAMA WAJIBI AL'UMMAR JAHAR JIGAWA SU JIN-JINAWA GWAMNONIN SU TIN DAGA SAMUN YANCIN KAI ZUWA YAU DA JAHAR TAKE CIKA SHEKARA 34.

Daga: Hassan Yunusa Takur.
..Jihar Jigawa Jiha Ce Dake Arewa Maso Yammacin ƙasar Nan, Wadda Akema Laƙabi Da Sabuwar Duniya "New World". An kirkiretane A Ranar 27 Ga Watan AUGUST, A Shekarar 1991. A Zamanin Mulkin Shugaban Najeriya Janaral Ibrahim Badamasi Babangida.

Jigawa Jahace da Allah Ya Albarkace Ta Da Fadin Kasa, Sannan Tana Da Yawan Mutane Daya Haura Mutum Miliyan Takwas Da Dubu Dari Uku Da Goma, K**ar Dai Yadda Rahoton Masu Kididdiga S**a Kididdige a Wannan Sheka.

Dutse Shine Babban Birnin Jahar Wanda Ake Yiwa Take Da Sabuwar Duniya, Gari Ne Mai Tsohon Tarihi Wanda Aka Fara Lissafa Shekarun Kafuwar Jahar daga ƙarni Na Goma Sha Uku (13).

Kuma An Kawatashi Da Gine-Gine Na Zamani Da Tituna A Lungu Da Sako, Dai-Dai Gwar-Gwado. Kuma Aikin Ya Farune Ta Dalilin Gwamnonin Da Jahar Jigawa Tayi Tin Mulkin Farko Bayan Da Jahar Ta Samu Yanci Kai Daga Jahar Kano Zuwa Yau.

Jigawa Jahace Da Take Da Masarautun Gargajiya Guda Biyar Da S**a Haɗa Da:👇
👉Masarautar Dutse.
👉Masarautar Gumel.
👉Masarautar Haɗejia.
👉Masarautar Kazaure.
👉Masarautar Ringim.

Jigawa tana da ƙananan hukumomin mulki 27, Inda Aka Kasa Jahar Gida Uku Wanda 'Yan-Majalisun Dattawa Zasu Wakilta kamar Kowace Jaha A Najeriya👇
👉Jigawa ta tsakiya
👉jigawa ta kudu
👉jigawa ta arewa.

SUWAYE WANNAN ZAKAKURAN GWAMNONI DA S**A JAGORANCI JAHAR?👇👇

1. Manjo Janar Olayinka Sule.

Gwamna Manjo Janar Olayinka Sule Shine Gwamna Na Farko A Jahar, Ya Zama Gwamna A Ranar 27 Ga Watan Agusta Na Shekara Ta 1991, Inda Kuma Ya Isa Babban Birnin Jahar Dutse, A Ranar 30 Ga Watan Agusta Na Shekar 1991.

Shine Ya Fara Aza Harsashin Gina Wannan Jahar, Babban Abin Da Ya Fara Aiwatarwa A Jahar Shine Samar Da Matsugunnai Da Ofisoshin Ma’aikata A Babban Birnin Jahar Dutse.

Ya Kuma Kaddamar Da Gidan Ruwa A Garin Shuwarin, Inda Ya Debi Sababbin Ma’aikatanta Domin Samar Da Ruwa Wadatacce A Fadin jahar, Don Tabbatar Da Walwala Da Jin Daɗin Jama’ar Wannan Birni Na Dutse.

Sannan Ya Sake Tabbatar Da Masarautun Dutse Da Ringim, ƙari A Kan Haɗeja, Gumel, Da Kuma Kazaure, Da Aka Gada Daga Tsohuwar Jahar Kano.

2. Barista Ali Sa’adu Birnin Kudu.

Barista Ali Sa’adu Birnin Kudu, Shine Gwamna Na Biyu Kuma Shine Gwamna Na farko a Mulkin Farar Hula, Ya Karbi Mulki A Hannun Manjo Janar Olayinka Sule A Shekara Ta 1991 A Watan Disamba A Inuwar jam’iyyar SDP(Social Democratic Party).

Ya kuma K**a Aiki A Watan Janairu Na Shekarar Ta 1992. Lalle Shima Ya Bada Gudunmawar Gina Jahar.

3. Birgediya Janaral Ibrahim Aliyu Mai Ritaya.

Birgediya Janaral Ibrahim Aliyu Mai Ritaya Shine Gwamna Na Uku kuma Na Biyu A Mulkin Soji, Ya Zama Gwamna A Shekarar 1993 Bayan Rugujewar Gwamnatin Riƙon ƙwarya ta Shugaba Ernets Shonekan, Yayi Gwamnatinsa ƙarƙashin Shugaba Muhammad Sani Abacha.

4. Kanal Rasheed Alade Shekoni.

Kanal Rasheed Alade Shekoni, Shine Gwamnan Jahar Jigawa na Huɗu, Wanda Ya Zama Na Uku A Mulkin Soji, Kuma Ya Zama Gwamnan Jahar A watan Agusta Na Shekara Ta 1996.

5. Kanal Abubakar Zakariyya Maimalari.

Kanal Abubakar Zakariyya Maimalari, Shine Gwamna Na Biyar A Jahar A Watan Agusta na Shekarar 1998. Kuma Na Hudu A Mulkin Soji Wanda Akewa Lakabi Da (Soja Dan Soja).

6. Alh. Ibrahim Saminu Turaki.

Alhaji Ibrahim Saminu Turaki Ya Zama Gwamna Na Shida Bayan Da Ya Karbi Mulki A Hannun Kanal Abubakar Zakariyya Maimalari Bayan An Gudanar Da Zabe A 1999.

Shine Gwamna Na Biyu A Mulkin Farar Hula,An Zaɓe Shi A Matsayin Gwamnan Jahar A Ranar 29 Ga Watan Mayu Na Shekarar 1999 A Karƙashin Inuwar Jama'iyyar ANPP (All Nigerian People's Party).

Yayi Kokari Matuka Wajen Cigaban Jahar Inda Ya Kirkiri Makarantar Koyon Kimiyyar Kwamfuta "Informatics Institute" Dake Kazaure Wadda Makarantar Itace Ta Farko A Najeriya.

Ya Kuma Samar Da Cibiyar Bayar Da Sabis Din Intanet Dake Garin Dutse mai suna "Galaxy ITT".

7. Dr. Sule Lamiɗo.

Dr. Sule Lamido Ya Zama Gwamna Na Bakwai Bayan Anyi Zabe A Shekarar 2007 A Ranar 29 Ga Watan Mayu, Yaci Zabe Karƙashin Inuwar Jama’iyyar PDP (Peoples Democratic Party).

Shi Ne Gwamnan Jahar Jigawa Na Shida, Sannan Gwamnan Farar Hula Na Uku. Alhaji Sule Lamiɗo, Gogaggen Dan Siyasa Ne, Wanda Ya Fara Siyasa Tun PRP Ta Marigayi Malam Aminu Kano Kuma Yazama Ya Koyi Siyasa A Hannun Sa.

Yayi Kokari Wajen Gina Jahar, Wanda Ya Gina Katafariyar Sakatariyar Jaha (State Secretariat) Dake Dutse, Ya Kuma Gina Gidan Rediyo Da Talabijin "Jigawa Television" (J.T.V).

Shine Ya Samar Da Manyan Makarantu Irin "Sule Lamido University, Dake Garin Kafin Hausa. Sannan Ya Samar Da Kwalejin Koyon Aikin Jinya Da Ungozoma Dake Birnin Kudu.

8. ALH. Muhammad Badaru Abubakar.

Alhaji Muhammad Badaru Abubakar Shine Gwamna Na Takwas Ya Karbi Mulki A Hannun Dr. Sule Lamido A Shekarar 2015 Karƙashin Inuwar Jama’iyyar "All Progressives Congress"(APC)

Alhaji Mohammed Badaru Abubakar, MON, MNI, Hamshaƙin Mai Kuɗi Ne, Dan Kasuwa, Kuma Basarake, Wanda Ya Bada Gudunmawa kwarai da gaske A Fadin Wannan Jahar Musanman Abin Ya Shafi Harkar Noma Dan Habbaka Tattalin Arzikin Wannan Jahar.

9. Mal. Umar A Namadi Danmodi.

Mal. Umar A Namadi Danmodi Shine Gwamna Na Tara Ya Karbi Mulki A Hannun Alhaji Muhammad Badaru Abubakar A Shekarar 2023 Karƙashin Inuwar Jama’iyyar "All Progressives Congress"(APC).

Gwamnan Wanda Yake Gaf Da Shiga Shekara Ta Uku Akan Karagar Mulki a Zangon Farko, Ya Hidimtawa Jahar Musanman Wajen Daukar Ma'aikata da Kuma Kawata Jahar Da Tituna Musamman a Birnin Dutse Babban Birnin Jahar.

Allah Ya Saka Musu Da Alkairi 🤲

Wani Dan Media Ya Turawa Uban Gidan Sa Sako.Ko Me Yayi Zafi?
18/08/2025

Wani Dan Media Ya Turawa Uban Gidan Sa Sako.

Ko Me Yayi Zafi?

17/08/2025

Allah Sarki Malam Nata'Ala Ga Dai Sakon Sa Ga Al'ummar Duniya.

YANZU-YANZU : Ana Tsaka Da Zabe Agent Din Jam'iyyar Adawa Ta PDP, Ya Koma Jam'iyyar APC Nan Take Kuma Ya Koma Agent Din ...
16/08/2025

YANZU-YANZU : Ana Tsaka Da Zabe Agent Din Jam'iyyar Adawa Ta PDP, Ya Koma Jam'iyyar APC Nan Take Kuma Ya Koma Agent Din Jam'iyyar APC. A Zaben Cike Gurbin Na Garki da Babura a Jahar Jigawa.

An wankeshi Yana tsaka da Aikin Jam'iyya.PDP Yanzu Kuma Ya Koma Yiwa Jam'iyyar APC Aiki Nan Take.

✍️ Hassan Yunusa Takur.

SUBHANALLAHI: Yanzu muke samun labarin an sace motar Aliyu Masi Government House a SAN HUSSAIN Super Market dake nan tso...
15/08/2025

SUBHANALLAHI: Yanzu muke samun labarin an sace motar Aliyu Masi Government House a SAN HUSSAIN Super Market dake nan tsohuwar kasuwa cikin kwaryar jihar Gombe.

Duk wanda yaga wannan fostin din ya taimaka mana da Sharing 🙏🙏🙏

Duk wanda yaga motar ya taimaka ya tuntubi wannan lambar 08038671985 ko kuma yakai korafi ga jami'an tsaro.

Address

Takur Site Layin Kosai Opp Godiya Miyatti Market, Dutse
Jigawa

Telephone

+2347062795419

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Jigawa Online Media posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share