Komai Hausa

Komai Hausa Labarai da rahotanni kan abubuwan da ke faruwa a Duniya cikin harshen Hausa zallah.

Gwamnan Jihar Legas, Babajide Sanwo-Olu, ya bayyana goyon bayansa a hukumance ga mataimakinsa, Obafemi Hamzat, a matsayi...
27/04/2026

Gwamnan Jihar Legas, Babajide Sanwo-Olu, ya bayyana goyon bayansa a hukumance ga mataimakinsa, Obafemi Hamzat, a matsayin wanda zai gaje shi a zaɓen gwamna na shekarar 2027 a jihar Legas.

26/04/2026

Dattawan jam'iyyar APC A Jihar Jigawa sun amince da shugaban ƙasa Tinubu a matsayin ɗan takara ɗaya tilo na shugaban ƙasa, tare da gwamna Namadi Ɗanmoɗi a matsayin ɗan takara ɗaya tilo na gwamna a Jihar. Sannan kuma, sun yi alƙawarin saya musu fom ɗin takara, Cewar Farouk Adamu Aliyu.

07/04/2026

Yadda gobara tayi ta'adi a kwalejin koyon aikin lafiya da ungozoma ta Jahun, Jihar Jigawa. Daga: Sawaba FM.

An ba wa Tinubu takobin ci gaba da yaƙi da azzaluman Najeriya da matsalolinta.
07/04/2026

An ba wa Tinubu takobin ci gaba da yaƙi da azzaluman Najeriya da matsalolinta.

Atiku Ya Gargaɗi Tinubu Kan Rabo Kayan Abinci A 2027Atiku Abubakar ya bayyana wa Bola Tinubu cewa rabon kayan abinci kam...
07/04/2026

Atiku Ya Gargaɗi Tinubu Kan Rabo Kayan Abinci A 2027

Atiku Abubakar ya bayyana wa Bola Tinubu cewa rabon kayan abinci kamar shinkafa da spaghetti ba zai iya tabbatar da sahihancin mulkinsa ko kuma tabbatar da sake zaɓensa a zabukan 2027 ba.

Atiku ya jaddada cewa neman goyon baya na siyasa ya fi bukatar ayyuka da tsare-tsaren da za su amfanar da al'umma fiye da rabon kayan agaji kawai.

GWAMNAN JIGAWA NA ZIYARAR AIKI KAN NOMAN SHINKAFA A ƘASAR LABERIYA:-Gwamnan Jihar Jigawa, Umar Namadi, ya jagoranci wata...
07/04/2026

GWAMNAN JIGAWA NA ZIYARAR AIKI KAN NOMAN SHINKAFA A ƘASAR LABERIYA:-

Gwamnan Jihar Jigawa, Umar Namadi, ya jagoranci wata babbar tawaga ta gwamnatin jihar zuwa ƙasar Liberia domin tattaunawa kan bunƙasa harkar noma, da ɗaga darajar noman shinkafa.

Ziyarar wadda ke gudana a birnin Monrovia na ƙasar, ta biyo bayan gayyatar da mataimakin shugaban ƙasar ta Liberia, Jeremiah Kpan Koung, Sr., Ya yi masa wanda kuma shi ne ya karɓi gwamnan tare da jagorantar wata muhimmiyar ganawar haɗin gwiwa a tsakani.

A yayin ganawar, ɓangarorin biyu sun tattauna kan yadda za a inganta noma, tabbatar da wadatar abinci, da kuma ƙarfafa zuba jari daga ɓangaren kamfanoni masu zaman kansu.

Rahotanni sun ce ƙasar Laberiya na da burin cin gajiyar ƙwarewar da Jihar Jigawa ta samu wajen bunƙasa noma, musamman a harkar shinkafa, domin inganta samar da abinci a ƙasar.

Tawagar Jigawa ta haɗa da Darakta Janar na InvestJigawa, Hajiya Aisha Sheikh Mujaddadi, tare da ƙwararru a fannin noman shinkafa.

Haka kuma, ganawar ta samu halartar manyan jami’an gwamnatin Liberia, wakilan ofishin jakadancin Najeriya, da ƴan kasuwa, domin samar da hanyoyin haɗin gwiwa da zuba jari.

Ana sa ran wannan ziyara za ta haifar da ƙarin yawan amfanin gona, musamman shinkafa, tare da taimakawa wajen tabbatar da wadatar abinci a Jigawa da Najeriya baki ɗaya.

Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf, ya gana da mawaƙi, Rarara yau a gidan gwamnatin Jihar.
07/04/2026

Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf, ya gana da mawaƙi, Rarara yau a gidan gwamnatin Jihar.

Shugaban Majalisar Dokokin Jihar Kebbi, Muhammad Usman Zuru, ya rasu a wani asibiti da ke ƙasar Egypt bayan fama da wata...
07/04/2026

Shugaban Majalisar Dokokin Jihar Kebbi, Muhammad Usman Zuru, ya rasu a wani asibiti da ke ƙasar Egypt bayan fama da wata rashin lafiya da ba a bayyana ba zuwa yanzu.

JIGAWA TA KORI ƳANKWANGILA DA MASU HA'INCI CIKIN GIRKIN ABINCIN ƊALIBAIMa’aikatar Jin-Ƙai da Ayyuka na Musamman ta Jihar...
07/04/2026

JIGAWA TA KORI ƳANKWANGILA DA MASU HA'INCI CIKIN GIRKIN ABINCIN ƊALIBAI

Ma’aikatar Jin-Ƙai da Ayyuka na Musamman ta Jihar Jigawa, ta kori wasu ƴan kwangila da masu kula da girki (Kitchen Masters) sakamakon zamba da kuma samar da abinci marar inganci a shirin ciyarwa na jihar.

Matakin ya biyo bayan ziyarar bazata da Kwamishinan ma’aikatar, Auwal D. Sankara ya kai a ƙananan hukumomin Kazaure, Roni, Gwiwa da Yankwashi, inda aka gano ninka adadin ɗalibai domin karkatar da kuɗaɗe, da kuma rashin bin ƙa’idojin abinci.

Binciken ya nuna cewa a wasu makarantu, adadin ɗaliban da ake bayar da rahoto ya ninka na ainihi, yayin da wasu ƴan kwangila ke samar da abinci marar inganci ga ɗalibai da marasa lafiya.

A sakamakon haka, an kori wasu masu girki da ƴan kwangila da aka samu da laifi, yayin da aka kuma buƙaci a binciki wasu ma’aikatan makaranta da ake zargi da haɗa baki wajen ƙara yawan ɗalibai a rahoton.

Da yake jawabi, Sankara ya jaddada cewa gwamnati ba za ta lamunci cin hanci da rashawa ba, yana mai cewa za a ci gaba da ziyarar bazata domin tabbatar da gaskiya da kare dukiyar jama’a.

Ma’aikatar ta kuma gargaɗi sauran masu ruwa da tsaki da su guji duk wani abu da zai kawo cikas ga nasarar shirin ciyarwa a faɗin jihar.

06/04/2026

Yadda mawaƙi, Soja Boya ya gudanar da wasa yau a birnin Maiduguri na Jihar Borno.

Address

Social Media
Jigawa

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Komai Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share