Triming Radio 96.3 Auyo

Triming Radio 96.3 Auyo Muna yada sabbi kuma ingantattun labarai, dakuma shawarwari game da noma, kiwo da kasuwanci, kucigaba da kasancewa damu.

SERAP TA BAIWA GWAMNA NEJA WA'ADIN SA'O'I 48 YA JANYE UMARNIN RUFE WANI GIDAN REDIYO A JIHAR  Kungiyar kare hakkin jama’...
03/08/2025

SERAP TA BAIWA GWAMNA NEJA WA'ADIN SA'O'I 48 YA JANYE UMARNIN RUFE WANI GIDAN REDIYO A JIHAR

Kungiyar kare hakkin jama’a da tabbatar da gaskiya ta SERAP ta bai wa Gwamnan Jihar Neja, Umaru Bago, wa’adin sa’o’i 48 domin ya janye matakin rufe tashar rediyon Badeggi FM, mai zaman kansa dake Minna, babban birnin jihar.

A cikin wata budaddiyar wasika da ta wallafa a jiya asabat, wacce Mataimakin Daraktan SERAP, Kolawole Oluwadare, ya sa wa hannu, kungiyar ta bayyana matakin gwamnatin jihar a matsayin danniya da rashin bin doka, tana mai bukatar a dawo da lasisin tashar tare da janye barazanar rushe ginin ta.

SERAP ta kuma nemi Gwamna Bago da ya daina kai hare-hare kan mamallakin tashar, Shuaibu Badeggi, da sauran ma’aikatanta, tare da bayar da tabbacin lafiyar su da ‘yancinsu a fili.

Wannan martani na SERAP na zuwa ne bayan Gwamna Bago ya bayar da umarnin rufe tashar a ranar Juma’a, tare da soke lasisinta, da kuma umurta Kwamishinan Tsaron Cikin Gida da ya binciki bayanan mamallakin tashar.

Ba Abinda Nafi Tsoro A rayuwa Kamar Talauci- Jaruma Jemima Osunde Jarumar fina-finai, Jemima Osunde, ta bayyana cewa tal...
03/08/2025

Ba Abinda Nafi Tsoro A rayuwa Kamar Talauci- Jaruma Jemima Osunde

Jarumar fina-finai, Jemima Osunde, ta bayyana cewa talauci ne mafi girman tsoro a rayuwarta, tana mai cewa ba za ta iya rayuwa da shi ko kadan ba.

Ta bayyana hakan ne yayin wata hira da aka yi da ita a shirin The Culture League Podcast da dan wasan Super Eagles, Victor Boniface, ke gabatarwa.

Osunde ta ce tana da karfin hali wajen jure yawancin kalubale na rayuwa, amma talauci abu ne da ba ta da ikon jurewa. Ta kuma jaddada cewa tana daraja mutuncinta da tarbiyyarta fiye da komai, kuma za ta yi duk mai yiwuwa don guje wa talauci, matuƙar hakan bai tauye kimarta ba.

"Ba na so na ma dandana talauci. Ina jin dadin inda nake yanzu, kuma bana son komawa baya," in ji ta.

GWAMNATIN JIGAWA TA GINA JINGA MAI TSAWON 132KM DOMIN KARE AMBALIYAGwamnatin jihar Jigawa ta sanar da gina ganuwar kariy...
03/08/2025

GWAMNATIN JIGAWA TA GINA JINGA MAI TSAWON 132KM DOMIN KARE AMBALIYA

Gwamnatin jihar Jigawa ta sanar da gina ganuwar kariya daga ambaliya mai tsawon kilomita 132 tare da magidanan ruwa 32 domin shawo kan matsalar ambaliya da ke ci gaba da addabar sassa daban-daban na jihar.

Gwamna Umar Namadi ne ya bayyana hakan a wajen kaddamar da gangamin na dasa bishiyoyi na bana a birnin Dutse, inda ya ce ganuwar da ake ginawa a gefen Kogin Hadejia za ta kare gonaki da kuma ƙarfafa ƙauyuka wajen fuskantar barazanar sauyin yanayi.

An tura injinan tono na ruwa guda biyu domin fadada kogin da buɗe hanyoyin ruwa da s**a toshe, yayin da ake rabon kayan aiki ga al’umma don ƙarfafa gudunmawar su wajen rage illar ambaliya.

Hukumomin bayar da agajin gaggawa na ƙasa da na jiha sun bayyana cewa suna gudanar da wayar da kai da kuma ɗaukar matakan rigakafi a dukkan ƙananan hukumomi 27 na jihar.

GWAMNATIN JIGAWA TANA DAUKAR MATAKAN DAKILE AMBALIYAGwamnatin jihar Jigawa ta sake jaddada aniyarta na kare al’ummomin d...
03/08/2025

GWAMNATIN JIGAWA TANA DAUKAR MATAKAN DAKILE AMBALIYA

Gwamnatin jihar Jigawa ta sake jaddada aniyarta na kare al’ummomin da ke fuskantar barazanar ambaliya, biyo bayan hasashen da Hukumar Yanayi ta ƙasa ta fitar.

A wata ziyara ta duba ayyukan jingar kogin da aka gudanar a Auyo da yankunan Tsidir, Agin, Matsa, Sorakin, Jiyan, Tage, Turabu da Tandanu a ƙananan hukumomin Auyo, Malam Madori da Kirikasamma, Mataimakin Shugaban Kwamitin kwararru kan Rage Illar Ambaliya na Jiha, Alhaji Hamza Muhammad Hadejia, ya bayyana cewa an fara aiwatar da matakan gaggawa irin su haƙa hanyoyin ruwa da ƙarfafa ganuwar kariya.

Ya bayyana cewa waɗannan matakai ba wai kawai don kare rayuka da dukiyoyin jama’a ake yi ba, har ma domin bunƙasa harkar noma, tabbatar da wadatar abinci da kuma samar da ayyukan yi a karkara.

Shugabannin al’umma a yankunan da abin ya shafa sun yabawa Gwamna Umar Namadi bisa wannan matakin na gaggawa, tare da yin alwashin bayar da haɗin kai domin ci gaba da aiwatar da shirin kariya daga ambaliya.

SHEKARA HUDU KAWAI ZANYI IDAN KUKA ZABE NI A 2027 - Peter ObiA cikin wani sako da ya wallafa a shafinsa na X, ɗan takara...
03/08/2025

SHEKARA HUDU KAWAI ZANYI IDAN KUKA ZABE NI A 2027 - Peter Obi

A cikin wani sako da ya wallafa a shafinsa na X, ɗan takarar shugaban ƙasa a ƙarƙashin jam’iyyar Labour a zaben 2023, Peter Obi, ya sake jaddada cewa zai yi wa’adin mulki na shekara huɗu kacal idan aka zaɓe shi a matsayin shugaban ƙasa.

Obi ya ce shugabanci na gari ba ya ginuwa ne a tsawon lokacin da aka yi a mulki ba, sai dai tasirin da aka bari a cikin al’umma.

Ya kwatanta kansa da manyan shugabanni na duniya kamar Abraham Lincoln, John F. Kennedy da Nelson Mandela waɗanda duk da gajeren mulkinsu, sun bar tarihi na adalci da rikon gaskiya.

Peter Obi ya bayyana cewa wannan alƙawari ba salon yaudara ba ne, illa dai cikar niyyarsa ta sauya fasalin shugabanci a Najeriya, yana mai ƙarfafa hujja da abin da ya cimma a lokacin da yake gwamnan jihar Anambra, inda ya ce kowane ɗan Najeriya na da 'yancin samun gaskiya, tsabta da nagartaccen shugabanci cikin kankanin lokaci.

HADIN KAN YAN NAJERIYA NE ZAI RUGUZA GWAMNATIN APC A 2027 - EL-RUFAITsohon Gwamnan Jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, ya yi g...
03/08/2025

HADIN KAN YAN NAJERIYA NE ZAI RUGUZA GWAMNATIN APC A 2027 - EL-RUFAI

Tsohon Gwamnan Jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, ya yi gargaɗi mai ƙayatarwa cewa haɗin kan al'umma a Najeriya na iya rushewa gaba ɗaya idan Shugaba Bola Ahmed Tinubu da jam’iyyarsa ta APC s**a dawo kan mulki a shekarar 2027. El-Rufai ya bayyana hakan ne a wajen wani taron wayar da kan jama’a da jam’iyyar DC ta shirya a jihar Sokoto.

A yayin taron, El-Rufai ya nuna cikakken goyon bayansa ga haɗakar jam’iyyu masu adawa, inda ya sha alwashin yin aiki tukuru don ganin an kayar da APC a babban zaɓe mai zuwa. Ya jaddada cewa dawowarsa siyasa ba don son kai ba ne, sai don ya taimaka wajen gyara kura-kuran da ya ce gwamnatin yanzu ta tafka.

Tsohon gwamnan ya bayyana cewa tsarin zamantakewar al’umma a Najeriya na fuskantar barazana sakamakon manufofi da matakan da gwamnatin APC ke ɗauka. Ya ce abu ne mai yiwuwa kawai a dawo da zaman lafiya da amincewa idan ‘yan adawa s**a haɗa kai.

El-Rufai, wanda ya fice daga jam’iyyar APC a watan Maris 2025 ya koma jam’iyyar SDP, ya ce wannan taron da aka yi a Sokoto shi ne mataki na farko na wata babbar ƙetare da za ta haɗa ‘yan Najeriya don kawo sauyi a tsarin mulki da shugabanci.

FG DA TSAWAITA WA'ADIN DAUKAR AIKIN DAMARAGwamnatin Tarayya ta sanar da tsawaita wa'adin ɗaukar ma'aikata a hukumomin ts...
03/08/2025

FG DA TSAWAITA WA'ADIN DAUKAR AIKIN DAMARA

Gwamnatin Tarayya ta sanar da tsawaita wa'adin ɗaukar ma'aikata a hukumomin tsaro da ke ƙarƙashin Ma’aikatar harkokin Cikin Gida, wanda da farko aka shirya rufewa a gobe Litinin, amma yanzu an ƙara wa'adin har zuwa Litinin, 11 ga watan Agustan nan.

Babban Sakataren Hukumar Kula da Ma'aikata na Civil Defence, Correctional, Fire da Immigration (CDCFIB), Manjo Janar Abdulmalik Jibrin (mai ritaya), ne ya bayyana hakan cikin wata sanarwa da ya fitar a yau Lahadi. Ya ce an yanke shawarar tsawaita wa'adin ne domin baiwa ƙarin mutane damar samun shiga cikin aikin gwamnati.

Manjo Janar Jibrin ya nanata cewa wannan daukar aiki na bude ne ga kowa kuma babu wani kudin da ake caji. Ya ce hukumar na da niyyar gudanar da shirin cikin gaskiya da adalci.

Ya bukaci ‘yan Najeriya da su amfana da damar ta hanyar cike aikace-aikacensu da gaggawa kafin sabon wa'adin ya cika.

Yau Jamhuriyyar Nijar Ke Gudanar Da Bikin Zagayowar Ranar Samun ƳanciYau Lahadi 3 ga watan Agusta, Jamhuriyyar Nijar ke ...
03/08/2025

Yau Jamhuriyyar Nijar Ke Gudanar Da Bikin Zagayowar Ranar Samun Ƴanci

Yau Lahadi 3 ga watan Agusta, Jamhuriyyar Nijar ke gudanar da bikin zagayowar ranar samun ƴanci daga turawan mulkin mallaka, bikin da a wannan karon ma ya gudana kamar yadda aka saba cike da shagulgula baya ga tuni kan gwagwarmayar da wannan ƙasa ta yankin Sahel ta yi.

Bisa al’ada akan yi amfani da wannan rana wajen dashen itatuwa a sassan Nijar don yaƙi da gurgusowar hamada, matsalar da ke matsayin babban ƙalubale ga wannan ƙasa ta yankin Sahel.

An gudanar da bikin tunawa da zagayowar ƴancin na wannan shekara a jihar Zinder, bikin da ya samu halartar shugaban ƙasar na mulkin Soji Janar Abderrahman Tchiani da wasu manyan muƙarraban gwamnatinsa.

A jawabin daya gabatar gaban taron tunawa da ranar ƴancin shugaba Tchiani ya yabawa jajircewar jama’ar ƙasa baya ga shan alwashin magance matsalolin da ke ciwa jama’a tuwo a ƙwarya.

Shugaba Tchiani bayyana cewa gwamnatinsa za ta mayar da hankalin kan muhimman abubuwa guda biyar da s**a ƙunshi magance matsalar ƙarancin abinci da rage dogaro da ƙasashen ƙetare wajen samun abinci sai kuma wani gagarumin shirin taimakawa manoma don sarrafawa da kuma adana kayakin gonar da ke da sauran lalacewa.

Haka Zalika shugaban ya kuma sha alwashin magance matsalolin tsaro da kuma tabbatar da haɗin kan ƙasar.

Wannan ne karo na biyu da ake gudanar da wannan biki ƙarƙashin mulkin Soji waɗanda s**a hamɓarar da shugaba Mohammed Bazoum daga ƙaragar mulki a ranar 27 ga watan Yulin shekarar 2023.

A ranar 3 ga watan Agustan 1960 ne Nijar wadda ta Faransa ta mulka, ta samu ƴancin kai kodayake dama tun a cikin watan Disambar 1958 Faransar wadda ta mulki ƙasashe da dama a yankin na Sahel ta amince da shirin miƙa mulki ga ƴaƴan goyon nata, gabanin aiwatar da shi a hukumance cikin shekarar ta 1960.
Tun bayan wannan lokaci Jamhuriyyar Nijar ke amfani da kowacce ranar 3 ga watan Agusta don tunawa da ranar da ta samun ƴancin kai.

Gwamnati Za Ta Gyara Tsarin Birnin Maiduguri Domin Kare AmbaliyaGwamnan jihar Borno Babagana Umara Zulum ya ce gwamnatin...
03/08/2025

Gwamnati Za Ta Gyara Tsarin Birnin Maiduguri Domin Kare Ambaliya

Gwamnan jihar Borno Babagana Umara Zulum ya ce gwamnatinsa ta fara yunƙurin gyara tsarin birnin jihar domin kiyaye jihar daga ambaliya.

Zulum ya bayyana haka ne jim kaɗan bayan ziyarar gani da ido da ya yi wajen gyara da ake yi a dam ɗin Alau, inda ya ce har yanzu akwai wasu da suke gini a magudanan ruwa da kuma masu zuba shara suna toshe magudunan ruwa.

"Za mu duba tare da gyara tsarin birnin Maiduguri domin mu tabbatar dukkan magudanan ruwanmu a buɗe suke kuma suna aiki," in ji shi kamar yadda jaridar Daily Trust ta ruwaito.

Ya yi gargaɗin cewa duk wani gini da aka yi a magudunan ruwa za a rushe su.

Ya ce za su ɗauki matakin rusau ɗin ne domin kare sake aukuwar irin ambaliya da ta auku a ranar 10 ga watan Satumban 2024 a Jere da ke Maiduguri.

A game da fargabar da ake yi a Maiduguri na sake aukuwar ambaliyar, Zulum ya buƙaci ƴan jihar su kwantar da hankalinsu, inda ya ce akwai babbar ma'adana ta dam ɗin Alau ɗin, da ya ce za ta janye ruwan idan ya cika.

ACF ta yaba wa Tinubu, ta bukaci karin kulawa ga yankin ArewaKungiyar Arewa Consultative Forum (ACF) ta bayyana jin dadi...
02/08/2025

ACF ta yaba wa Tinubu, ta bukaci karin kulawa ga yankin Arewa

Kungiyar Arewa Consultative Forum (ACF) ta bayyana jin dadinta da wasu muhimman matakai da Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya dauka tun bayan hawansa mulki, musamman wadanda s**a shafi bunkasa tattalin arziki da tabbatar da zaman lafiya a kasashen kungiyar ECOWAS.
Wazirin Dutse kuma daya daga cikin jiga-jigan ACF, Bashir Dalhatu, ne ya bayyana hakan yayin taron tattaunawa tsakanin gwamnati da al’umma da aka shirya a Kaduna karkashin Ahmadu Bello Memorial Foundation.
A cewarsa, kirkirar Ma’aikatar Kiwon Dabbobi da bude kan iyakoki sun kawo sauki a rayuwar al’ummar Arewa. Haka kuma, ya yaba da yadda Shugaban kasa ke tura kudade zuwa jihohi domin tallafa wa cigaban jama’a, musamman a yankin Arewa.
“Shugaban kasa ya cancanci yabo bisa irin matakan da ya dauka, wadanda s**a rage radadin rayuwa a Arewa,” in ji Dalhatu.
Sai dai ya ce akwai sauran aiki, inda ya lissafa bukatu da dama da har yanzu ba a magance su ba, ciki har da rashin tsaro, talauci, yara da ba sa zuwa makaranta, da kuma manyan ayyuka kamar Ajaokuta, hakar mai a Kolmani da gina hanyoyi a Arewa.
Dalhatu ya bayyana cewa ACF ta riga ta mika wadannan bukatu ga Shugaba Tinubu tun ranar 30 ga Mayu, 2024, tare da neman kafa wani kwamiti da zai ci gaba da kula da batutuwan.
Ya kuma bukaci gwamnatin tarayya ta rika daukar Arewa a matsayin abokiyar tafiya mai muhimmanci, ba kawai lokacin neman kuri’a ba. Ya ce akwai bukatar a gyara tsarin kasafin kudi da kuma habaka masana’antun noma domin tallafa wa manoma da samar da ayyukan yi.
A karshe, Dalhatu ya nuna godiya da yadda manyan wakilan gwamnati s**a halarci taron a matsayin wakilan Shugaban kasa, yana mai bayyana kwarin gwiwar su cewa za a cika wa Arewa muradunta karkashin wannan gwamnati.

Rodrygo ya jaddada matsayarsa na son ci gaba da zama a Real Madrid, in ji ESPN
02/08/2025

Rodrygo ya jaddada matsayarsa na son ci gaba da zama a Real Madrid, in ji ESPN

Barcelona ta yanke shawarar cewa ba za su sayar da Ronald Araújo ba, kamar yadda rahoton La Ser ya bayyana Hanya ɗaya ti...
02/08/2025

Barcelona ta yanke shawarar cewa ba za su sayar da Ronald Araújo ba, kamar yadda rahoton La Ser ya bayyana

Hanya ɗaya tilo da zai iya barin kulob ɗin ita ce idan shi da kansa ya yanke shawarar tafiya.

Wannan ya nuna irin muhimmancin da Barcelona ke bai wa ɗan wasan na Uruguay, inda s**a ɗauke shi a matsayin muhimmin ginshiƙi a ginin tawagar yanzu da nan gaba. Duk da cewa akwai manyan kulake da ke nuna sha’awa.

Address

1 Auyo Road
Jigawa

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Triming Radio 96.3 Auyo posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share