Amana News

Amana News Feed the public with breaking news

19/08/2025

Celebrating my 4th year on Facebook. Thank you for your continuing support. I could never have made it without you. 🙏🤗🎉

GIDAN JARIDUN APA HAUSA, IDON MIKIYA DA DOKIN KARFE TV SUN YI WA SHEIKH MUHAMMAD SANI YAHYA JINGIR KARYA.Lallai gidajen ...
19/08/2025

GIDAN JARIDUN APA HAUSA, IDON MIKIYA DA DOKIN KARFE TV SUN YI WA SHEIKH MUHAMMAD SANI YAHYA JINGIR KARYA.

Lallai gidajen Jaridun Najeriya musamman masu yada labarai ta yanan Gizo sun zamo cikin mafi sharri a wannan zamani.

Yau mun tashi da ƙararrayi da s**a fito daga wannan gidajen Jaridu cewa a fadar su Sheikh Muhammad Sani Yahya Jingir Limamin Muslim - Muslim ya magantu wajen goyawa gwamnatin tarayya baya kan tallafin ziyarar da kiristoci ke zuwa ƙasar Isra'ila (Jerusalem).

To ga duk mai karatu ya sani Sheikh Muhammad Sani Yahya Jingir har zuwa yanzu da nake wannan rubutun bashi da masaniyar gwamnatin tarayya ta bada wannan tallafin b***e ma yayi magana

Don haka gidajen Jaridu da duk wani da ya yada cewa Sheikh Ya goyi bayan to Ya sani ya yi karya da Kuma kirkirar karyan ga Sheikh.

Da sun jira suji matsayar Sheikh daga nan Sai su yaɗa tun da Kowa yasan Sheikh baya nuku-nuku cikin lamuran Sa.

Sannan Muna kalubalantar Wadannan gidajen Jaridu da su Kawo audio ko video Ko Wani wallafa daga Shalkwatan Izala kan wannan zancen.

Don haka mun karyata wannan labarin Kuma muna kira duk Wani gidan Jarida da ya wallafa hakan da su yi saurin janye Wannan labarai.

Sannan Ina jan hankali da Kowa ya sani Sheikh baya da masaniya har zuwa wannan lokaci kan abubuwan da wadannan makaryata masu son a zagi Sheikh s**a wallafa.

Kawai sun aikata wannan abu ne don sun san in ance Sheikh Ya fadi haka to za su sami karuwan mabiya.

Munyi tirr da wannan labarai na APA Hausa, Idon MIKIYA. Dokin Ƙarfe TV da sauran su.

Ibrahim Maina Muhammad
(Shugaban Kwamitin Yanan Gizo, Jibwis Jihar Filato)

AL'UMMAR GARIN JOS, GA AIKIN ALLAH!Ina ku ke al'ummar garin Jos da ma Jihar Filato baki ɗaya? Ku matso kusa don yin aiki...
11/08/2025

AL'UMMAR GARIN JOS, GA AIKIN ALLAH!

Ina ku ke al'ummar garin Jos da ma Jihar Filato baki ɗaya? Ku matso kusa don yin aikin Allah.

Wannan gada a na yi mata laƙabi da gadar “La ilahaillah". Ta haɗa anguwan Rogo, Bayan Seminary, Laranto/Katako market, Kwanar Shagari, da sauran anguwanni.

Ta shafe tsawon shekaru masu yawa a wannan yanayi, inda a wasu lokuta, mabiyanta, musamman yara suke faɗawa.

Da wannan ne al'ummar garin Jos, musamman mabiya wannan hanya suke yin kira saboda Allah da kuma miƙa ƙoƙon barar su ga masu hannu da shuni a ciki da wajen jihar Filato, akan su dubi Allah su kawo agaji don ceton rayuwar ɗimbin al'umma.

Za'a iya tuntuɓar hukumar wannan kafa akan lambar waya 07015898279 don neman ƙarin bayani.

A taya mu ‘sharing' har saƙon ya isa gurin da a ke so.

Amana News, domin talakawa

BREAKING NEWS:Gwamnatin Kano ta tsawaita wa'adin dakatar da nuna wasu fina-finai 22 zuwa nan da mako gudaHukumar tace fi...
19/05/2025

BREAKING NEWS:

Gwamnatin Kano ta tsawaita wa'adin dakatar da nuna wasu fina-finai 22 zuwa nan da mako guda

Hukumar tace finafinai ta jihar Kano ta amince da tsawaita wa'adin dakatar da nuna wasu manyan fina-finai masu dogon zango 22.

Tun da farko hukumat ta sanar da dakatar da nuna finafinan ne sakamakon zarginsu da saɓa ƙa'idar hukumar, sannan ta ba masu finafinan mako ɗaya su cika ƙa'idojin hukumar.

Sai dai a wata sanarwa da shugaban Haɗaɗɗiyar Ƙungiyar Masu Shirya Finafinai ta Najeriya (MOPPAN) reshen jihar Kano, Ado Ahmad Gidan Dabino, ya ce an tattauna, kuma an fara samun mashalah.

BBC Hausa

Amana News

YANZU-YANZU: Hukumar Tace Finafinai Ta Jihar Kano Ta Dakatar Da Nuna Fim Din 'Dadin Kowa', 'Labarina', Gidan Sarauta, Ga...
19/05/2025

YANZU-YANZU: Hukumar Tace Finafinai Ta Jihar Kano Ta Dakatar Da Nuna Fim Din 'Dadin Kowa', 'Labarina', Gidan Sarauta, Garwaahi Da Karin Wasu Fitattun Finafinai Guda 18

Hukumar tace finafinan wadda ke karkashin jagorancin Abba El-mustapha ta dauki wannan kwakkwaran matakin ne a kokarin ta na ganin an tsaftace masana'antar fim ta hanyar kawo finafinai suna tantancewa kafin a sake shi.

A cewar Arewa Updates, Finafinan da aka dakatar sun hada da;

1. Dakin Amarya
2. Mashahuri
3. Gidan Sarauta
4. Wasiyya
5. Tawakkaltu
6. Mijina
7. Wani Zamani
8. Labarina
9. Mallaka
10. Kudin Ruwa
11. Boka Ko Malam
12. Wa Ya San Gobe
13. Rana Dubu
14. Manyan Mata
15. Fatake
16. Gwarwashi
17. Jamilun Jiddan
18. Shahadar Nabila
19. Dadin Kowa
20. Tabarma
21. Kishiyata
22. Rigar Aro

Me za ku ce kan wannan mataki?

Kasancewar Alkali Ustaz Abubakar Salihu Zaria a matsayin baƙo a Shirin Gabon Showroom ya janyo cecekuce tsakanin ƴan Are...
15/05/2025

Kasancewar Alkali Ustaz Abubakar Salihu Zaria a matsayin baƙo a Shirin Gabon Showroom ya janyo cecekuce tsakanin ƴan Arewa, inda wasu ke ganin bai dace malamin ya amsa gaiyatar ba, yayin da wasu kuma ke ganin Babu laifi da hakan.

Amana News

The Nigerian Film corporation( NFC) In partnership with Adonis production will be screening the historical screening thr...
14/05/2025

The Nigerian Film corporation( NFC) In partnership with Adonis production will be screening the historical screening thriller movie 77” at the Marche, during the 2025 Cannes Film Festival which gets underway May 13-24, in France. #77

Ali Nuhu Mohammed

Amana News

In reply, please quote;Ref No. CZ.5300/FPRD/FHQ/ABJ/VOL.6/436                Date: May 13, 2025The Director of News …………...
13/05/2025

In reply, please quote;
Ref No. CZ.5300/FPRD/FHQ/ABJ/VOL.6/436 Date: May 13, 2025
The Director of News
…………………………….
PRESS RELEASE

FINANCIAL CRIMES: POLICE NET TWO HIGH-PROFILE CYBER CRIMINALS, ARRAIGN SUSPECTS IN COURT.

In the ongoing fight against transnational financial crimes, the Nigeria Police Force INTERPOL National Central Bureau (NCB) Abuja has once again achieved significant breakthroughs, apprehending two high-profile suspects wanted for investment fraud and cybercrime. These arrests underscore the Nigeria Police Force's commitment to tackling both financial and cyber related threats.

Following a meticulous investigation, INTERPOL NCB Abuja successfully apprehended Robert Harms, a Canadian national, in connection with a fraudulent investment scheme targeting Tepison Enterprises, Ikot Ekpene, Akwa Ibom State. The investigation was initiated following a formal petition by the company. The complainant alleged that Harms, introduced through a Polaris Bank account officer in June 2023, fraudulently induced them to invest in a fictitious Waste-to-Energy Project in Canada. Under this pretence, Tepison Enterprises transferred $210,000 to secure a fabricated "capital project bond," with promises of a $30,000 return within four weeks, returns which never materialised.

Investigations revealed that Harms fabricated a fraudulent Project Bridge Loan Agreement and orchestrated the transfer of funds to an account in Dubai through Allah Mai Girma Bureau de Change in Abuja. Further inquiries confirmed that Harms had no legitimate affiliation with VDQ-NRG Systems Limited, the Canadian company he falsely claimed to represent, the CEO of VDQ-NRG Systems Limited when contacted denied any knowledge of or association with Harms. Harms was apprehended by INTERPOL operatives on February 7, 2025, at the Nnamdi Azikiwe International Airport, Abuja, while attempting to flee to Canada. Harms admitted to receiving the funds and violating the investment agreement. Formal criminal charges were filed at the Federal High Court, Uyo, on April 22, 2025. Harms was arraigned on May 9, 2025, and remanded at the Uyo Custodial Centre. The case has been adjourned to May 20, 2025.

In a separate operation, INTERPOL NCB Abuja also successfully re-apprehended Ms. Okeke Ogechi Njaka, who is wanted for series of cybercrimes and fraud-related offences, including cyberbullying, cyberstalking, obtaining money under false pretences, cheating, and criminal breach of trust. The case against Njaka was initiated in September 2020, following a report filed by Hajia Maryam Shehu, represented by M.I. Tsav & Co. Legal Practitioners & Notaries Public, Abuja. Investigations revealed Njaka's active involvement in cyberstalking and cyberbullying through multiple social media platforms, where she maliciously distributed n**e photos and videos of her victims.

Njaka was declared wanted via a Special Police Gazette Bulletin issued in 2021. She was initially arrested in Anambra State on January 4, 2025, but subsequently absconded after jumping administrative bail. Persistent intelligence-led efforts led to her re-arrest on May 8, 2025, in her hideout in Abuja. Njaka will be arraigned before the Federal High Court on Tuesday, May 13, 2025.

Furthermore, Njaka's non-governmental organisation, Ogechi Helping Hands Foundation, is also facing prosecution for allegedly obtaining N452,821,982 in a medical assistance scam before the Federal High Court Abuja, along with Emeka Ezeogbo and Tolotolo Family Foundation.

The Nigeria Police Force under the leadership of the Inspector-General of Police, IGP kayode Egbetokun Ph.D, NPM once again emphasises its unyielding resolve to combatting all forms of transnational financial crimes and urges members of the public to exercise utmost caution and due diligence before entering into high-value international agreements and to promptly report any suspicious activity to law enforcement agencies.

ACP OLUMUYIWA ADEJOBI, mnipr, mipra, fCAI
FORCE PUBLIC RELATIONS OFFICER,
FORCE HEADQUARTERS,
ABUJA.

13th May 2025.

Yayin da Alhazai daga Najeriya ke sauka a Madinah, tawagar dake karɓar baki da masauki ta NAHCON na aiki ba dare ba rana...
13/05/2025

Yayin da Alhazai daga Najeriya ke sauka a Madinah, tawagar dake karɓar baki da masauki ta NAHCON na aiki ba dare ba rana domin tarbar su da kuma tabbatar da sun samu masauki cikin sauƙi a unguwar Markaziyya – wacce ke kusa da Masallacin Annabi SAW

Ana baiwa kowane mahajjaci gado na musamman, sannan ma’aikatan suna koya musu yadda za su yi amfani da katin shiga, su hau lif, su yi amfani da bandaki, da kuma yadda za su gano hanyar komawa daga otal zuwa Masallacin Annabi SAW

Hajj Mabrur!!

Hajji Kiran Allah

RUNDUNAR SOJIN NAJERIYA TA CE SUN TARWATSA WANI SANSANIN BOKO Haram A Sambisa Rundunar sojin Najeriya ta ce sojojinta na...
12/05/2025

RUNDUNAR SOJIN NAJERIYA TA CE SUN TARWATSA WANI SANSANIN BOKO Haram A Sambisa

Rundunar sojin Najeriya ta ce sojojinta na Operation HADIN KAI (OPHK) sun kashe mayaƙan Boko Haram da dama a wani samame da s**a ƙaddamar a dajin Sambisa da ke jihar Borno.

Hakan na zuwa ne bayan sabbin hare-haren da mayaƙan Boko Haram s**a ƙaddamar kan wurare daban-daban a jihar Borno, inda matsalar rikicin Boko Haram ta fi ƙamari.

A sanarwa da rundunar ta wallafa a shafinta na X, mataimakin daraktan hulda da jama’a na Sojojin, Kyaftin Reuben Kovangiya, ya tabbatar da cewa sojojin sun yi arangama da ’yan ta’addan cikin kazamin fada.

Amana News

JAMB TA CE ZA TA YI NAZARIN ƘORAFE-ƘORAFEN DA AKA GABATAR KAN SAKAMAKON JARRABAWAR UTMEHukumar shirya jarrabawar shiga m...
12/05/2025

JAMB TA CE ZA TA YI NAZARIN ƘORAFE-ƘORAFEN DA AKA GABATAR KAN SAKAMAKON JARRABAWAR UTME

Hukumar shirya jarrabawar shiga manyan makarantu (JAMB) ta ce za ta sake duba Jarrabawar UTME ta shekarar 2025, bayan korafe-korafe da yawa daga jama’a kan matsalolin fasaha da tambayoyi da ba su cika ba, da kuma sakamakon ƙaramin maki ba kamar yadda aka saba ba.

A cikin wata sanarwa da jami'in hulda da jama'a na hukumar, Fabian Benjamin ya fitar, JAMB ta bayyana cewa ta karɓi “ƙorafe-ƙorafe da ba su saba ba” tun bayan fitar da sakamakon jarrabawar a ranar Jumma’ar da ta gabata.

Sanarwar ta ce wannan ƙoƙorafe-ƙorafen ne ya saka hukumar ta yanke shawarar yin bincike cikin gaggawa saɓanin yadda aka saba yi a baya watanni bayan kammala jarrabawar.

An haɗa ƙwararru daga fannin kimiyyar kwamfuta da masu kimanta jarrabawa da shugabannin jami’o’i don taimakawa a aikin.

Amana News

ANCELOTTI ZAI BAR MADRID DOMIN HORAS DA BRAZILAn tabbatar da kocin Real Madrid, Carlo Ancelotti a matsayin sabon kocin b...
12/05/2025

ANCELOTTI ZAI BAR MADRID DOMIN HORAS DA BRAZIL

An tabbatar da kocin Real Madrid, Carlo Ancelotti a matsayin sabon kocin babbar tawagar ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Brazil

Ɗan ƙasar Italiyan - wanda aka jima ana alaƙantawa da aikin horas da Brazil - ya kasance ɗan ƙasar waje na farko da zai horas da babbar tawagar ƙasar.

Ana sa ran Ancelotti zai fara sabon aikin nasa zuwa ƙarshen watan da muke ciki.

A watan Maris ne Brazil ta kori manajan tawagar ƙasar - Dorival Júnior - bayan Argentina ta casa ƙasar 4-1 a wasan neman gurbin shiga gasar Kofin Duniya.

Amana News
BBC Sport

Address

Jos
9090

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Amana News posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share