Kaduna Media Forum

Kaduna Media Forum Officially page kaduna media forum of the Islamic movement under the leadership of Sheikh Ibraheem Zakzaky(H)

'YANCI KWATARSA AKE YI, BA SIYOSHI AKE YI A KASUWA BA'– Inji Malam Aliyu Tirmizi KadunaMalam Aliyu Tirmizi, wakilin 'yan...
05/06/2026

'YANCI KWATARSA AKE YI, BA SIYOSHI AKE YI A KASUWA BA'

– Inji Malam Aliyu Tirmizi Kaduna

Malam Aliyu Tirmizi, wakilin 'yan uwa almajiran Sheikh Zakzaky na Kaduna, ya yi wannan magana ne a lokacin gudanar da muzaharar nuna goyon baya ga al'ummar Palestine a Kaduna.

Malamin ya ce gwagwarmayar Palestine ba ta Musulmi ko Kirista ko wani rukuni na musamman ba ce, ya ce ta kowa ce, duk mai mutuntaka.

Ya ce wannan gwagwarmaya da al'ummar Palestine ke yi, suna neman 'yancinsu ne wanda aka daɗe ana take musu, inda yanzu s**a yunƙura domin neman wannan 'yanci nasu.

Ya ce dama 'yanci ba siyoshi ake yi a kasuwa ba, kwatarsa ake yi. Domin neman 'yanci sai an fito, an sadaukar, sannan ake samunsa.

Malamin ya ce su almajiran Sheikh Zakzaky suna goyon bayan wannan gwagwarmaya da al'ummar Palestine ke yi.

Ya ce sannan suna kira ga gwamnatin Najeriya da ta yanke alaƙa da haramtacciyar ƙasar Isra'ila, tare da yin Allah-wadai da kashe-kashen raunanan al'ummar Palestine da Yahudawa suke yi.

Daga ƙarshe, malamin ya ce za su ci gaba da wannan fitowa domin bayyana goyon bayansu ga al'ummar Palestine.

Kaɗan kenan cikin jawabin malamin.

Bin Muhammad KD
Kaduna Media Forum
2026/06/05 M

JAGORA YANASO YAGA KUNYI YUNKURI NE SAI SHIKUMA YA KARFAFEKU.      Inji Malam Aliyu Tirmizi KadunaWasu Suna Jiran Suji J...
04/06/2026

JAGORA YANASO YAGA KUNYI YUNKURI NE SAI SHIKUMA YA KARFAFEKU.

Inji Malam Aliyu Tirmizi Kaduna

Wasu Suna Jiran Suji Jagora Yace Suyi Abu Ne Kuma Lallai Jagora Bazece Suyi Ba Amma Idan Yaga Kun Nuna Zakuyi To Yana Karfafaku .

Wata Shekara Za'ayi Muzaharar Qudus Sai Jagora Yafadi Duk Garuruwa Daza'ayi Sai Befadi Kaduna Ba Sai Muka Tambayi Jagora Mukace Akara makallah Munji Kafadi Garuruwa Daza'ayi Muzaharar Qudus Amma Baka Fadi Kaduna Ba Sai Jagora Yace Ai Kaduna Munji Ance Azzalumai Zasu Sanya Bomb A Waje kaza Da Waje Kaza Sai Mukace Mawa Jagora Ai Akwai Wani Waje Da Zamuyi Sai Jagora Yace Don Allah Zakuyi? Sai Mukace Eh Sai Jagora Yafara Mana Addu'a Yanata Farin Ciki Inji Malam Aliyu Tirmizi,

Wato Shi Jagora Bazece Kuyi Dole Ba Amma Idan Ku din Kunga Yak**ata Kuma Kukayi To Jagora Zeyi Farin Ciki Kuma Zemuku Addu'a.

Wani jawabi na Malam Aliyu Turmizi shekar da ta wuce wajen wani taro a kaduna,

Bin Muhammad KD
kaduna media forum
_2026/06/04 M,

*Taya Murnar Edil Ghadirkum**Daga Dadanlin Masu Yaɗa Labarai na Da'irar Kaduna Wato Kaduna Media Forum*Muna an fani da w...
04/06/2026

*Taya Murnar Edil Ghadirkum*

*Daga Dadanlin Masu Yaɗa Labarai na Da'irar Kaduna Wato Kaduna Media Forum*

Muna an fani da wannan damar a kuma wannan rana ta 18 /Zulhajji / ranar da Manzon Rahama Muhammad (S) ya nasabta Wakilin sa a doron kasa Imam Ali Bin Abi Ɗalib (AS) a madadin kafatalin dukkan ma'aikatan Kaduna Media Forum muna taya Jagoran mu Sheikh Ibraheem Zakzaky (H) murna da wannan rana da kuma Imamin Zamanin mu Imamul Hujjah (ATF) da dukkan musulman Duniya.

Allah ya maimaita mana.

Kaduna Media Forum

Ba a shiga gaban jagora kuma ba a bari yayi ma nisa ana bin jagora ne duk wajen da ya cire kafa sai ka saka ba wuceka ba...
03/06/2026

Ba a shiga gaban jagora kuma ba a bari yayi ma nisa ana bin jagora ne duk wajen da ya cire kafa sai ka saka ba wuceka ba kuma bai maka nisa ba kuma baka shiga gaban sa ba. ana rike jagora ne irin rikon noti mai tsatsa wato kwance shi sai an shirya to ya zama ka kankame jagora fiye da haka_ Inji Malam Aliyu Turmizi Kaduna

Bin Muhammad KD
Kaduna Media forum
_2026/06-03 M,

IDAN JAGORA ZAI FITO TO DAN UWA KO WANI ABU ZAI SIYAR YASAIDA YASHIGA ABUJA,      Cewar Malam Aliyu Umar Turmizi.Wakilin...
02/06/2026

IDAN JAGORA ZAI FITO TO DAN UWA KO WANI ABU ZAI SIYAR YASAIDA YASHIGA ABUJA,

Cewar Malam Aliyu Umar Turmizi.

Wakilin yan uwa Almajiran Sheikh Zakzaky (H) na Garin Kaduna Malam Aliyu Umar Turmizi yafadi hakan ne lokacin da yake kulle jawabin jajen shahadar Kwamandan rundunar Allah ta kasar Lubnan Sayyid Hasan Mai Nasara,

Malamin yace abin mamaki sai kaga yan uwa Sunyi zamansu a garuruwansu Malam yana abuja yana jawabi baisan mezai faru ba.

Yaci gaba da cewa gara Dan uwa Yazama komai zai faru yafaru a gabanka domin har yanzu Azzalumai suna neman yanda zasuyi su auk**a Jagora yace ko kunzaci shikenan yanzu?.

Malamin yace Wannan maulidin da s**aje abuja duk wanda yaje yaga abinda yafaru na zuwan Sojoji Idan banda taimakon Allah da ruwan Sama da Yazo da Wani labari yan uwa zasuji Domin da shirinsu s**azo wajen taron lolacin Jagora yana jawabi,

Yace gara yazama bakanan kayi Shahada akan kare Jagora bawai kana garinku Kaji bakin labari ba Domin har yanzu Azzalumai Basu hakura ba.

Yakara da cewa Idan ma Dan uwa yace Bashi da kudin shiga Abuja to Idan Yazama Babu Jagora Allah Ya kiyaye Zaka Samu kudi Duk inda Suke domin guduwa.

Yace dole kowane dan uwa yashirya shiga abuja kowane lokaci Musamman Idan Jagora Zai Fita Domin Wadannan azzalumai din suna bibiyar kowane takun Jagora Kuma Kunga Dai Abinda yake faruwa yanzu na salon kisan haramtacciyar kasar tatsuniya,

Daga karshe yace Allah yakyauta kana garinku Kaji Labarin ankai kan Jagora yace mudai gara yazama Muna Wajen afara gamawa Damu Yazama bamuga Abinda yasami Jagora ba,

Kadan Daga Cikin Jawabin Malamin kenan da ya gabatar a wajen jajen shahadar Sayyid Hasan Mai Nasara da ya gudana a Fudiyya rimi rigasa kaduna wata Lahadi,







Bin Muhammad KD
Kaduna Media Forum
_2026/06/02 M,

Taron Cin Abincin Salla Domin Samun Kusanci Da Haɗin Kan Musulmi A Garin Maraban Jos A yau Litinin, 15 ga watan Zhul-Hij...
01/06/2026

Taron Cin Abincin Salla Domin Samun Kusanci Da Haɗin Kan Musulmi A Garin Maraban Jos

A yau Litinin, 15 ga watan Zhul-Hijjah, 1447H (01/06/2026) ne, ƴan'uwa musulmi mabiya Jagora Sayyid Ibraheem Zakzaky (H) na garin Maraban Jos, Kaduna, s**a shirya taron cin abincin Salla domin samun kusanci, fahimtar juna da kuma haɗin kai a tsakanin al'ummar musulmi.

Taron ya samu halatar sarakai, limamai da kuma manyan malamai da ke garin, bayan buɗe taro da addu'a daga bakin Malam Shehu, sai karatun Alƙur'ani daga bakin Malam Muttaƙa limamin Kwara-Kwara, sannan Malam Rayyanu Umar Sanda ya bayyana maƙasudin taro k**ar haka; "Cin abincin Salla da kuma tattaunawa tsakanin ɓangarorin al'ummar musulmi domin samun kusanci da fahimtar juna".

Malami na farko daga ɓangaren Ɗarikar Tijjaniyya, Malam Zubairu Bin Jafar, shi ne ya fara jawabi akan Maudu'i mai taken "Muhimmancin haɗin kai a tsakanin al'ummar musulmi", inda a jawabin nasa, ya bayyana cewa duk inda musulmi yake to ɗan'uwan musulmi ne, haka nan, ko ba komai to Musulunci ya haɗa mu, Alkur'ani ya haɗa mu, Manzon Allah (S) ya haɗa mu, sannan ya ci gaba da kira akan mu so juna, mu riƙa kyauta a tsakaninmu domin tana janyo soyayya, a ƙarshen jawabinsa ya ƙarƙare da cewa, kowannenmu ya kula da haƙƙin makoftaka.

Malami na biyu daga ɓangaren Izala, wato Malam Umar Waliy ya yi magana ne akan maudu'i mai taken " Halin da Musulunci da al'ummar musulmi suke ciki a yau", ya bayyana a jawabinsa, irin jin daɗinsa da shirya irin wannan taro, sannan ya ci gaba da kawo ayoyi da Allah Ta'ala Ya yi umurni da haɗin kai, ya bayyana cewa k**ar yadda kafirai kansu yake a haɗe to mu ma musulmai yana da kyau mu zama a dunkule, domin babbar matsalar da ke damun musulmi a duniyar yau ita ce rarrabuwa, sannan ya ƙarfafi yin ziyara a tsakanin ɓangarorin. A ƙarshe ya bada misali da nuna cewa sai ka ga malamai sun aje saɓani idan a wajen taron siyasa ne, ana gaisawa da juna ana fara'a saboda za a ba wa kowa kuɗi, to a haɗe kai saboda Allah ne, sannan a kula ƴan siyasa suna haɗa malamai faɗa, inda ya bada misali sai ba wa wani Malamin wani ɓangare k**ar miliyan 3, sai kuma su je su ce Malam wane ya baku kuwa? mun ba shi ai ya raba har da ku, ko dai don ya ga ba fahimtar ku ɗaya bane?

Malami na uku, shi ne Malam Sani liman akan maudu'i mai taken " Abin da al'ummar musulmi ya k**ata su yi a halin da ake ciki", sai babban limamin Masallacin Juma'a na garin, wato Imam Malam Hayatu, sannan Na'ibinsa Malam Nura akan maudu'i mai taken " Tarbiyyar yara a Musulunci".

Wakilin ƴan'uwa musulmi na garin Maraban Jos, Malam Abdullahi Umar shi ne ya yi ta'aliƙi bayan sauran malamai da wakilin sarki sun kammala jawabansu, a jawabin nasa, ya bayyana cewa wato batun haɗin kai dai umarni ne na Allah Ta'ala, kuma irin wannan haɗuwa takan sanya a yi zumunci, sannan kusantar juna shi ke kawo fahimta da rage saɓani, sannan ya ci gaba da cewa irin wannan taro ba ɓoyayyen abu bane, domin tun bayan juyin-juya halin Musulunci a ƙasad Iran, Imam Khomaini (QS) ya assasa irin wannan, wanda ake gayyatar musulmi masu fahimta daban-daban daga nahiyoyi daban-daban domin a samu kusanci da fahimtar juna, haka a nan gida Najeriya ma, Jagoranmu Sayyid Zakzaky (H) tsawon shekaru ya assasa irin wannan, wanda ake gayyatar musulmi (malamai) daga firƙoƙi daban-daban a matakin ƙasa da garuruwa duka domin a samu haɗin kai, a ƙarshe ya ƙarƙare da bayyana cewa yana kyau mu riƙa yiwa juna adalci, a nan ya kawo ayoyi da suke magana dangane da hakan da sauran jawabai.

A ƙarshe Malam Sani shugaban alarammomi ne da kuma Malam Ɗanladi Mamman daga ɓangaren Ƙur'ani Zalla, s**a rufe taron da addu'a aka sallami al'umma.

Rahoto; Ali Al-Haidary Maraban Jos

—KD Media Forum
01/06/2026M
15/12/1447H

*SANARWA GA DUK WANI ƊALIBIN FUDIYYA NA GARIN KADUNA*Assalamu alaikum wa Rahmatullahi ta'ala,Allahumma Salli‘ala Muhamma...
01/06/2026

*SANARWA GA DUK WANI ƊALIBIN FUDIYYA NA GARIN KADUNA*

Assalamu alaikum wa Rahmatullahi ta'ala,

Allahumma Salli‘ala Muhammad wa Ahli Muhammad wa ‘ajjil Farajahum.

Dandalin Tsofaffin Ɗaliban Makarantun Fudiyyah na Harkar Musulunci ƙarƙashin jagorancin Sayyid Ibraheem Zakzaky(H)
Suna farin cikin sanar da dukkanin ɗaliban da s**a yi karatu a makarantun Fudiyyah da sauran makarantun Harkar Musulunci, da ke ƙarƙashin inuwar (FOSA) na yankin Kaduna da kewaye cewa, sak**akon shirye-shiryen gudanar da bikin (Fudiyyah Day) wanda za a gudanar k**ar haka.

Ranar
Asabar, 13/06/2026, dai-dai da
27th Zhulhajj 1447H;

Kwamitin shirya taron sun yanke cewa Kowane Ɗalibi da Ɗaliba Tsoho da sabo, zasu bayar da hakkin kuɗi daga ₦500 zuwa sama domin tallafawa wannan babban Taro ɗin.

Account number: 8087198579
Khadija Muhammad Tasiu
Bank: Monie Point

Da fatan ƴan uwa za su bada haɗin kai da tallafi domin gudanar da wannan taro cikin nasara da armashi,
Allah Ya bada ikon tallafawa.

Sanarwa:
Kwamitin Shirya (Fudiyya day)
01/06/2026

MUNA KIRAN SABUWAR GWAMNATIN KADUNA DA TA TUHUMI EL-RUFA’I KAN ABINDA YA YI MANA IDAN DA GASKE TAKE— Cewar Malam Aliyu U...
01/06/2026

MUNA KIRAN SABUWAR GWAMNATIN KADUNA DA TA TUHUMI EL-RUFA’I KAN ABINDA YA YI MANA IDAN DA GASKE TAKE
— Cewar Malam Aliyu Umar Tirmizi

Daga: Bin Muhammad KD ✍️

Bayan kammala muzaharar Maulidin Manzon Allah (S) da aka gudanar a garin Kaduna ranar Alhamis kwanakin baya, wakilin ƴan uwa Almajiran Sheikh Ibrahim Zakzaky (H) na Kaduna, Malam Aliyu Umar Tirmizi, ya gabatar da takaitaccen jawabi a wajen rufe taron.

Malamin ya fara jawabin nasa da taya al’ummar Musulmi murnar zagayowar ranar haihuwar Manzon Allah (S), inda ya yi bayani kan falaloli, daraja da matsayi na Manzon Allah (S), da kuma girman wannan wata mai albarka.

Daga nan sai ya yi magana kan haɗin kai a tsakanin Musulmi, inda ya bayyana cewa masu kashe Musulmi a Gaza, Palestine, su ne ke kashe Musulmi a nan Nijeriya. Ya yi kira ga al’ummar Musulmi da su haɗa kai domin fuskantar wannan ta’addanci, yana mai cewa Yahudawan nan ne ke da hannu a irin waɗannan ayyuka ko’ina.

Malamin ya kuma tabo batun sabon tsarin mulkin Jihar Kaduna, inda ya ce suna ganin alamun cewa sabuwar gwamnatin na iya son sauya salon siyasa, amma ya jaddada cewa ba za su yarda da hakan ba sai sun ga an tuhumi tsohon gwamnan jihar, Nasiru El-Rufa’i, kan abin da ya aikata musu a lokacin mulkinsa.

Ya ce idan iyakar abin da sabuwar gwamnati za ta yi shi ne magana kawai ba tare da daukar mataki ba, to babu wani sauyi da aka samu. Domin a cewarsa, babu wanda aka zalunta k**ar yadda aka zalunce su a gwamnatin da ta gabata. Ya kara da cewa idan ba a tuhumi El-Rufa’i ba, to su ma ba za su dauki sabuwar gwamnatin a matsayin wacce ta zo da canji ba, kuma za su ci gaba da yi mata addu’o’i iri-iri k**ar yadda s**a yi wa wadda ta gabata.

Malam Aliyu Umar Tirmizi ya jaddada cewa idan za a fara biyan hakki, to su ne ya k**ata a fara da su, domin a cewarsa an kashe musu mutane sama da 1000 a bainar jama’a, an kona wasu, an k**a wasu ba tare da laifi ba, sannan tsohon gwamnan ya rushe musu makarantu, gidaje da asibitoci.

A karshe ya ce ba za su amince da cewa akwai wani bambanci tsakanin sabuwar gwamnati da wacce ta gabata ba, sai idan sun ga an tuhumi tsohon gwamnan Jihar Kaduna, Nasiru El-Rufa’i, kan laifukan da ya aikata musu. Idan kuwa hakan bai faru ba, a wajensu babu wani canji da aka samu.

Wannan kadan ne daga cikin jawabin da Malam Aliyu Umar Tirmizi ya gabatar a wajen rufe muzaharar Maulidin Manzon Allah (S) da ta gudana a wata Alhamis a garin Kaduna.

Kaduna Media Forum
_ 2026/06/01 M,

YANZU ZA A IYA CIN YAKI TA HANYAR KAFOFIN MEDIA: Cewar Malam Aliyu Umar TirmiziDaga:Bin Muhammad KD ✍️Malam Aliyu Umar T...
01/06/2026

YANZU ZA A IYA CIN YAKI TA HANYAR KAFOFIN MEDIA: Cewar Malam Aliyu Umar Tirmizi

Daga:Bin Muhammad KD ✍️

Malam Aliyu Umar Tirmizi, wakilin ’yan’uwa Musulmai almajiran Sheikh Zakzaky (H) na garin Kaduna, cikin jawabin da ya gabatar a taron Mu’utamar na yankin Kaduna Media Team, ya yi muhimman bayanai da nasihohi ga ’yan media.

Da farko, Malamin ya jaddada cewa duk wani abu da mutum zai yi, ana bukatar ya kasance da ikhlasi, wato ya yi shi domin Allah, ba don a yaba masa ko a san shi ba. Ya ce duk wanda ya yi aiki saboda Allah, Allah kansa ne zai kai shi ga nasara da abin da yake nema.

Ya ci gaba da cewa Allah yana son aikin da aka yi ne domin Shi. Saboda haka aikin Media idan aka yi shi da ikhlasi, yana da girma a wajen Allah. Ya kara da cewa sau da yawa ma, dan Media yakan fi malamin da ake gani yana wa’azi daraja a wajen Allah—idan malamin baya yin aikinsa da ikhlasi.

Matsayin Mace a Harkar Media

Malam ya tabo muhimmancin rubutun mata a cikin Media. Ya ce akwai mutane da idan s**a ga mace ce ta yi rubutu, sai lallai su tsaya su karanta. Don haka bai dace a bar mata a baya ba. Jagora (H) yana son aikin hadin kai, kowa ya taka rawarsa. Sai dai, ya ce matsala tana faruwa ne idan mace ta yi aure, wasu maza s**an hana matansu cigaba da aikin.

Media a Matsayin Mafakar Kare Gaskiya

Malam Tirmizi ya bayyana cewa yanzu Media ta zama babbar kafa ta yakar mummunan ra’ayi da bayyana gaskiya. A da mutane s**an dogara da abin da gidajen jarida ko radiyo ko TV s**a fada, saboda ba a bar wani yaji daga wani bangare ba. Wannan ya bai wa makiya damar yada karairayi.

Ya ce yanzu, zuwan kafofin sada zumunta ya bai wa ’yan uwa damar bayyana gaskiyar da take faruwa, ba k**ar a da ba. Idan mutum ya yi karya a kansu, su ma za su iya mayar da martani cikin gaskiya da hujja ta hanyar Media.

Hanyoyin Mu’amala a Media

Malam ya gargadi ’yan Media da su guji shiga cece-kuce, zage-zage da cin mutunci. Ya ce Jagora (H) ya sha gargadi a kan wannan, har ma ya yi kira ga masu zage-zage da su daina gaba daya.

Ya ce yin raddi kuwa, ba wajibi bane kowa ya rika yin raddi. Idan mutum daya ko biyu sun yi raddi cikin hikima da ilimi, hakan ya wadatar. Amma idan kowa zai yi raddi, sai ya koma rikici da hayaniya. Jagora (H) ya ce akwai wadanda Allah ya ba su basiyar yin raddi cikin hikima, su ne ya k**ata a bari su yi.

Media a Matsayin Filin Yaƙi

Ya kara da cewa yanzu ana iya cin yaƙi ta hanyar Media, domin ta zama makami mai ƙarfi fiye da na gargajiya. Saboda haka ’yan Media su zage dantse, su jajirce, su kara neman ilimi domin inganta aikinsu.

Ya ce Jagora (H) ya ba wa Media muhimmanci ne saboda yadda take da tasiri wajen fallasa zalunci. A lokacin hare-haren da jahiliyya ta yi wa ’yan’uwa, Media ta taka babban rawa wajen nuna wa duniya gaskiyar abin da ke faruwa, har mutane s**a nuna tausayi.

Game da Hotuna da Rahotannin Waki’a

A karshe, Malam ya ja hankalin masu daukar hoto da su rinka kula da irin hotunan da za su saki idan an samu waki’a. Kada a saki hoton da zai nuna k**ar ’yan’uwa sun yi galaba a kan jami’an tsaro, domin hakan yana iya hana wasu mutane tausaya musu. A fiye a saki hotunan da ke nuna yadda jami’an tsaro s**a aukawa ’yan’uwa, musamman idan har an harbe su—domin hakan shi ne gaskiyar abin da ke faruwa.

Haka kuma ya ce Jagora (H) ya jaddada cewa idan aka yi waki’a, a fara sakin rahoton taron da aka yi kafin a saki na waki’ar. Wannan domin kada a nuna k**ar an yi taro don a yi rikici.
Kammalawa Wannan kadan ne daga cikin jawabin da Malam Aliyu Umar Tirmizi ya gabatar a taron Mu’utamar na Kaduna Media Team wanda ya gudana a masallacin Sheikh Dahiru Usman Bauchi, Tudun Wada Kaduna, ranar Lahadi 7 ga Disamba 2025.

Kaduna Media Forum
_2026/06/01 M,

"Indai mutum ɗan'uwa ne almajirin Jagora Sayyid Zakzaky (H), kuma mazaunin garin Kaduna, sannan ya kasance mai halartar ...
31/05/2026

"Indai mutum ɗan'uwa ne almajirin Jagora Sayyid Zakzaky (H), kuma mazaunin garin Kaduna, sannan ya kasance mai halartar wajen Ta'alim, Pre-Khuɗba da jawabobin Malam Mukhtar Sahabi Kaduna, to ba wata iska ko guguwa da zata zo ta girgiza shi (a Harkar nan) sai dai shi ma ya jawo wani".

—Cikin jawabin da Waƙilin ƴan'uwa na Da'irar Kaduna, Malam Aliyu Tirmizi ya yi ma ƴan'uwa na Kaduna, waɗanda suke mazauna Ƙasar Iraqi da s**a kai mai ziyarar Sallah.

Kaduna Media Forum

Address

Kaduna South
800001

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Kaduna Media Forum posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Kaduna Media Forum:

Share