01/06/2026
Taron Cin Abincin Salla Domin Samun Kusanci Da Haɗin Kan Musulmi A Garin Maraban Jos
A yau Litinin, 15 ga watan Zhul-Hijjah, 1447H (01/06/2026) ne, ƴan'uwa musulmi mabiya Jagora Sayyid Ibraheem Zakzaky (H) na garin Maraban Jos, Kaduna, s**a shirya taron cin abincin Salla domin samun kusanci, fahimtar juna da kuma haɗin kai a tsakanin al'ummar musulmi.
Taron ya samu halatar sarakai, limamai da kuma manyan malamai da ke garin, bayan buɗe taro da addu'a daga bakin Malam Shehu, sai karatun Alƙur'ani daga bakin Malam Muttaƙa limamin Kwara-Kwara, sannan Malam Rayyanu Umar Sanda ya bayyana maƙasudin taro k**ar haka; "Cin abincin Salla da kuma tattaunawa tsakanin ɓangarorin al'ummar musulmi domin samun kusanci da fahimtar juna".
Malami na farko daga ɓangaren Ɗarikar Tijjaniyya, Malam Zubairu Bin Jafar, shi ne ya fara jawabi akan Maudu'i mai taken "Muhimmancin haɗin kai a tsakanin al'ummar musulmi", inda a jawabin nasa, ya bayyana cewa duk inda musulmi yake to ɗan'uwan musulmi ne, haka nan, ko ba komai to Musulunci ya haɗa mu, Alkur'ani ya haɗa mu, Manzon Allah (S) ya haɗa mu, sannan ya ci gaba da kira akan mu so juna, mu riƙa kyauta a tsakaninmu domin tana janyo soyayya, a ƙarshen jawabinsa ya ƙarƙare da cewa, kowannenmu ya kula da haƙƙin makoftaka.
Malami na biyu daga ɓangaren Izala, wato Malam Umar Waliy ya yi magana ne akan maudu'i mai taken " Halin da Musulunci da al'ummar musulmi suke ciki a yau", ya bayyana a jawabinsa, irin jin daɗinsa da shirya irin wannan taro, sannan ya ci gaba da kawo ayoyi da Allah Ta'ala Ya yi umurni da haɗin kai, ya bayyana cewa k**ar yadda kafirai kansu yake a haɗe to mu ma musulmai yana da kyau mu zama a dunkule, domin babbar matsalar da ke damun musulmi a duniyar yau ita ce rarrabuwa, sannan ya ƙarfafi yin ziyara a tsakanin ɓangarorin. A ƙarshe ya bada misali da nuna cewa sai ka ga malamai sun aje saɓani idan a wajen taron siyasa ne, ana gaisawa da juna ana fara'a saboda za a ba wa kowa kuɗi, to a haɗe kai saboda Allah ne, sannan a kula ƴan siyasa suna haɗa malamai faɗa, inda ya bada misali sai ba wa wani Malamin wani ɓangare k**ar miliyan 3, sai kuma su je su ce Malam wane ya baku kuwa? mun ba shi ai ya raba har da ku, ko dai don ya ga ba fahimtar ku ɗaya bane?
Malami na uku, shi ne Malam Sani liman akan maudu'i mai taken " Abin da al'ummar musulmi ya k**ata su yi a halin da ake ciki", sai babban limamin Masallacin Juma'a na garin, wato Imam Malam Hayatu, sannan Na'ibinsa Malam Nura akan maudu'i mai taken " Tarbiyyar yara a Musulunci".
Wakilin ƴan'uwa musulmi na garin Maraban Jos, Malam Abdullahi Umar shi ne ya yi ta'aliƙi bayan sauran malamai da wakilin sarki sun kammala jawabansu, a jawabin nasa, ya bayyana cewa wato batun haɗin kai dai umarni ne na Allah Ta'ala, kuma irin wannan haɗuwa takan sanya a yi zumunci, sannan kusantar juna shi ke kawo fahimta da rage saɓani, sannan ya ci gaba da cewa irin wannan taro ba ɓoyayyen abu bane, domin tun bayan juyin-juya halin Musulunci a ƙasad Iran, Imam Khomaini (QS) ya assasa irin wannan, wanda ake gayyatar musulmi masu fahimta daban-daban daga nahiyoyi daban-daban domin a samu kusanci da fahimtar juna, haka a nan gida Najeriya ma, Jagoranmu Sayyid Zakzaky (H) tsawon shekaru ya assasa irin wannan, wanda ake gayyatar musulmi (malamai) daga firƙoƙi daban-daban a matakin ƙasa da garuruwa duka domin a samu haɗin kai, a ƙarshe ya ƙarƙare da bayyana cewa yana kyau mu riƙa yiwa juna adalci, a nan ya kawo ayoyi da suke magana dangane da hakan da sauran jawabai.
A ƙarshe Malam Sani shugaban alarammomi ne da kuma Malam Ɗanladi Mamman daga ɓangaren Ƙur'ani Zalla, s**a rufe taron da addu'a aka sallami al'umma.
Rahoto; Ali Al-Haidary Maraban Jos
—KD Media Forum
01/06/2026M
15/12/1447H