IDON GARI

IDON GARI IDON GARI Jarida ce ta Yanar Gizo mai dauke da sahihan Labarai masu inganci a Najeriya da sauran sass

Gidauniyar ABBA PANTAMI DATA FOUNDATION ta ziyarci gidan marayu na Al-Guh Foundation da ke cikin kwaryar jihar Gombe, in...
24/03/2025

Gidauniyar ABBA PANTAMI DATA FOUNDATION ta ziyarci gidan marayu na Al-Guh Foundation da ke cikin kwaryar jihar Gombe, inda ta taimakawa marayu da kayan abinci duba da halin maraicin da suke ciki na rashin iyaye.

Yanzu haka Datar MTN SME tana tafiya Successfully a cikin Application din ABBA PANTAMI DATA LTD. Kamfanin MTN sunyi susp...
15/03/2025

Yanzu haka Datar MTN SME tana tafiya Successfully a cikin Application din ABBA PANTAMI DATA LTD.

Kamfanin MTN sunyi suspended din Datar MTN SME har sabuwar da s**a kawo shiyasa ta kare a kasuwa masu ita kuma sun zabga mata kudi da kyar ake samota wurin mutanen kudu shiyasa za kuga ba kowane Application din Data bane za kuga Datar SME a yanzu ba, karshe dole kowa ya koma siyan MTN GIFTING kafin su sake kawo wata sabuwar Datar tasu.

Yanzu haka Datar MTN SME tana tafiya a cikin Application din ABBA PANTAMI DATA LTD, itama MTN GIFTING 1GB Naira 355 tana tafiya Successfully.

Duk wanda SME ta mishi tsada sai ya sayi MTN GIFTING.

Kuyi Download din Application din ABBA PANTAMI DATA ta wannan link din a PlayStore
👇👇
https://play.google.com/store/apps/details?id=ng.com.abbapantamidata.app

Mai bukatan karin bayani, ya tuntubi daya daga cikin customer care ta WhatsApp;
09138275183
08126081967
07046868000
07061347599.

WATA SABUWA: Akwai Lauje Cikin Nadi A Tafiyar Matasa A NigeriaDaga Muhammad Chigari kumoWani matashi dan jihar Jigawa Ac...
16/02/2025

WATA SABUWA: Akwai Lauje Cikin Nadi A Tafiyar Matasa A Nigeria

Daga Muhammad Chigari kumo

Wani matashi dan jihar Jigawa Activitist Isma'eel S Jauro, ya zargi shugabanin Tafiyar matasa da nada wasu mutane da basa cikin tafiyar tun farkon farawa kamar yadda ya wallafa a shafin sa na sada zumunta.

Matashi ya ce, "Wannan tafiyar Matasan reshen Jihar Jigawa waÉ—anda suke cikin tafiyar kuma ake tattauna lamuran tafiyar dabam, daga bisani kuma a kawo wasu daga jihar kano aka naÉ—a su Shugabancin tafiyar".

Ya kara da cewa, "Ina cikin group na WhatssApp na tafiyar an tattuna akan cewa ranar 18/2/2025 za'a yi Meeting ido-da-ido a nan cikin garin Dutse dake jihar, katsam sai naga Abba Hikima ya wallafa a Facebook wai har sun zo Dutse an gudanar da zaɓen ba tare da mun sani ba"

Shin ya kuke kallon Tafiyar zuwa yanzu da aka fara zaban shugabanin jahohi ko kun gansu da zaɓen a jahohin ku ?

Shugaban kamfanin ABBA PANTAMI DATA ya ziyarci Majidadin Daular Usmaniyya Professor Sheikh Isa Ali Pantami  A jiya Larab...
07/11/2024

Shugaban kamfanin ABBA PANTAMI DATA ya ziyarci Majidadin Daular Usmaniyya Professor Sheikh Isa Ali Pantami

A jiya Laraba shugaban kamfanin ABBA PANTAMI DATA ya ziyarci tsohon ministan sadarwa na Najeriya Professor Sheikh Isa Ali Ibrahim Pantami kuma Majidadin Daular Usmaniyya.

A yayin ziyarar Comr Abba Pantami, ya baiwa Majidadin Daular Usmaniyya katin gayyatar daurin Aurensa wanda za'a gudanar a ranar 7 ga watan December a jihar Gombe, ya kuma tayashi murnar nadin babbar Sarauta da mai alfarma Sarkin Musulmi ya mishi na Majidadin Daular Usmaniyya.

Haka zalika Shehin Malamin ya bawa Comr Abba Pantami, kyautar shahararran littafinshi mai suna "Skills Rather than Just Degrees". Sunyi doguwar tattaunawa mai muhimmanci tare da Shehin Malamin na cigaban matasa da sauransu.

GAYYATAR DAURIN AURENA    Ina mai farin cikin gayyatar dukkannin 'yan uwa da abokanan arziki zuwa daurin Aurena da Ummuk...
21/10/2024

GAYYATAR DAURIN AURENA

Ina mai farin cikin gayyatar dukkannin 'yan uwa da abokanan arziki zuwa daurin Aurena da Ummukulthum Usman Hayatu, wanda In Sha Allahu za'a gudanar a ranar 07 ga watan December, 2024, a karamar hukumar Dukku dake jihar Gombe. Wa 'yanda ba zasu samu damar halarta ba muna bukatan Addu'o'insu.

Ga masu kira da tambayoyi game da zuwansu daurin Auran, In Sha Allah, akwai kwamitin tarbar baki da za muyi wanda zai kula da bangaren bakin da s**a zo daga nesa cikin kwaryar birnin Gombe zasu sauka, zamu fitar da kwamitin da zaran lokacin bikin ya karato.

Ga wa 'yanda suke son suyi anko Sky Blue ce, kowa in yana so zai iya siya ya dinka a garin da yake.

Sannan ina mai bawa kowa da kowa hakuri, bazan iya bin kowa ta Private na tura mishi Invitation ba abun da yawa. Ina mai rokon kowa da ya karbi wannan sanarwar a matsayin katin gayyata na musamman.


Ƙungiyar Arewa Media Writers Ta Halarci Taron Wayar Da Kan Al'umma Da Gamayyar Kungiyoyin Arewacin Najeriya Ta Shirya A ...
13/10/2024

Ƙungiyar Arewa Media Writers Ta Halarci Taron Wayar Da Kan Al'umma Da Gamayyar Kungiyoyin Arewacin Najeriya Ta Shirya A Jihar Katsina

Daga Kungiyar Arewa Media Writers

Ƙungiyar marubutan Arewa a kafofin sadarwar zamani "Arewa Media Writers" ƙarƙashin jagorancin shugaban ƙungiyar na ƙasa, Comr Haidar H. Hasheem, ta halarci taron wayar da kan al'umma a jihar Katsina. Taron na kwana guda an shirya shi ne ƙarƙashin gamayyar kungiyoyin arewacin Najeriya (Coalition of Northern Groups - CNG), wanda aka gudanar a jiya Asabar bisa jagorancin Shugaban kwamitin amintattu na CNG, Dr. Nastura Ashir Sharif.

Taron ya samu halartar shugabannin ƙungiyar a matakin jiha da kuma mambobi daga Katsina, inda aka samu wakilcin shugaban Arewa Media Writers na jihar Katsina, Comr Nura Siniya, tare da shugabannin ƙungiyar na jihar Katsina da sauran mambobi. Wannan taro na da muhimmanci wajen tattauna matsalolin tsaro da kuma yadda za a kare yara daga shan miyagun ƙwayoyi, musamman a yankin Arewacin Najeriya.

Shugaban ƙungiyar na ƙasa, Comr Haidar H. Hasheem, ya yi jawabi a wajen taron, inda ya nuna muhimmancin haɗin kai wajen magance matsalolin da suke addabar yankin Arewa. Ya kuma jaddada cewa, akwai buƙatar gwamnati da sauran masu ruwa da tsaki su haɗa hannu wajen kare martabar yankin ta hanyar magance matsalolin tsaro da shaye-shayen kayan maye.

A yayin taron, an gabatar da tattaunawa mai zurfi kan hanyoyin da za a bi domin ƙarfafa tsaron al'umma da kuma samar da shawarwari akan dabaru da za su taimaka wajen tsaftace rayuwar matasa da kare su daga faɗawa cikin haɗarin shaye-shaye. Haka kuma an yi kira ga iyaye da su yi amfani da damar wajen kula da tarbiyyar 'ya'yansu.

A ƙarshe, Comr Haidar H. Hasheem, ya buƙaci mambobin ƙungiyar da al’umma baki ɗaya su ci gaba da bayar da goyon baya domin samun nasarar burin da aka sanya a gaba na inganta tsaro da walwalar al’umma.

Arewa Media Writers na bukatar addu'oinku domin ganin ta sauke babban aikin da ta É—auka a wannan lokaci.

Ƙungiyar Arewa Media Writers Ta Kasa Ta Ziyarci Shugabannin Kungiyar Reshen Jihar Katsina Domin Tattaunawa Kan Inganta A...
12/10/2024

Ƙungiyar Arewa Media Writers Ta Kasa Ta Ziyarci Shugabannin Kungiyar Reshen Jihar Katsina Domin Tattaunawa Kan Inganta Ayyukan Kungiyar.

Daga Ƙungiyar Arewa Media Writers.

A wani rangadi na zagayen jihohin Arewa 20 har da babban birnin tarayya Abuja, sabon shugaban ƙungiyar marubutan Arewa a kafofin sada zumunta na zamani wato "Arewa Media Writers" na ƙasa, Comr Haidar H. Hasheem, ya jagoranci wata muhimmiya ziyarar rangadi zuwa jihar Katsina ranar Juma'a 11 ga watan Oktoba shekarar 2024, inda ya gana da shugabannin kungiyar reshen jihar da wasu mambobi na ƙungiyar.

Wannan taro na musamman ya samu halartar manyan shugabannin kungiyar Arewa Media Writers reshen jihar Katsina tare bisa jagorancin shugaban ƙungiyar a jihar Katsina Comr Nura Siniya, wanda s**a tarbi sabon shugaban ƙungiyar na ƙasa Comrd Haidar H. Hasheem da tawagarsa.

Manufar wannan taro ita ce farfaɗo da shugabancin kungiyar a jihar Katsina, da kuma farfaɗo da ayyukan ƙungiyar a jihar. Shugabannin ƙasa da na jihar sun tattauna batutuwa masu muhimmanci kan yadda za'a inganta ƙungiyar, ta hanyar rubuce-rubuce da zasu taimaka wajen inganta yankin Arewa baki ɗaya.

A yayin da yake jawabi, Shugaban kungiyar na ƙasa, Comr Haidar H. Hasheem, ya nuna farin cikinsa game da yadda shugabannin na jihar Katsina s**a yiwa wajen ciyar farin ɗango,Mahalartan sun matukar nuna ƙwazo sun kuma nuna a shirye suke don aiki tuƙuru wa ƙungiyar. Haidar ya jaddada cewa haɗin kai da aiki tare sune kaɗai zasu taimaka wajen cimma burin ƙungiyar, tare da tabbatar da cewa za'a yi aiki tukuru don amfanar da ƙungiyar baki ɗaya.

Shugabannin sun yi nazari kan yadda za a tabbatar da cewa ƙungiyar ta cigaba da kasancewa cikin tsari, tare da yin amfani da rubuce-rubuce wajen haɓaka ilimi da kuma wayar da kai a yankin Arewa. Haka kuma an tattauna dabaru na zamani da zasu taimaka wajen isar da saƙonni ga al'umma cikin ingantacciyar hanya don kiyaye yaɗa labarin ƙanzon-kurege cikin al'umma.

Bayan kammala jawabin Shugaban ƙungiyar, an b

Anyi Bikin Ranan Fulani ta Duniya A Jahar Gombe" A yau cikin ikon Allah akayi bikin ranar fulani a jihar Gombe kamar yad...
12/10/2024

Anyi Bikin Ranan Fulani ta Duniya A Jahar Gombe"

A yau cikin ikon Allah akayi bikin ranar fulani a jihar Gombe kamar yadda aka tsara a fadin Nigeria baki daya.

Jihar Gombe tana cikin jahohi da ake alfahari da yaren fulani da sauran yaruka wanda haka ya nuna akwai hadin kai da zaman lafiya a wannan jiha namu na Gombe.

Alhamdulillah, taron ya samu halartan manyan mutane sarakuna iyayen kasa tareda jami'an tsaro.

An kuma yi dukkan wasa na Al'adu na fulani kamar Rawan fulani, Koroso da sauran dukkan abubuwa na fulani.

Muna Addu'a Allah ya kara zaman lafiya a jihar Gombe.

Daga Muhammad Chigari kumo

Don Allah duk wanda ba shida account number cikin Application din ABBA PANTAMI DATA, ya shiga wurin ADD MONEY yanzu haka...
12/10/2024

Don Allah duk wanda ba shida account number cikin Application din ABBA PANTAMI DATA, ya shiga wurin ADD MONEY yanzu haka za'a bashi Permanent Account Number wadda da zaran ya tura kudi kai tsaye zata dinga shiga wallet dinshi.

Ga *Doctor X* ga wadanda basu fara ba, backed by ION 👇https://doctorx.meme/Follow the link, download the app and use my ...
09/10/2024

Ga *Doctor X* ga wadanda basu fara ba, backed by ION 👇

https://doctorx.meme/

Follow the link, download the app and use my referral code 👇

Gombawa

An nada Alh. Auwal Muhammad Kala (WAKILIN GABAS BARUNDE)Babban Digacin na Barunde Alhaji Sulaiman Muhammad Atiku, ya bay...
07/10/2024

An nada Alh. Auwal Muhammad Kala (WAKILIN GABAS BARUNDE)

Babban Digacin na Barunde Alhaji Sulaiman Muhammad Atiku, ya bayyana hakan ne a yayin da ya tura tawaga mai karfī zuwa gidan Alh. Auwal Muhammad Kala domin tabbatar mar da wannan sarautar ta WAKILIN GABAS BARUNDE

Nadin Hagalaren yabiyo bayan jajircewan Alh. Auwal kala tare da bayar da gudunmawa da goyon baya wajen cigaban na Barunde musamman wajen yada taimakawa Al'ummar yankin.

Daga muhammad Chigari kumo

Gombe Class Teacher Supports Maiduguri Flood Victims By Sa'ad Abubakar, KumoA Teacher working with Akko Local Education ...
29/09/2024

Gombe Class Teacher Supports Maiduguri Flood Victims

By Sa'ad Abubakar, Kumo

A Teacher working with Akko Local Education Authority in Gombe State Malam Shagari Mu'azu has expressed his intention to donate relief materials to victims of flood in Maiduguri, Borno State.

Shagari Mu'azu, made the commitment known while expressing sympathy with the victims of the unfortunate situation which put many households in difficult situations.

He added that "Their condition is worrisome considering the economic hardship being experienced, I therefore decided to contribute the little I have to encourage those with low source of income not to hesitate in giving out to those in need".

Shagari applauded the Borno State Governor Babagana Umara Zulum for his timely response to the plights of the victims.

He equally appreciated the Chairman Northern States Governors Forum and Gombe State Governor Muhammadu lnuwa Yahaya for the donation of one hundred million Naira as relief to the victims.

The items to be donated include spaghetti and cooking oil.

Address

Kaduna State

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when IDON GARI posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to IDON GARI:

Share