Azzahara tv News 24

  • Home
  • Azzahara tv News 24

Azzahara tv News 24 Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from Azzahara tv News 24, TV Channel, .

A wanann Shekara mata da s**a fita sallar Idi Sunfi mazan a wasu masallatan idi anan Katsina  sai Nace a iya binceke na,...
31/03/2025

A wanann Shekara mata da s**a fita sallar
Idi Sunfi mazan a wasu masallatan idi anan Katsina sai Nace a iya binceke na, sai nake tunai
Ina masu ce mana masu addinin da mata? wato A Hankali Ahankali Aikin mujadaddi nata ratsa Al'umma tabbas Hakin mata da aka taushe yana gab da Rushewa wani ma abu daya birge ni bayan na dawo idi sai na biya maƙabarta ziyara To a nan naci karo da motoci sai naga iyalai ne daban- daban suma daga salla idi s**a biyo makabarta domin ziyarar mamatansu na ce Allah kara ma Sayyid Zakzakiy( H) Lafiya
.

29/03/2025

Ba ke zuwa duba wata ba, Mune zamu gani Mu sanar da Su Yan Uwa.
Kar kace wai Kana jira, kaima Jiran ka Ake.

Muzaharar Quds na cigaba da gudana lafiya a garuruwan:SOKOTOBAUCHIJOSPOTISKUMMASHI, Jihar Katsina.9:30am28/3/2025 — Hurr...
28/03/2025

Muzaharar Quds na cigaba da gudana lafiya a garuruwan:

SOKOTO
BAUCHI
JOS
POTISKUM
MASHI, Jihar Katsina.

9:30am
28/3/2025

— Hurrasul Harakatil Islamiyya


LABARI MAI SOSA ZUCIYA!😢😭Wata baiwar Allah ce take tambayar wani malami neman mafita akan wani abu wanda ke damunta ga l...
27/03/2025

LABARI MAI SOSA ZUCIYA!😢😭

Wata baiwar Allah ce take tambayar wani malami neman mafita akan wani abu wanda ke damunta ga labarin k**ar haka:---👇

Dan Allah malam inason ayimin addu'a wallahi nida mijina mun kasance muna son juna har takai ga mukayi aure. bayan munyi aure sai mijin nawa Allah ya jarabeshi da samun matsaloli a fannin kasuwanci sa, dakuma sauran al'ummaransa.

nantake ya alakantani da wannan matsalar data sameshi har yake ikirarin cewa aiduk waɗannan matsalolin da yake ciki nice sila, domin ai kafin ya aureni ba haka yake ba a dalilin hakan nema harma ya sakeni,😢

nakoma gidanmu, kuma gashi inada juna biyu kusan wata bakwai 7 baya bani kulawa ga kuma gidan banada mahaifiya aciki domin Allah yayi mata rasuwa kuma banajin daɗin gidan. hakan taƙare bayanin ta cikin kuka😰 da ban tausayi.

daga ƙarshe take cewa dan Allah malam ataimaka min da addu'ar Allah ya daidaita tsakanin mu nida mijina yadawo gareni. Allahu Akbar

Dan Allah ƴan uwa maza mudaina azabtar mata yenmu akan ƙaddarar da Allah ya jarabemu da ita domin dukkanin musulmi sai ya yadda da ƙaddara ta alkhairi ko sharri sannan zai kasance cikakken musulmi mutuna cewa su mata tamkar iyayene, 'ƴaƴa, dakuma ƙanne agaremu sannan su tamkar amanace agaremu kuma Allah zai tambaye mu akan amanar daya bamu akansu sannan Babu Mai azurtawa ko talautawa sai Allah.

Allah ya ganar damu gaskiya yakuma bamu ikon amfani da ita a inda yadace amin.

Aminu Kano

Kissar Yajuj da Majuj (Gog da Magog)Tushen LabariLabarin Yajuj da Majuj yana cikin Al-Qur’ani a Suratul Kahf (18:94-98) ...
27/03/2025

Kissar Yajuj da Majuj (Gog da Magog)

Tushen Labari

Labarin Yajuj da Majuj yana cikin Al-Qur’ani a Suratul Kahf (18:94-98) da Suratul Anbiya (21:96-97). Hakanan yana cikin Hadisan Annabi (SAW) da littattafan tarihi.

Wanene Yajuj da Majuj?

Su gaggan mutane ne, masu barna da fasadi a duniya Kuma sun kasance babban fitina a duniya tun zamanin da, Dhul Qarnain, wani sarki adali, ya gina katanga mai ƙarfi don hana su fitowa A ƙarshen duniya kuma za su samu hanyar fita, su bazama cikin duniya suna lalata ta.

Cikakken Kisah

1️⃣ Dhul Qarnain da Katangar Yajuj da Majuj

A zamanin Dhul Qarnain, mutane sun koka masa cewa Yajuj da Majuj suna fitowa suna lalata musu ƙasa. Sai s**a roƙe shi ya gina katanga don hana su. Dhul Qarnain ya tara ** ƙarfe da tagulla**, ya dumama su ya haɗa su, har sai da s**a zama katanga mai ƙarfi sosai.

Ya gaya musu cewa "Lokacin da Allah ya so, wannan katanga zai karye, kuma za su fita."

2️⃣ Yajuj da Majuj Za Su Fito A Karshen Duniya

Annabi (SAW) ya ce, kullum Yajuj da Majuj suna kokarin huda wannan katanga, amma sai su ce "Gobe za mu kammala!" Amma ba sa cewa ‘Insha Allah’, shi yasa sai Allah ya dawo da katangar yadda take kowace rana. Lokacin da Allah ya nufa su fita, sai su ce "Gobe za mu kammala Insha Allah!", sai su samu katangar a lalace, su fito duniya.

3️⃣ Barna Da Za Su Yi

Idan s**a fito, za su cika duniya da barna, su kashe mutane da dabbobi, Za su sha ruwayen duniya gaba ɗaya Za su harba kayayyakinsu zuwa sama, kuma Allah zai maida su k**ar sun buge wani abu a sararin samaniya.

4️⃣ Kisan Su Da Allah Zai Yi

Annabi Isa (AS) zai yi addu’a, Allah zai aika cuta da tsutsa da za ta kashe su duka a dare guda Za su zama gangar jiki a ƙasa, har sai da ƙasar za ta cika da ƙamshin mutuwa, Sai Allah ya aika da tsuntsaye su ɗauke gawarwakinsu, sannan ya yi ruwa mai ƙarfi don tsaftace ƙasa.

Darussan da Za a Koya

1. Duniya tana da iyaka, kuma Allah yana da iko akan komai.
2. Dole ne a kiyaye lalata da barna domin hukuncin Allah yana nan.
3. Allah ne ke da iko akan kowane abu, kuma Lokacin Ƙarshe zai zo da fitina masu girma.

Yajuj da Majuj fitina ce da za ta zo a ƙarshen duniya, kuma za su kasance alamar Ƙiyama. Sai dai Allah ya tanadi ƙarshensu da nasara ga musulmi.

Me kake tunani?

Aminu Kano

26/03/2025

Kafin kaga Mai kudi da mace 4 sai ka samu talaka 20 da mata hudu yaya 50
Me ya jawo haka?

SANARWAR RUFE TAFSEER...Insha Allah ana sanar da ’yan’uwa musulmi cewa gobe Laraba 26 ga watan Ramadan, 1446 (26/03/2025...
25/03/2025

SANARWAR RUFE TAFSEER...

Insha Allah ana sanar da ’yan’uwa musulmi cewa gobe Laraba 26 ga watan Ramadan, 1446 (26/03/2025) ne Sheikh Yakub Yahya Katsina zai yi Khatmar Tafseer din Alƙur’ani mai girma na watan Ramadan ɗin shekarar bana 1446/2025.

Kamar yadda aka saba a Muhallin Markazin ’yan’uwa musulmi almajiran Sayyid Zakzaky (H) na Da’irar Katsina da ke Kofar Marusa. Da misalin ƙarfe 4:30pm.

Allah Ya bada ikon halarta.

Allah Kuma ya maimaita mana na baɗin baɗaɗa cikin ƙoshin lafiya da yalwar arziƙi, Ya karbi sa’ayin da aka gabatar.




KIRISTOCI MASOYA SAIYIDA FATIMA(A) DAGA GARIN FATIMA A PORTUGALA Yammacin duniya tun shekaru 100  da s**a gabata, a wani...
22/03/2025

KIRISTOCI MASOYA SAIYIDA FATIMA(A) DAGA GARIN FATIMA A PORTUGAL

A Yammacin duniya tun shekaru 100 da s**a gabata, a wani gari da ayanzu ake kiran shi da suna Fatima, garin da yake shine daya tilo a fadin duniya da yake amsa sunan Fatima bintu Rasul(S) a kuma kasar Turai a tsakiyar Kiristoci. Akwai Cocin tafarkin Katolika da yawa da suke karba wannan sunan na masoyan Fatima(A) da aka fi sanin Cocin nasu da ma’abota Cocin da suna ( Our Lady Of Fatima ), harma da karsarmu Nijeriya akwai wadannan masoyan na Saiyida Fatima(A) daga Kiristoci dubabbani masu yawa.

KISSAS LABARIN SU A TAKAICE:
Sun ce Mala’i ka ko kuma Saiyida Maryam Al Azra’u (Virgo) Alaihas salaam. Ta baiyana cikin sifar haske mai k**a da hasken rana a garin Vatican. Musulman Andalus (Spain) suna kiranta da sunan Cofa Da Iria Fatima domin girmamawarsu ga Saiyida Fatima Azzahara’ Alaihas Salam. Mabiya irin wadannan Cocin wasunsu sun ce wai, Saiyida Maryam Al Azra’ (Virgo) alaihas salam, ta zabi Garin na Portugal domin baiyana domin isar da wasu bayanai na girmamawa ga addinin Musulunci da kuma danta Annabi Muhammad (S) Annabin Musulunci. A zahirin gaskiya Fatima ce ‘yar Annabi Muhammad(S) ta baiyana ba Maryam Mukaddasa ba.
Saiyida (A) ta baiyana masu a cikin irin wannan sifar ne har sau shida (6).Tana baiyana ne a gaban wasu yara kirista masu kiwon Awaki a bayan Gari. Kamar yanda Annabi Isa (A) yake yi a lokacin rayuwarsa a wannan duniyar. Wadannan yaran ana kiransu ( Lucia Santos, Jacinta, Francisco Marto ). Baiyanar nata yakan kasance sau daya ne a wata kuma a ranar 13 ga wata. Baiyanar farko ya kasance a irin ranar Haihuwar Saiyid Fatima Azzahra (A) da ya dace da a ranar Juma’a 13/5/1917, 20/21/6/1335. A lokacin wannan baiyanar ya kasance ta koya ma wadannan Yaran 3 yanda ake Yin Sallah da kuma Addu’a.
Abinda yafi shahara a cikin lamarin nata shine ya kasance a ranar Juma’a 13/7/1917 = 23/24/9/1335, ta sanar da su wasu labarai guda 3 da ba makawa zasu tabbata. Amma babu inganci akan ruwayoyin da s**a fito daga Yaran nan 3 dangane da zantukan da suaka ruwaito. Saiyida (A) ta bukaci babban taron gangami a ranar baiyanarta na karshe a ranar 13/10/1917 = 27/12/1335, domin ta nunan masu aya daga ayoyin Allah Ta’ala.
A wannan ranar na Asabat 13/10/1917 = 27/12/1335 sama da Mutum Dubu 70,000 ne s**a halarci wannan taron, wannan ranar an wayi gari da ruwan sama k**ar da bakin kwarya. Amma a take alokacin baiyanar nata (A) ruwan ya dauke giza-gizai s**a dare domin Hasken rana ya sami fitowa, akarshe Mutane a wannan ranan sunga taurari da rana tsaka da hasken su cikin launin haskensu.
Alokacin da yaran s**a fara ganin ta a cikin madaukakin haske mai ban sha’awa, hasken day a dusashe hasken rana. Sai Saiyida Fatima (A) take cewa da wadannan yaran “ Kar kuji tsoro bana zo bane domin na tsorata ku”
Yaran sun tambaye ta “ Ke wacece? “
Saiyida Fatima ta amsa masu da cewa; “ Nice Fatima ‘yar Annabi Muhammda “
Sun kara tambaya s**a ce: “ Daga ina kika zo nan? ‘
Fatima (A) tace “ Nazo ne daga Aljanna “
Yaran sun sake tambaya “ Me kika zo yi a wurinmu? “
Saiyida Fatima ma’abuciyar tasbihi ta gaya masu cewa: Na baiyana ne a gareku a karon farko a yanzu, anan gab azan gaya maku abin da yakawo ni wurinku. A baiyanarta na karshe a ranar Asabat 13/10/1917 da sanar dasu sakon da tazo dashi.

Wani Muhimmanci wannan Labarin yake dashi da kuma alakarsa ga mu Musulmai??! Abin lura anan shine;

Da farko dai baiyanarta a ranar Juma’a 13/7/1917 ya kasance a irin ranar Lailatul Qadr watau ranar 23/9/1335. Kuma a irin wannan ranar ce na 23/Ramadan za ayi shelar baiyanar Imam Mahdi (A). Sannan baiyanar Aya ya kasance ne a ranar Asabat 13/10/1917 da yayi daidai da ranar 27/12/1335H.
Labarin farko na baiyanar ita Saiyida (A) an nuna cewa ta Nuna masu Jahannama, sannan ta nuna masu cewa mafiya yawan Mutane da Aljanu za a kona su a cikinta.Labari na biyu kuwa, an nuna cewa ta baiyana masu cewa yakin duniya na farko yana gab da ya kare. Sai dai kuma in har Kasar Rasha (Soviat) bata rungumi addinin Allah ba wani yakin da yafi wannan zai sake aukuwa. Bayan nan da ‘yan watanni sai yakin duniya na farko ya kare. Bayannan kuma sai yakin duniya na biyu ya auku.
Sannan Labari na uku an nuna cewa masana ilimin Falaki sun boye shi har ya zuwa wasu shekaru nan gaba. Duk da cewa akwai shakku a cikin ingancin maganganun. Da ake yadawar. Sai dai akwai nuni da cewa Mala’ikan Haske ( Tauraruwa mai Wutsiya, wasu kuma na ganin cewa Missale ne ), zai kona kusan dukkan duniya. Muna neman Tuba a gareka Ya Allah. Mutane za su shiga halin Yaki za a yaki mabiya Addinin Kiristanci za kuma a karya Kuros a lokacin faruwar hakan cikin bazata. Saidai Saiyida alaihas salam, zata kiyaye Masu Imani a wannan Lokacin. An ce ana sa ran faruwar wannan lokacin ne bayan shekara 100 daga Tarihin baiyanar ta Sayida (A).

Bayan amsar rantsuwa da kwana bakwai a Matsayin ta na Mataimakiyar Shugaban Majialisar Matasan ta NYCN a jihar Katsina A...
17/03/2025

Bayan amsar rantsuwa da kwana bakwai a Matsayin ta na Mataimakiyar Shugaban Majialisar Matasan ta NYCN a jihar Katsina Amb. Khadija Sulaiman Saulawa ta k**a aiki.

A kokarin ta da cika alkawurran data dauka a lokacin yakin neman zaben yar takarar shugabancin kungiyar Matasa ta NYCN. Khadija Saulawa ta fara ziyartar kungiyoyin matasa na bangororin addinin da mallaman jihar Katsina don neman hadin gwiwa da fiddo da hanyoyin ciyar da matasan jihar Katsina gaba.

Mataimakiyar shugabancin NYCN wacce kuma itace ofishin ta keda hakkin kula da bangaren mata da kuma masu bukata ta musamman ta kai ziyarar girmamawa da neman hadin gwiwa wajen matasan shi'a karkashin jagorancin Shugaban Shi'a na jihar Katsina watau Sheikh Yakubu Yahya Katsina inda ta samu kyakykyawar tarba daga shehin Mallamin da iyalan sa da kuma mukarraban shi.

Bayan tabbatar da makasudin wannan ziyara mallamin ya sha alwashin bayar da shawarar data dace dakuma dukkanin goyon baya ga Khadija Sulaiman Saulawa wajen ganin ta cimma muradun wannan kujera data samu musamman kan bangaren da ya shafi inda suke iya tsoma baki.
Sheikh Yakubu Yahya kuma yayi mata nasiha mai tsawo tare da jawo hankali da nusar da ita akan muhimmaci dakuma darajar da Allah Ya baiwa mace tun kafin wani abu wai shi Human rights da yace ba gaskiya bane yaki da akidar musulunchi ne, inda yace babu wani abu a Duniya daya daga darajar mace yake kallon ta a matsayin sarauniya sai musulunchi.

Haka kuma tawagar ta kai ziyara ga Churchin Catolica don ganawa da matasan kiristochi ta yanda zata tafi tare da su wajen ciyar da kowane matashin jihar Katsina gaba, suma sun nuna matukar jin dadin su inda s**a ce irin wannan ziyara ta wannan matashiya itace ta farko a tarihin su don haka sun jinjnawa Amb. Khadija Saulawa tare da alkawarin bata dukkanin goyon baya

Daga karshe queen da tawagar ta sun yi godiya ga Sheikh Yakubu Yahya Katsina da jama'ar sa tare addu'oin fatan alkhairi.

Yau Shekara 108 da bayyana Sayyada Zahara (As)  a Kasar potugal. Yayin da Sayyada (As) ke Safkowa daga Sama Acikin Haske...
12/03/2025

Yau Shekara 108 da bayyana Sayyada Zahara (As) a Kasar potugal.

Yayin da Sayyada (As) ke Safkowa daga Sama Acikin Haske.

Lucia Santos, Jacinta, da Francisco Marto ). Ƴara masu kiwon Awaki dake a Vatican ta kasar Potugal, Sai S**a Nemi Su Ruga da Gudu

Sai Saiyida Fatima (A) take cewa da wadannan yaran “ Kar kuji tsoro bana zo bane domin na tsorata ku”

Yaran s**a tambaye ta “ Ke wacece? “
Saiyida Fatima ta amsa masu da cewa; “ Nice Fatima ‘yar Annabi Muhammda “

Sun kara tambaya s**a ce: “ Daga ina kika zo nan? ‘

Fatima (A) tace “ Nazo ne daga Aljanna “

Yaran sun sake tambaya “ Sayyada Fatima (As) Me kika zo yi a wurinmu? “
Saiyida Fatima ma’abuciyar tasbihi ta gaya masu cewa: Na baiyana ne a gareku a karon farko a yanzu, anan gaba zan gaya maku abin da yakawo ni wurinku. A baiyanarta na karshe a ranar Asabat 13/10/1917 Sayyada ta sanar dasu sakon da tazo dashi.

Ci kake labarin Yana zuwa insha Allahu danjin Abinda ta faɗa masu. Barka mu da shan Ruwa.

Amincin Allah ya Tabbata a Gare ki ya sayyada Alawiyya (As)
Zahara

Yanzu yanzu Yau Litinin da misalin karfe  8 da mintina 3 agogon Najeriya, cikin kudurar Allah, wata zai tsaya daidai sai...
10/03/2025

Yanzu yanzu

Yau Litinin da misalin karfe 8 da mintina 3 agogon Najeriya, cikin kudurar Allah, wata zai tsaya daidai sai tin tsakiyar dakin ka'aba mai tsarki

In ka daga kanka sama a daidai lokacin, to wata na daidain tsakiyar dakin ka'aba dari bisa dari. alokacin zaka iyayin addu'a kasa bukatar ka Allah ya amsa mana.

Shafin Inside the Haramain ne ya wallafa labarin.

Address


Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Azzahara tv News 24 posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

  • Want your business to be the top-listed Media Company?

Share