AL IHWAN hausa

AL IHWAN hausa wannan shafin,an Samar da shine don isarwa alumma ingantattun labaru.

Yemen ta harba mak**ai masu linzami 3 kasar mamaya, bayan gurgunta tashar jiragen ruwa.Dakarun kasar Yemen sun yi lugude...
17/07/2025

Yemen ta harba mak**ai masu linzami 3 kasar mamaya, bayan gurgunta tashar jiragen ruwa.

Dakarun kasar Yemen sun yi luguden wuta da wani makami mai linzami da jirage marasa matuka guda hudu zuwa wasu wurare uku masu muhimmanci na kasar mamaya bayan tilasta wa gwamnatin kasar sanar da rufe daya daga cikin manyan tashoshin jiragen ruwa.17 Jul 25

Zaman makokin da Iyalan tsohon shugaban kasa marigayi Muhammadu Burahi keyi tareda matemakin shugaban kasa me ci Kashim ...
14/07/2025

Zaman makokin da Iyalan tsohon shugaban kasa marigayi Muhammadu Burahi keyi tareda matemakin shugaban kasa me ci Kashim Shattima a birning London.14 Jul 25

Wata majiyar ta ce, kasar lɍañ ta kori bakin haure Ƴan asalin kasar Afganistan mutum dubu ɗari uku da tamanin(380,000), ...
03/07/2025

Wata majiyar ta ce, kasar lɍañ ta kori bakin haure Ƴan asalin kasar Afganistan mutum dubu ɗari uku da tamanin(380,000), waɗanda s**a shigo kasar ta iyakar Dogharoom..

Mataimakin Gwamannan lardin Revazi Khorasan ya ce, na mayar da waɗannan bakin hauren inda s**a fito cikin mutunci da girmamawa.

Kasar lɍañ dai ta fuskanci matsalar rashin tsaro daga cikin gida sak**akon kwararar bakin haure zuwa cikin kasarta, mafi yawansu daga kasashen maƙota ne waɗanda yanayin Yaƙe-yake ya kore zuwa cen domin samun mafaka, amma sai dai da yawa daga cikinsu sun zama masu yi makiyan aikin leken asiri, kuma su ne s**a rika hare-hare cikin kasar da bama-bamai.

Zuwa yanzu lɍañ ta k**a Ƴan leken asiri akan a kalla sama da mutum 3000, wasu ta yanke musu hukuncin kisa ta hanyar rataya, wasu na zaman jiran hukunci.

A. Abubakar

Bayanin Hukumar Tsaron Ƙasa ta Iran kan farmakin sansanin sojin Amurka a Qatar: Harin da aka kai kan sansanin sojin Al U...
23/06/2025

Bayanin Hukumar Tsaron Ƙasa ta Iran kan farmakin sansanin sojin Amurka a Qatar:

Harin da aka kai kan sansanin sojin Al Udeid da ke Qatar wata martani ne da ta shafi tsarin ramuwar gayya bisa doka, kuma ya yi daidai da dokar ƙasa da ƙasa da kuma haƙƙin kare kai cikin halasci.

Dakarunmu sun aiwatar da aikin harin makami cikin nasara, inda s**a kai hari kan sansanin sojin Amurka na Al Udeid — ɗaya daga cikin manyan sansanonin sojin Amurka a yankin.

Adadin mak**an da aka yi amfani da su ya yi daidai da yawan bom da Amurka ta yi amfani da su a harin da ta kai kan cibiyoyin nukiliya na Iran.

Wurin da aka kai harin soja yana nesa da yankunan zama da birane a cikin ƙasar Qatar.

Aikin ba ya da wata barazana ga ƴan uwanmu mutanen Qatar, kuma ba zai haifar da wata matsala ba ga tsaron ƙasar Qatar.

Sannan muna jaddada alaƙar mu mai cike da tarihi da ke tsakaninmu da ƙasar Qatar, kuma wannan martani bai zai rusa wannan ba — kuma ba zai taɓa lalata wannan dangantaka ba. Sai dai martani ne da ya ƙunshi kare mutuncin ƙasa da martabar ƙasa.

kwana uku kafun Amurka ta kaiwa manyan tashoshin Nukilyar Iran hari,an hangi treloli fiye da 20 sun yi ayari a kofar waj...
22/06/2025

kwana uku kafun Amurka ta kaiwa manyan tashoshin Nukilyar Iran hari,an hangi treloli fiye da 20 sun yi ayari a kofar wajen.

hakan nanuna cewa,Iran ta kwashe muhimman kayyakin ta daga wajen kafin wannan hari "na borin kunya" da Amurka ta kai a daren jiya.

mutuwa ga amurka da izraila

Ga sanarwar da Dakarun Ali s**a s**a fita yau da Asuba. lɍan ta yi amfani da makamin Milinzayil na Fattah-1 a karon fark...
18/06/2025

Ga sanarwar da Dakarun Ali s**a s**a fita yau da Asuba.

lɍan ta yi amfani da makamin Milinzayil na Fattah-1 a karon farko. Rundunar Kare Daular Muslnc ta ce guguwar mikami na 11 ta hari gaskiya na 3, an gudanar da ita ne da makamin milinzayil na Fattah na farko (Fattah-1,).

A cikin sanarwar Dakarun sun bayyana cewa ce manufar harba wannan makami na Fatah-1 shi ne, domin su nuna wa kasar makiya cewa, wannan shi ne mataki na na karahe da za su iya kare kasarsu, wato farkon karshe na matakin kariya da sojojin Aladu za su iya yi domin kare kasarsu daga mak**aan lɍæn.

Makamin Milinzayin na Fattah mai karfin gaske a daren yau sun haddasa girgizar kasa a maboyar ‘yan kwacen kasa matsorata, bayan sun kutsa cikin garkuwar kariya ta makamin milinzayil.

Yadda aka nuna makamin ya keta tsaron lzɍal har shigaye goma sha bakwai (17), to wannan yana bayyana sakon karfin na lɍæn ne ga kasashen ƙawancen lzɍala da ke tunzura wannan yakin na Tallabibu. Dakarun sun ce karfin wannan makamin ya hasashe.

Dakarun sun ce, harin makami da s**a kai na daren yau ya tabbatar da cewa suna da karfi kuma da cikakken iko a kan mak**an kariya na sararin samaniyar yankunan da aka mamaye, kuma yadda makamin ya rika sauka a cikin kasar a daren jiya, ya nuna cewa yanzu makiya ba su da cikakken tsaro daga harin mak**an lɍañ.

Almujtabah Abubakar

JAGORA (H) YA GABATAR DA JAWABIN RANAR GHADEERDaga Ofishin Sayyid Ibraheem Zakzaky (H)Da yammacin Lahadi 18 ga Zulhijja,...
16/06/2025

JAGORA (H) YA GABATAR DA JAWABIN RANAR GHADEER

Daga Ofishin Sayyid Ibraheem Zakzaky (H)

Da yammacin Lahadi 18 ga Zulhijja, 1446 (15/6/2026), Jagoran Harkar Musulunci, Shaikh Ibraheem Zakzaky (H) ya gabatar da jawabin Ranar Idil Ghadeer a gidansa da ke Abuja,

Jagoran ya fara jawabi ne da godiya ga Allah Ta’ala dangane da sanya mu da ya yi a cikin masu Wilaya. Yace, ba shakka wannan yini ne mai muhimmanci. “An tambayi Imam Jafarus Sadiq (AS), baya ga Idodin nan biyu da kuma Juma’a, Musulmi na da wani Idi ne? Sai yace, kwarai kuwa, shi ne ma ya fi dukkansu, shi ne Idil Ghadeer. Yace Allah bai aiko wani Annabi ba daga cikin Annabawa face ya yi Idi da wannan Idin.”

Jagora yace, ba bisa hadari ba ne ya zama dukkan Annabawa sun saka ‘Ausiya’ dinsu a irin wannan rana ta Ghadeer, wato 18 ga Zulhijja. Yace, ba wani Annabi da ya taba zuwa da sako, ya tafi ya bar al’ummarsa wawai, ba tare da wanda zai cigaba da bayanin sakonsa a bayansa ba. “Wannan hankali ba zai dauka ba, ace Allah Ya aiko Annabi, ya shiryar da al’umma, har ma ya kafa daula, - ko da ma bai kafa daula ba, ballantana kuma ace ya kafa daula, - amma shikenan sai ya tafi ya bar su, yace ‘amrukum shura bainakum’, kawai sai su yi shawara su zabi wanda ya dama. Hankali ba zai yarda da wannan ba. Tunda dai shi Allah Ya aiko shi, kuma ya san abinda ya fi dacewa ga al’umma, to (dole) shi ne zai shiryar da su izuwa ga wannan abin.”

Jagora ya bayar da uzuri ga ‘yan uwa dangane da rashin yiwuwar gabatar da taron Ghadeer tare da shi a babban muhalli. Yace, hakan ya faru ne sak**akon takura mu da mahukuntan kasar nan, wadanda karnukan Sahayina ne s**a yi. Ya kuma karfafi cewa, a nemi jawaban da ya gabatar a shekarun baya wanda duk an sajjala su a kaset mai hoto da kuma na sauti. “Akwai Cibiyar Wallafa, sun saka karatuttukan da muka yi na baya, amma sauti ne, saboda haka ba bukatar mu yi ta maimaita abu guda.”

Shaikh Zakzaky ya bayyana cewa: “Mu muna magana da junanmu ne, ba muna yi da wasu ba ne, muna yi da Ahlul Wilay

Yadda Iran Ta Jefa Mak**ai Masu Linzami Kan Yankunan Da Isra’ila Ta Mamaye a FalasɗinuA cikin wani sabon salo na martani...
14/06/2025

Yadda Iran Ta Jefa Mak**ai Masu Linzami Kan Yankunan Da Isra’ila Ta Mamaye a Falasɗinu

A cikin wani sabon salo na martani, Iran ta kaddamar da jerin hare-haren mak**ai masu linzami a kan wurare da dama a cikin yankunan Falasɗinu da Isra’ila ta mamaye, inda hakan ya haifar da mummunan ɓarna da asarar rayuka, k**ar yadda rahotanni ciki harda na yammaci s**a tabbatar.

Wannan shi ne zagaye na uku na aikin soja na ramuwar gayya da Iran ta kira “Alƙawari Na Gaskiya III”, wanda ya fara da misalin ƙarfe 1:30 na safe agogon Iran, bayan hare-hare biyu na nasara da ta samu a baya wacce ta kai ga lalata wasu muhimman wuraren Isra’ila.

Rahotannin kafafen watsa labarai na Isra’ila sun bayyana cewa sabon zagayen hare-haren ya rutsa da yankuna irinsu Talabib, birnin da aka mamaye na al-Quds (birnin Urushalima), Tafkin Tiberias, Haifa, Beersheba da wasu wurare.

Mafi munin harin dai ya auku ne a Talabib, inda makami ɗaya ya faɗa a ginin bene mai hawa 50, wanda ya haddasa fashewa mai ƙarfi tare da hayaki mai yawa yana tasowa zuwa sararin samaniya.
Kafafen yada labarai na Isra’ila sun bayyana yanayin tashin hankali da rudani a Talabib, inda hukumomin bada agajin gaggawa ke daukar matakai bisa kiran da s**a bayyana a matsayin “muhimmin hari” a wani cibiyar aiki mai tsananin muhimmanci a kudancin birnin.

Saboda mahimmancin wurin da aka kai hari, hukumar “Home Front Command” ta Isra’ila ta sanya takunkumi kan yada wasu bayanai don guje wa ƙarin kunyata kasar.

Shugaban cibiyar nazari kan dabarun tsaro da hulɗar ƙasa da ƙasa, Amir Al-Mousawi, ya bayyana cewa ɗaya daga cikin mak**an Iran ya faɗa a cibiyar binciken nukiliya da ke Talabib.

Wasu rahotanni sun bayyana cewa ma’aikatar harkokin soja ta Isra’ila ma an sami nasarar kai mata hari. Rahotannin kafafen yada labarai na Isra’ila sun ce gwamnatin Isra’ila ta sanya takunkumi ga mazauna ƙasar, tana hana su wallafa hotuna ko bidiyon wuraren da aka kai hari.

Hukumomin Isra’ila na ci gaba da tantance barnar da aka yi musu da kuma aikin

Sheikh Ibraheem Zakzaky (H) yayi Magana akan Cigaba da tsare Sheikh Abduljabbar Nasiru Kabara.Da yake tsokaci dangane da...
14/05/2025

Sheikh Ibraheem Zakzaky (H) yayi Magana akan Cigaba da tsare Sheikh Abduljabbar Nasiru Kabara.

Da yake tsokaci dangane da tsare Shaikh Abduljabbar da mahukunta ke cigaba da yi har yanzu, Jagora Shaikh Ibraheem Zakzaky ya bayyana cewa: “Ba mu san wane ‘interest’ su mahukuntan yanzu suke da shi na rike shi har yanzu ba, don ba wani dalili na rike shi. Ganin cewa ‘case’ ne wanda babu yadda za a yi a mizanin hankali a tabbatar da shi.

“Wato mutum ne yake cewa, wannan hadisi an mai da Manzon Allah tamkar kaza kenan. Sai aka ce shi ya ce ma Manzon Allah kaza. Wai to ina kai ka samu wannan? Don yace, wannan ai k**ar an raina Annabi (S) ne, an maishe shi tamkar kaza… To sai aka ce, atafau wai shi ya dai wannan kalmar.”

Shaikh Zakzaky ya bayyana cewa, ko mutum ya yarda ko kar ya yarda, mahukunta na baya, sarakai, sun yi wasa da hadisin Annabi (S), sun sa an musu hadisai, kuma sun sa an jirkita musu hadisai, sun yi amfani da su don biyan bukatan kansu.”

Yace, mutane suna ganin k**ar tonowa da ake ace wannan Hadisin ba daidai ba ne, k**ar zai rusa musu addininsu ne. “Amma kuma lallai addinin nan ba zai tsaya ba, sai an tono wadannan abubuwan da suke ba daidai ba, an ce ba daidai ba ne, don a kare martaban Annabi (S).”

Bayan da ya kawo misalsalai masu yawa na yadda aka rika jirkitawa tare da kirkiran hadisan karya a baya, Shaikh Zakzaky ya bayyana cewa: “Irin wannan ne ya janyo wasu mutane s**a ce, kai ba ruwansu ma da Hadisan gabadaya tunda abin haka ne, s**a koma Alkur’anawa.” Yace: “To wallahi gara Bakur’ane sau dubu, da wanda zai karanta Hadisi yace iyayen Annabi (S) na wuta.”

Sayyid Ibraheem Yaqoub Zakzaky (H) a jiya Talata 13/05/2025

27/04/2025
ANYI JANA'IZAR MARIGAYI SHEIKH MAINASARA LIMAN  !Damisalin karfe 2:30 na ranar yau Lahadi  27 - 4-2025 ,  aka gabatar da...
27/04/2025

ANYI JANA'IZAR MARIGAYI SHEIKH MAINASARA LIMAN !

Damisalin karfe 2:30 na ranar yau Lahadi 27 - 4-2025 , aka gabatar da jana'izar Marigayi Sheikh Mai Nasara Liman Tudun Wadan Zariya , wanda Allah yayiwa rasuwa jiya Asabar a Asibiti bayan yayi fama da jinya...

Jana'izar wanda SHEIKH SALAHUDDEN IBRAHIM INYASS ya jagoranci dunbin al umma a filin Idin Mallawa dake Jos Road Kofar Doka Zaria .

Sarkin Zazzau Amb Malam Ahmad Nuhu Bamalli , Manyan manyan shehunan malamai shuwagani yan siyasa yan kasuwa daga sassa daban daban ne s**a halarta.

Muna addu'an Allah yajikanshi yasa Aljanna Makoma 🤲

AAqil Abdulkadir
27/4/2025.

26/04/2025

GWAMNATIN JOYLANI TA QADDAMAR DA HARI KAN QABILUN ALAWIT DAKE SURIYA.

Kafofin labaran cikin gida na $uriya, sun bada labarin cewa, jami'an tsaron gwamantin Ƴan Tawayen Kasar sun kai wani gagarumin farmakin kwamushe a birnin Hims, inda s**a k**ar gwamman matasan ƙabilun Alawit, k**ar yadda kamfanin labarin Almayadden s**a labarto.

Majiyoyin sun kara da cewa an samu gawarwakin mutane yawa na Kabilun alawit da Gwamantin Joylani ta sa aka k**a kwanakin baya aka tsare su, an gano gawarwakinsu a wani Asibiti, jikkunansu da alamu harbi, wanda ke nuna cewa bayan an k**a su da ransu, sai aka harbesu gaba ɗayansu an kashe su.

Sak**akon wannan farmakin kamun da jami'an tsaron gwamantin Ƴan tawayen $uriya s**a kai a birnin Homs, ya sanya wasu birnen zama cikin shirin ko ta kwana,

Almujtabah Abubakar

Address

Kaduna

Telephone

+2347067821832

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when AL IHWAN hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share