17/08/2025
MAZAN AURE A KAI ZUCIYA NESA
Wani magidanci dan shekaru 50 a garin Bama jihar Borno mai suna Modu Isah ya saki matarsa, daga bisani ya nemi ta dawo gidansa taki saboda ya mata saki har guda uku, shine ya dauki wu_ka ya dat$e azzakarinsa saboda bacin rai, ya kuma caka wu_kar a cik!nsa
Lamarin ya faru shekaran jiya juma'a, Matar mai suna Bayanze Modu, 'Yan sandan Bama sun dauki mutumin jina-jina s**a kai shi General Hospital Bama, sannan an mayar da case din zuwa State CID Maiduguri
Da ake tambayarsa dalilin aikata haka, yace shi yayi yunkurin ka$he kansa ne saboda yana kishin matar da ya sake domin ta iya kwanciyar aure, ya gwammace ya bar duniya akan ya rayu ya ga wani ya aureta, yace idan bai mutu ba to babu amfanin zaman azzakarinsa a jikinsa ba tare da tsohuwar matarsa da ya sake ba
'Yan uwa Magidanta mu dinga kai zukatan mu nesa, idan ka san zaka auri mace ka saketa daga baya kayi nadamar sakin don Allah kar kayi, Musulunci ma ya hana yin saki a cikin fushi duk saboda gudun nadama irin wannan
Na taba yin case din abokin wani abokina, ya auri wata mata da mijinta ya sake saki uku, sai ta dinga masa karya cewa zataje asibiti, ashe tsohon miji ne yake kiranta a waya tana fita suna haduwa, shine ya bani nambar wayan matar na bincika, na ganoshi har daidai gurin da yake zuwa yana daukarta, da inda yake kaita, aka je aka k**ashi, har gidan yari sai da ya tafi
A takaice wannan shawara ne da kuma darasi ga mazan da suke da ra'ayin sakin matansu na aure su dawo suna nadama
Allah Ya kiyaye
Daga Datti Assalafy