Hasmag TV.

Hasmag TV. Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from Hasmag TV., .

Hasmag Online TV Gidan Talabijin ne da zai dunga Kawo maku Sahihan labarai na gida Najeriya tare da kasashen ƙetare, haɗi da ilimantarwa faɗakarwa nishaɗantarwa ku tuntubemu a 09121774270 Domin bamu labarai kan halin da kuke ciki a yankunan ku

Maraba da Zuwa Shafin Hasmag TV  Ku Bibiyemu ta WhatsApp Channel Domin Samun Labarai da Dumi-Dumin SaFollow the HASMAG T...
10/01/2026

Maraba da Zuwa Shafin Hasmag TV Ku Bibiyemu ta WhatsApp Channel Domin Samun Labarai da Dumi-Dumin Sa

Follow the HASMAG TV channel on WhatsApp: https://whatsapp.com/channel/0029Vb7pygJEquiHaMEIZD2f

SUBHANALLAH: ’Yan bindiga sun sake kai mummunan hari a Borgu, Jihar Neja.

A daren Juma’a, 9 ga Janairu, 2026, wasu ’yan bindiga sun kai hari a ƙauyen Damala da ke yankin Wawa, cikin Ƙaramar Hukumar Borgu ta Jihar Neja. Harin ya faru ne tsakanin ƙarfe 8:00 zuwa 8:30 na dare.

Rahotanni daga mazauna yankin sun nuna cewa maharan sun kashe mutane huɗu, tare da kwashe dabbobin jama’a gaba ɗaya, s**a tura su cikin daji. Haka kuma sun ƙona coci guda ɗaya da gidaje da dama, lamarin da ya jawo asarar dukiya mai yawa tare da tilasta wa iyalai da dama tserewa daga gidajensu.

Shaidu sun ce an kai harin ne kwatsam, kuma babu jami’an tsaro a yankin a lokacin, abin da ya sa al’umma s**a rasa kariya. Ya zuwa lokacin fitar da wannan labari, babu wata sanarwa a hukumance daga hukumomin tsaro.

Mazauna Borgu da ƙauyukan da ke kewaye sun sake yin kira ga gwamnatocin jiha da tarayya da su gaggauta tura jami’an tsaro domin kare rayuka, dukiyoyi da wuraren ibada.

Hasmag TV

Maraba da Zuwa Shafin Hasmag TV  Ku Bibiyemu ta WhatsApp Channel Domin Samun Labarai da Dumi-Dumin SaFollow the HASMAG T...
10/01/2026

Maraba da Zuwa Shafin Hasmag TV Ku Bibiyemu ta WhatsApp Channel Domin Samun Labarai da Dumi-Dumin Sa

Follow the HASMAG TV channel on WhatsApp: https://whatsapp.com/channel/0029Vb7pygJEquiHaMEIZD2f

NANISS ta ƙi amincewa da buɗe wasu makarantu a Jihar Neja.

Ƙungiyar Ɗaliban Jihar Neja (NANISS) ta bayyana rashin amincewarta da buɗe wasu makarantu a jihar Neja, tana mai nuna damuwa kan batun tsaro da walwalar ɗalibai.

Ƙungiyar ta ce har yanzu ba a samar da isassun matakan tsaro ba, musamman a wasu yankuna da ke fama da matsalolin tsaro, lamarin da ka iya jefa rayukan ɗalibai da malamai cikin haɗari.

NANISS ta buƙaci gwamnatin jihar Neja da ta ɗauki matakan gaggawa domin tabbatar da tsaro kafin a buɗe makarantu gaba ɗaya..

Hasmag TV

Maraba da Zuwa Shafin Hasmag TV  Ku Bibiyemu ta WhatsApp Channel Domin Samun Labarai da Dumi-Dumin SaFollow the HASMAG T...
10/01/2026

Maraba da Zuwa Shafin Hasmag TV Ku Bibiyemu ta WhatsApp Channel Domin Samun Labarai da Dumi-Dumin Sa

Follow the HASMAG TV channel on WhatsApp: https://whatsapp.com/channel/0029Vb7pygJEquiHaMEIZD2f

A Madadin Shugaban Gudanarwa na Wannan Kafa Alh Anas Attah,Na Gayyatar Daukacin Al'umma Zuwa Wurin Daurin Auren 'Yan Uwan Sa,A Madadin Iyalan Marigayi Alhaji Attah Abdullahi (Rijau)
na gayyatar ku cikin girmamawa zuwa bikin
DAURIN AUREn ’ya’yansa kamar haka:

1.
Malam Abdulmumin Attah Abdullahi (Dan Islam) da Malama Firdausi Shaibu
Lokaci: 2:00 na rana
📍 Wuri: Sabon Gari, Kontagora

2.Alhaji Abbas Attah Abdullahi
da Umulkairi Muhammed
Lokaci: 11:00 na safe
📍 Wuri: Gidan Kafinta, Kontagora

3.Alhaji Abdullahi Attah Abdullahi
tare da Hafsat Nura Noma
🕝 Lokaci: 2:30 na rana
📍 Wuri: Gidan Sarkin Noma, kusa da Gidan Arah, Kontagora

Allah Ya ba da ikon halarta. Ameen. 🤲

Hasmag TV

10/01/2026
10/01/2026

Kungiyar Munazzamatul Fityanul Islam First Aid Kontagora Tayi Sabon Shugaba.

KUNGIYAR MUNNAZAMATUL FITYANUL ISLAM FIRTS AID GROUP KONTAGORA TA BAIWA DR. ABDULLAHI MUSA (CHAIRMAN) RESHEN KONTAGORA.

A yau Juma’a, 9 ga watan Janairu, 2026, Kungiyar Munnazamatul Fityanul Islam First Aid Group, reshen Kontagora, ta karrama Dr. Alhaji Abdullahi Musa. Shugaban (Chairman) reshen Kontagora, bisa kwarewarsa, jajircewa da gagarumar gudunmawar da yake bayarwa, musamman a fannin addini da hidimar al’umma.

An bayyana cewa kungiyar ta yanke shawarar ba Dr. Alhaji Abdullahi Musa wannan karramawa ne domin yaba masa kan irin himma, gaskiya da jajircewar da yake nunawa wajen tallafa wa harkokin addini, tarbiyya da cigaban al’umma a yankin Kontagora.

A yayin bikin karramawar, shugabannin kungiyar sun jaddada cewa Daraktan ya zama abin koyi ga matasa da shugabanni, duba da yadda yake riko da gaskiya, adalci da shugabanci nagari a dukkan al’amuransa.

Kungiyar ta kuma yi masa fatan alheri a wannan sabon mukami, tare da addu’ar Allah Madaukakin Sarki Ya ba shi ikon riko da adalci, hikima da nagarta, domin sauke nauyin da aka dora masa yadda ya dace.

A nasa bangaren, Dr. Alhaji Abdullahi Musa ya bayyana godiyarsa ga kungiyar bisa wannan karramawa, yana mai alkawarin ci gaba da aiki tukuru domin cigaban addini, zaman lafiya da walwalar al’umma baki daya.

Hasmag TV

08/01/2026

Sabuwar Dokar Haraji da Gwamnatin Tarayya Ta Amince dashi Abune da Ya Tsayawa Talakan Najeriya a Rai.

Hakan Yasa Shirin RA'AYI RIGA Ya Santa da Mal Musa Kwazo,Mai Sharhi Kan Al'amuran Yau da Kullum In da Ya Kara Mana Haske Kan Sabuwar Dokar Haraji.

Ku Kasance Damu da Misalin 8:00pm Don Kallon Shirin.

Hasmag TV

Address


Telephone

+2349121774270

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Hasmag TV. posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Hasmag TV.:

  • Want your business to be the top-listed Media Company?

Share