Fityanul islam media Zango

Fityanul islam media Zango Godiya ga Allah da ya raya mu, tsira da aminci su tabbata ga shugabanmu Annabi Muhammadu s.a.w Tare da Ahlinsa da Sahabbansa.

14/12/2023

Kudaina ajiye account number naku barkatai a ko ina a social media, duk da a iya sanina babu wata hanyar da za'a iya kwashe maku kudade ta sanin Account number naku kadai ba amma saboda tsare account din yanada kyau a kiyaye, Idan Hac-ker ya mallaki Account Number naka akwai wasu hanyoyi guda 4 da zai iya bi wurin yunƙurin kwashe maka kuɗi:

1. Social engineering attempts: Ta wannan hanyar hac-ker zai iya amfani da Account number naka wurin ƙoƙarin samun information naka daga wurinka ko daga wurin wasu makusantanka, misali: za iya kiranka a waya ya karanto maka Account Number naka daga farko har ƙarshe, sannan yace maka daga bankinka yake, dan haka yana buƙatar login credentials naka da wasu personal details, da duk wasu sensitive information naka na banki, da niyar cewa za'ayi maka wani gyara ne, kai kuma saboda ya karanto account number naka hakan sai yasa ka amince dashi kuma katura mashi.

Kai tsaye zaiyi amfani da wannan damar ya kwashe komai acikin asusun naka.

Note: Duk wanda ya kiraka a waya ya karanto maka Account Number naka yace maka ka bashi wani Login credentials naka, ka kashe wayarka kawai. idan banki s**a kiraka ce maka zasuyi kaje banki ayi maka duk abinda za'ayi maka acen.

2. Phishing attacks: Idan Hac-ker ya mallaki account number naka, zai iya amfani da wannan damar musamman idan yanada Email naka ko Phone number sai ya tura maka phishing emails ko message mai ɗauke da malicious links wanda kana danna shi zai kaika fake websites nashi mai k**a da Exactly irin bankin da ka buɗe, yace maka ka cike personal information naka na banki zaka samu kyautar 100k daga banki.
kana sakawa shikenan bayananka zasu tafi kai tsaye zuwa gareshi zai iya kwashe ko nawa ne a account naka.

Note: Duk wani Email da za'a turo maka tareda wani Links ka tsaya ka natsu sosai ka duba kaga wanene sender ɗin, kuma ka tabbatar address ɗin na gaske ne.

3. Account verification attempts: Akwai websites ɗin da ake amfani da account number wurin yin verification process na canza information naka na banki, hac-ker zai iya canza password naka da sauran details naka ta waɗannan websites ɗin ta hanyar contacting customer service na bankin naka su kuma zasuyi duk abinda hac-ker ɗin ya buƙace su suyi domin duk a tunaninsu kaine.

Note: Karka biyo ni Inbox kace na faɗa maka Websites ɗin koda wasa bazan faɗa ba.
a kula sosai a duk sanda aka turo maka wani Verification code karka sake wani ya kiraka yace katura mashi.

4. Limited financial transactions: Idan Hac-ker ya samu Account Number naka da kuma wasu information naka irinsu sunanka, address naka, phone number, Sim ɗinka, da BVN, to hac-ker zai iyayin yunƙurin yin Transaction na kuɗi daga bankinka wurin yin siyayya a online, transfer na kuɗi zuwa wani account daban da saka katin waya.

Note: Mu kiyaye sensitive information namu ba kowa zaka bari yasan information naka na banki ba saboda tsaro.

A ƙarshe ina cewa, waɗannan hanyoyin guda 4 sune kaɗai hanyoyin da nasani da hac-ker zai iyayi yunƙurin kwashe maka kuɗi kuma ba lallai yayi nasara ba sai ya samu cikakken goyon bayanka, ko kuma cikakken sakakinka, Mu kula sosai mu dinga sanya strong password, unique passwords, da sanya tsarin two-factor authentication ga accounts namu domin tsare kawunanmu daga faɗawa hannun azzalumai..

Ayi sharing ma sauran yan'uwa..

Allah ne mafi sani..

Allah Yataimaka..🙏

Everyone

29/04/2023

BARKANKU MASOYA
WASU LABARAI KUKA FI BUƘATA MU RIKA KAWO MAKU?

Barayin waya sun guntulewa matashi hannu yayin karban wayanshi,Shin Wai meyasa barayi Suke rashin imanin Nan ne mutun da...
28/04/2023

Barayin waya sun guntulewa matashi hannu yayin karban wayanshi,

Shin Wai meyasa barayi Suke rashin imanin Nan ne mutun da Abunshi Dan zaku sata sai kun na ka sa shi?

Sata k**ar na waya, mashin, yafi zama ruwan dare a yanzu abun haushi ma kaida abunka sai a na ka sa ka a lokacin da za'a karba

idan kuka k**a barayi Wani shawara zaku bada ga hukuma?

Barayin waya sun guntulewa matashi hannu yayin karban wayanshi,

Shin Wai meyasa barayi Suke rashin imanin Nan ne mutun da Abunshi Dan zaku sata sai kun na ka sa shi?

Sata k**ar na waya, mashin, yafi zama . lokacin da za'a karba

idan kuka k**a barayi Wani shawara zaku bada ga hukuma?

Barayin waya sun guntulewa matashi hannu yayin karban wayanshi,Shin Wai meyasa barayi Suke rashin imanin Nan ne mutun da...
28/04/2023

Barayin waya sun guntulewa matashi hannu yayin karban wayanshi,

Shin Wai meyasa barayi Suke rashin imanin Nan ne mutun da Abunshi Dan zaku sata sai kun na ka sa shi?

Sata k**ar na waya, mashin, yafi zama . lokacin da za'a karba

idan kuka k**a barayi Wani shawara zaku bada ga hukuma?

Kawo yanzu Matar shahararren dan wasa Achraf Hakimi ɗan asalin ƙasar Marocco ta nemi da ya sawwaƙe mata sannan kuma kotu...
14/04/2023

Kawo yanzu Matar shahararren dan wasa Achraf Hakimi ɗan asalin ƙasar Marocco ta nemi da ya sawwaƙe mata sannan kuma kotu ta sa ya bata rabin duk dukiyar da ya mallaka.

Sai aka sanar da ita cewa ai shi Hakimi ɗin bai mallaka komai ba, domin duk dukiyarsa ya sanya sunan mahaifiyarsa ne akai.

Ana biyan Achraf zunzurutun kuɗi dai har Miliyan €1 daga ƙungiyarsa ta PSG a duk wata.

Amma kaso 80% duk sai ya rubuta a riƙa turawa asusu mai ɗauke da sunan mahaifiyarsa Hajiya Fatima.

Don haka shi kawai ƴan canji yake da shi kaso 20% wanda yake gudanar da rayuwarsa da matarsa.

Duk manyan kadarori k**ar gidaje, motoci, gwala-gwalai da sauran kayan alatu har ma suturu masu tsada suna ɗauke ne da sunan mahaifiyarsa.

Kuma duk sanda yake buƙatar wani abu sai ya tambaye ta ta saya masa.

Ya k**ata ayi koyi da wanga hali na Hakimi, saboda Anzo aci banza, Amma banza bata samu ba.

YAU NE ZAGAYOWAR RANAR YAKIN BADAR A Rana Mai K**ar Ta Yau 17 Ga Watan RAMADAN Aka Gwabza Yakin Badar, Babban Yakin Tari...
08/04/2023

YAU NE ZAGAYOWAR RANAR YAKIN BADAR

A Rana Mai K**ar Ta Yau 17 Ga Watan RAMADAN Aka Gwabza Yakin Badar, Babban Yakin Tarihi Na Duniya Wanda Ba'a Taba Yin Irinsa Ba, Inda Musulmai (313) S**a Gwabza Da Kafirai (1000,) Kuma ALLAH Ya ba Musulmai Nasara S**a Kashe Kafirai S**a K**a Fursunonin Yaki

TARIHIN SHIEKH IBRAHIM INYASS.Amsar Tambayar Ibrahim Muhammad Bello.SHEIKH IBRAHIM INYASS SHINE MALAMIN MUSULMI NA FARKO...
01/07/2022

TARIHIN SHIEKH IBRAHIM INYASS.
Amsar Tambayar Ibrahim Muhammad Bello.

SHEIKH IBRAHIM INYASS SHINE MALAMIN MUSULMI NA FARKO & KADAI A DUNIYA WANDA SARKI FAISAL NA SAUDIYYA YA ZIYARA A KAUYEN SA (KAOLACK) A SENEGAL.

Wanene Shaihu Ibrahim Niasse?

Niasse shi ne dan Afirka ta Yamma na farko da ya jagoranci Masallacin Al-Azhar a Masar , bayan da aka yi masa lakabi da "Sheikh al-Islam". Ya kasance kusa da yawancin Shugabanin masu fafutukar Neman 'yanci a Afirka ta Yamma saboda gudunmawar da ya bayar na 'yancin kai a kasashen Afirka.

Shehu Ibrahim ya tsaya tsayin daka wajen yakar mamaya (Imperialism) da sabbi da tsoffin salon mulkin mallaka da kare yancin kasashe da mutuncinsu da kuma ganin sun tsaya bisa kafafunsu, tareda kara dankon zumunci tsakanin Kasashen Africa dana Yankin Asia dama karfafa tsaron Duniya baki daya.

Menene ma'anar Inyass?

Abubuwa 2 da aka gabatar daga Najeriya sun yarda da sunan Inyass yana nufin " Mutumin kirki "

Ibrāhīm Niasse (1900–1975) - ko (Faransanci Ibrahima Niasse) , Wolof , Larabci: شيخ الإسلام الحاج إبراهيم إبن الحاج عبد الله التجاني الكولخي‎ التجاني الكولخي Shaykh al-'Islām al-Ḥājj Ibrāhīm ibn al-Ḥājj ʿAbd Allāh at-Tijānī al-Kawlakhī - ya kasance babban shugaban Senegal (wolof) na Tijānī Sufi na Islama a Afirka ta Yamma . Mabiyansa a yankin Senegambiya suna kiran shi a harshen Wolof a matsayin Baay, ko "uba."

Niasse shi ne mutumin Afirka ta Yamma na farko da ya jagoranci Masallacin al-Azhar a Misira, bayan an yi masa laƙabi da "Sheikh al-Islam". Ya kasance kusa da masu gwagwarmayar neman ƴanci da yawa a Afirka ta Yamma saboda gudummawar da ya bayar don samun' Ƴanci a Ƙasashen Afirka. Ya kasance aboki kuma mai ba da shawara ga Shugaban Ghana na farko, Kwame Nkrumah, da aboko Ga Gamal Abdel Nasser da Sarki Faisal na Saudi Arabia. Sheikh Ibrahim kasance Mataimakin Shugaban Ƙungiyar Ƙasashen Musulmi ta Duniya tare da Faisal a matsayin Shugaba.

An haife shi a Ranar Alhamis 8 Ga Watan Nuwamba 1900 a ƙauyen Tayba Ñaseen (wanda aka rubuta

KWALE-KWALEN DUFUNA✍️✍️ Basiru Ibrahim Chilo ZangoWannan wani kwale-kwale ne na tafiye tafiye a ruwa da aka gano a kauye...
30/06/2022

KWALE-KWALEN DUFUNA

✍️✍️ Basiru Ibrahim Chilo Zango

Wannan wani kwale-kwale ne na tafiye tafiye a ruwa da aka gano a kauyen Dufuna dake karamar hukumar Fune dake jihar Yobe, a kusa da kogin Komadugu.

An gano wannan kwale-kwale a shekarar 1987. Mallam kaga ba wani dadewa akayi ba ko? Hasalima wani Bafulatani ne makiyayi ya gano shi.

Daga baya Jami'ar Maiduguri da Jami'ar Frankfurt dake Jamus s**ayi aikin hakoshi, a shekarar 1994. Lebura wajen 50 aka saka kan aikin.

Masana kufai da tarihi sun nuna cewa wannan kwale-kwale zaiyi shekaru 8,000 zuwa 8500 da yin amfani dashi. Hasalima,sun auna wasu kwayoyin gawayi da s**a samu a wurin, kuma ya kara basu wannan lissafin.

Idan hakane, kaga tun zamanin Annabawan farko akwai mutane dake rayuwa a wannan yanki namu kenan.

Ina masana? Akwai karin bayani da sharhi kan wannan lamari? Almajiran tarihi Irina kuma muyi tsam da ranmu mu karu daga masana, kada muyi ta shirme da fade-fade.

10/05/2022

Babu wanda ya tuntubemu bare yaji labarin rashin jinmu kwana biyu

18/04/2022

DAGA CIKIN HADISIN SAYYADINA RASULALLAHI (S.A.W)
Daga
Basiru Ibrahim Chilo Zango
*عن أبي هريرة رضي الله عنه، أن النبي صلى الله عليه وسلم قال:- من نصي وهو صاءم، فأكل أو شرب، فليتم صومه فإنما أطعمه الله و سقاه".*
FASSARA:*
An karbo daga abi hurairah (r.a) yace, hakika annabi (s.a.w) yace:-*
"Wanda ya manta yana azumi, Sai yaci (wani abu) ko ya sha (wani abu), to ya cika azuminsa, hakika Allah ne ya ciyar dashi ya shayar dashi (azuminsa bai karye ba)".*

03/04/2022

Barkanmu da zuwan Azumin watan Ramadana

Kira Ga Iyayen Yara Game Da Littafin Maryse Conde Segu Da Bankin UBA Ke Rabawa Dalibai A MakarantuDaga     Iyaye muyi ha...
07/02/2022

Kira Ga Iyayen Yara Game Da Littafin Maryse Conde Segu Da Bankin UBA Ke Rabawa Dalibai A Makarantu

Daga

Iyaye muyi hattara da wani littafi mai suna Maryse Conde Segu da Bankin UBA (United Bank for Africa Plc) Foundation ke rabawa kyauta ga Daliban Makarantar Sakandire, Babu abunda ke cikin wannan littafi sai labaran batsa da lalata tarbiyya.

Wani magidanci a jihar kano ya shaidawa Jaridar ZaurenLabarai k**ar haka,
'Yata yar shekara 12 tana cikin wayanda akaba wannan littafi a Makaranta, ranar 31/01/2022, amma Allah SWT ya taimaka na karba na karanta kuma naga miyagun abubuwan dake ciki. Saboda haka na karbe littafin, na kuma yi sauri na sanar da Makarantar su.

Makarantar sun umarci duk yaron da akaba littafin ya dawo dashi. Saboda haka idan kasan yaronka ya karbi wannan littafi a Makaranta kayi sauri ka karbe ka kuma sanar da Makarantar domin ka ceci sauran yaran dake Makarantar.

Zaku iya duba shafi na 83, 188, 189, 195, 224, 274, 277, 279, 384, 400, 401, 416, 418, 419, da wasu shafukan da dama a cikin littafin. Wannan shine littafin 👆

Ku taimaka ku isar da wannan sako domin ceton tarbiyyar yaran mu.

DARASIN PEPSI 😂😂Ance wani saurayi a siriya yaga wata yarinya yana so, nan take yaje gidansu neman aurenta, baban kuwa ya...
24/01/2022

DARASIN PEPSI 😂😂

Ance wani saurayi a siriya yaga wata yarinya yana so, nan take yaje gidansu neman aurenta, baban kuwa ya yaba da halayensa yace masa to ya kawo sadaki kawai a daura aure, yace lera 200 kawai ya isa. (kimanin kudin kwalbar lemon pepsi)

haka saurayi ya tafi cikin murna da annashuwa ya kawo sadaki aka kai masa amarya gidansa.

saurayin nan se ya fara tsokanar matar tasa da kwalbar pepsi, motsi ba motsiba yace, kin ganki din nan kudinku daya da kwalbar pepsi😥 ko ya aje kwalbar pepsi akan teburin cin abinci yacewa matar darajar wannan darajarki😭😭 (kuma fa shi har ga Allah da wasa yake), yana darajtata yana kimantata amma kuma yana mata wannan wasan ita kuma bata so.
wata rana sunyi tafiya se s**a sayi lemon pepsi, yace yanzu fa da asarar lemon nan da asararki duk dayane ko??

abin ya mata zafi ta tafi gidansu ta fada, don haka babanta yace ta zauna, miji yazo ze dauki matarsa akace yaje ya zo da babansa da mamansa.
bayan sun zo se aka dauko musu lemon pepsi kowa aka aje masa a gabansa, s**a shanye tas, se s**a ce to wance ta fito mu tafi.
babanta yace kun bamu pepsi daya mun baku guda uku😂 ku tafi ku bani waje.

iyayen mijin basu san meke faruwaba, se da baban yarinyar ya basu labari, aiko s**a ce tabbas be k**ata yarinyar nan ta dawo gidan dansuba.
gogan naka se ya zauce har da suma😂 baban yarinya yace kudin biko milyan goma😂😂 in baka dasu ka hakura.
da yike yana sonta haka ya cake milyan goma ya fanshi kwalbar pepsinsa ya maidata gida😂
da s**a koma gida, ya kalleta cikin murmushi yace har gidan yayi haske da kika dawo, yake kamfanin pepsi🤣🤣

BAKI MAI YANKA WUYA!!!

🖍️🖍️

GORON JUMAA INJI Hon. NASIRU SANI ZANGON DAURA MEMBER REPRESENTING ZANGO BAURE FEDERAL CONSTITUENCY.Alhamdlillah.....Ana...
21/01/2022

GORON JUMAA INJI Hon. NASIRU SANI ZANGON DAURA MEMBER REPRESENTING ZANGO BAURE FEDERAL CONSTITUENCY.

Alhamdlillah.....

Ana sanar da wadanda sunayensu ya fito a kasa da su hanzarta yin printing Invitation slip kuma su duba ranar da zasuje ABUJA DOMIN YIN DOCUMENTATION DA AMSAR OFFER'S OF APPOINTMENT NA CIVIL DEFENCE.........

HON.NASIRU SANI ZANGON DAURA Yana masu fatan Alkhairi.......

BAURE LG

1.NAZIRU HUSSAINI
07035152762
2. IBRAHIM ABUBAKAR
08142227569
3. IMRANA SULAIMAN
08137737906
4. MUSA BASHIR
08106142812
5. JABIR ZUBAIRU
07030447474
6. LAWAL SHAFIU
09060479907
7. YASIR BASHAR
08166943967
8. ABDU UMAR
08102950006
9. MUSBAHU RABIU
09035532571
10. SULEMAN ALIYU
07065655434
11.MANSIR ABUBAKAR
08038321369
12. GAMBO DAHIRU
07067428510
13. MUSA AMADU
07026123994
14. MUSA MAHARAZU
07061267798
15. LAWAL ISYA
08071033356
16. SAMINU HARUNA
08165118986

ZANGO LG

1. SANI ABDULMAJID
08169486940
2. UBALE AHMAD
07065881960
3. ADAMU ABDULKARIM
08032974327
4 ABDULWARISU YAKUBU
09017794751
5. BASHIR JAMILU UMAR
08034319650
6. TASIU USMAN
09032267761
7. IBRAHIM GALADIMA
08033818427
8. ADAMU KABIR
07064454398
9. NASIR SAADU
08142523860
10. MUSA YAHAYA
07034712620
11. RABIU FALALU
08107954674
12. SANI IBRAHIM
08147797055
13. TASIU SANI SHUAIBU
07066105265
14. ALI LAWAL
08036100017
15. ABDURRASHID ABDULLAHI
07038304301
16. SALMANU ABUBAKAR
07039265331
17.MANNAIR BASHAR
08031844128
18. SANI SALISU
07035308288
19. ABDURRAHMAN YAHUZA
09038603532
20. NAFIU SANI
08145149035
21. YAKUBU JAMILU
09020906821
22.AMINU MANSUR
09069689066

Sani Baure
Media and Publicity secretary
21/01/2022

Akaron farko Qungiyar izala zata shirya taron maulidin Sahabban Annabi S.A.W wanda akaiwa laqabi da Makon Sahabbai, a Ka...
18/01/2022

Akaron farko Qungiyar izala zata shirya taron maulidin Sahabban Annabi S.A.W wanda akaiwa laqabi da Makon Sahabbai, a KanoDaga

Kungiyar izala zata shirya wani katafaren taron na tunawa da sahabban Annabi wanda akafi sanin irin wadannan taruka da (maulud) na tsawon sati guda, don tunawa da sahabban Annabi S.A.W
Shidai wannan taro za'a fara sane cikin sati me zuwa akwai manya manyan malaman Izala daza su gabatar da lakca awajan taron da za acinye sati guda anayi, kadan daga cikin su akwai Dr. Muhammad Sani Umar Rijiyallemo, da Dr. Mansur Sokkoto, da Dr. Bashir Muhd Umar, da Shugaban Izala na Kano Dr. Abdullahi Sale Pakistan, da sauran manyan malamai da lokaci bazai ba da damar jerosu ba .

Sedai tun bayan fitar sanarwa ta wannan taro ya haifar da cece kuce musamman daga 6angaren 'yan darika inda suke cewa Annabi S.A.W yafi cancanta Qungiyar izala tafara tarukan tunawa dashi ba sahabbai ha, kasancewar kungiyar ta haramta duk wani nau'in taro na tunawa da rayuwar manzon Allah S A.W (maulud) inda kungiyar tace bid'a ne, ace warsu be k**ata ba bayan sune da kansu su hana ai irin wadannan taruka kan manzon Allah S.A.W ba, sukuma agansu zasuyi kan sahabbai wadanda Almajiran Annabi S.A.W ne

Ko menene ra'ayoyin ku akan wannan batu?

Ayi sharing.

Watarana IMAM MALIK (R.T.A) yana bacci sai yayi Mafarki yaga Mala'ikan mutuwa su kayi ta hira.Sai Imam Malik ya tambayi ...
16/01/2022

Watarana IMAM MALIK (R.T.A) yana bacci sai yayi Mafarki yaga Mala'ikan mutuwa su kayi ta hira.
Sai Imam Malik ya tambayi Mala'ikan mutuwa shin saura kwana nawa ya ragemin a duniya?

Sai Mala'ikan ya masa nuni da yatsu
biyar 5, Imam Malik yace me kake nufi da wannan 5? Sai Mala'ikan Mutuwa ya bace anan take, da gari ya waye sai hankalin imam malik ya tashi ya tafi wajen wani Malami masanin fassarar mafarki. Ana ce da shi "Ibn Sirin" Ya bashi labarin tsakaninsa da mala'ikan mutuwa, yace amma abinda ya tayarmar da hankali shine bansan wannan 5 me take nufi ba shin kwana 5 ne ko sati 5 ko wata 5 ne ko kuma shekara 5 ne?

Sai Malamin yace ai wannan 5 itace a
karshen "Suratul Luqman" inda Allah yace"

(1). Lallai Sanin alqiyama na Allah ne shi kadai,

(2). Shike saukar da ruwa,

(3). Shi yasan abinda mahaifa ta kunsa,

(4). Ba wata rai da ta san abinda zata aikata gobe.

(5). Ba wata rai da tasan a ina zata mutu, lallai Allah shine masani mai bada labari.

Daga nan Sai Imam Malik ya koma gida ya dage da ibadah don tanadin mutuwa.

Ya Allah kasa idan mutuwarmu tazo mu cika da imani Albarkan ANNABI S.A.W

Allah kara mana soyayyar annabi s.a.w

Wata Sabuwa, Na Yi Nadamar Rera Waƙar Da Na Yi Wa Buhari Ta "Yau Najeriya Riƙo Sai Mai Gaskiya"  Lokacin Da Ya Fara Yin ...
16/01/2022

Wata Sabuwa,

Na Yi Nadamar Rera Waƙar Da Na Yi Wa Buhari Ta "Yau Najeriya Riƙo Sai Mai Gaskiya" Lokacin Da Ya Fara Yin Takarar Shugaban Kasa. Yanzu Haka Ina Shirin Rera Wata Waƙar Don Bai Wa Ƴan Najeriya Haƙuri Bisa Ga Rashin Tabbatuwar Alkawullan Da Buhari Ya Yi Masu Na Kyautata Rayuwarsu Idan Ya Hau Mulki.

Mawaƙi Ibrahim Yala.
Daga shafin

Wannan Shine Shugaban masu lura da makwancin Shugaba (S.A.W).shi ne wanda ke shiga har dakin da kabarin mai tsira da ami...
14/01/2022

Wannan Shine Shugaban masu lura da makwancin Shugaba (S.A.W).
shi ne wanda ke shiga har dakin da kabarin mai tsira da aminci yake fiye da shekara 20 watarana an tambayeshi shin ko ya taba ganin Manzon Allah(S.A.W) a mafarki?

Sai ya bada amsa da cewa: "Ba sai har munyi mafarki ba zamuga shugaba bana ji muna da bukatar sai a mafarki zamu ganshi ﷺ"

Da aka kara tambayarsa Shin mene abinda ya karanta da wajen duk lokacin da yake shiga? sai yace:

Mutane dayawa da s**a samu shiga wajen in s**ayi sallama fache sai sunji anmaida masu sallamarsu kuma ya fadi cewa duk lokacin da aka samu matsalar wuta ko rashin haske duk sanda mutum ya shiga wani haske yana fitowa daga wajen kabarin Shugaba(S.A.W) da allura zata fadi cikin duffai hasken dake gareahi zai haskakata. Haka wani daga cikin masu yin hidimar makwancin mai tsarki ya kasance yayi wani ciwon ido mai tsanani watarana ya shiga sai kurar dake kan mayafin da aka rufe kabarin Shugaba ta bugi idonsa yace tun daga lokacin bai kara ciwon ido ba ko rauni a ganinsa saboda alfarma Shugaba ﷺ.

Muhammad Jameel.

©Zauren---Labarai.

Address

Kaduna

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Fityanul islam media Zango posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Fityanul islam media Zango:

Share