Shahidanmu TV

Shahidanmu TV Mun bude wannan Page din ne domin kawo muku Fina finain Muslinci kar kashin harkar Muslinci, wadda jagoran mu Malam Ibrahim Zakzaky (H) Yake Jagoranta,

Wannan page din Mallakar A.S Prductions Limited ne wanda ze rinka kawo muku fina finan harkar musulunci qar kashin jagoran Malam Ibrahim Yaqub Zakzaky (H) dan haka muna godiya ga masu kallon mu da kuma masu bamu shawara, akan yanda muke tafiyar da aikin fina finan mu.

JAGORA (H) YA RUFE TATTAKIN ARBA'EEN NA IMAM HUSAINI (AS) NA SHEKARAR 1448HJagora Shaikh Ibraheem Zakzaky (H) ya gabatar...
04/08/2026

JAGORA (H) YA RUFE TATTAKIN ARBA'EEN NA IMAM HUSAINI (AS) NA SHEKARAR 1448H

Jagora Shaikh Ibraheem Zakzaky (H) ya gabatar da jawabin rufe Tattakin Arba'een na Imam Husaini (AS) a yau Talata, 20 ga Safar 1448H, wanda ya yi daidai da 4 ga Agusta, 2026. An gudanar da taron ne a Babban Filin Wasa na Suleja, kusa da Babban Birnin Tarayya, Abuja.

A farkon jawabinsa, Jagora (H) ya tunatar da mahalarta cewa ranar 20 ga Safar ita ce ranar cikar kwanaki arba'in da shahadar Imam Husaini (AS), iyalansa da sahabbansa. Ya bayyana cewa ziyarar Arba'een wata ibada ce da ta samo asali tun daga shekara ta 61 bayan Hijirar Manzon Allah (SAW), lokacin da Sahabi Jabir bn Abdullahi Al-Ansari (RA) ya fara ziyartar kabarin Imam Husaini (AS) bayan aukuwar waƙi'ar Karbala.

Ya ci gaba da bayyana muhimmancin ziyarar Arba'een tare da kawo hadisai da s**a nuna falalarta, yana mai ƙarfafa muminai su ci gaba da raya wannan al'ada ta Ahlul Baiti (AS).

Shahidanmu TV

03/08/2026

Ministan harkokin wajen Iran Abbas Araghchi ya yi tafiya zuwa birnin Najaf na Iraki a ranar Litinin kafin Arbaeen, cika kwana 40 da Shahadar IMAM Hussain (A.S)

DARUSSAN ARBA'IN Assalamu Alaikum wa Rahmatullahi wa Barakatuh, iyaye masu daraja.Arba'in wata babbar dama ce ta tunawa ...
03/08/2026

DARUSSAN ARBA'IN

Assalamu Alaikum wa Rahmatullahi wa Barakatuh, iyaye masu daraja.

Arba'in wata babbar dama ce ta tunawa da sadaukarwar Imam Husain (A.S.) da sahabbansa a Karbala. Wannan rana tana tunatar da mu cewa gaskiya tana buƙatar jajircewa, kuma kare addini da mutuncin ɗan Adam yana iya buƙatar sadaukarwa.

Imam Husain (A.S.) ya ƙi amincewa da zalunci, ya zaɓi tsayawa kan gaskiya duk da ya san irin wahalhalun da za su biyo baya. Wannan ya koya mana cewa Musulmi na gaskiya ba ya sayar da addininsa saboda tsoro ko son duniya.

A matsayinmu na iyaye, mu yi ƙoƙarin tarbiyyantar da 'ya'yanmu a kan gaskiya, adalci, haƙuri, biyayya ga Allah, da ƙaunar Ahlul Baiti (A.S.), domin waɗannan su ne manyan darussan Karbala.

Allah Ya sanya mu da iyalanmu cikin mabiyan Imam Husain (A.S.) na gaskiya, Ya ba mu ikon rayuwa da mutuwa a kan tafarkinsa.

السَّلَامُ عَلَى الْحُسَيْنِ، وَعَلَى عَلِيِّ بْنِ الْحُسَيْنِ، وَعَلَى أَوْلَادِ الْحُسَيْنِ، وَعَلَى أَصْحَابِ الْحُسَيْنِ.

✍️ Zahra Muhammad Ibrahim

02/08/2026

Yanda tattakin IMAM Hussain yake gudana daga yankin Kaduna Part 8

02/08/2026

Yanda tattakin IMAM Hussain yake gudana daga yankin Kaduna Part 7

02/08/2026

Yanda tattakin IMAM Hussain yake gudana daga yankin Kaduna Part 6

02/08/2026

Yanda tattakin IMAM Hussain yake gudana daga yankin Kaduna Part 5

02/08/2026

Yanda tattakin IMAM Hussain yake gudana daga yankin Kaduna Part 4

02/08/2026

Yanda tattakin IMAM Hussain yake gudana daga yankin Kaduna Part 3

Address

No R7 Afamu Road Badikko
Abuja
8002122

Telephone

+2348142292256

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Shahidanmu TV posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Shahidanmu TV:

Shortcuts

Share