02/05/2026
sHAm✔,
BAITIL HARAM:- (ɗakin ka'aba) ta na garin makkah,
BAITIL MAQDIS:- ta na ƙasar sham,
SHAM,:- sham ƙasa ce mai albarka, ALLAH ya sanya albarka a cikin ta ne saboda ɗakin shi na masjidil aqsa da ya ke cikin ta,
masjidil aqsa ta na ɗaya daga cikin masallatai uku mafiya daraja a sararin duniya, domin shine masallaci na biyu mafiya daraja a tarihin duniyar musulunci a wannan duniyar namu,
farkon masallaci a doron ƙasa na wannan duniyar namu shine ɗakin ka'aba da ke birnin makkah, daga nan sai masallacin qudus na kasar sham, Wato baitil maqdis,
an tambayi annabi S.A.W, tsakanin masallacin ka'aba da masallacin qudus shekara nawa ne?, sai yace:- tsakanin su shekaru 40 ne,
kasar sham, kasa ce mai albarka saboda wannan masallaci na baitil aqsa da yake cikin ta, kasar sham ALLAH ya mayar da wajen wurin hijirar annaawa, saboda albarkan da ya sanya mata,
annabi musa_A.S a nan yayi hijirah, annabi ibrahim_A.S shi ma a nan yayi hijirah bayan ya bar kasar iraqi, nan ne a ka mayar dashi wurin kaiwa da dawowar annabi dawud_A.S, da annabi sulaiman_A.S,
kasar sham kasa ce mai albarka, domin a lokacin da annabi muhammad_S.A.W zai yi isra'i da mi'iraji to daga makkah ya ta so zuwa kasar sham,
ISRA'I:- shine tafiyar dare da Annabi Muhammad S.A.W ya ka yi daga baitil haram zuwa baitil maqdis,
MI'IRAJi:- kuma shine tashi domin tafiya sama daga masjidil aqsa zuwa sama wurin ALLAH S.W.A,
baitil maqdis a kasar sham ta ke, ƙasar sham, tabbas kasa ce mai albarka, ALLAH ya sanya dausayi a cikin ta, kuma ya sanya koguna na ruwa a cikin ta, idan ka je ka ga yadda yankin lebanon da yankin jordan da kuma ita kan ta sham din ta ke, idan ka ga yadda wurin ya ke da yanayi mai kyau, ga tsaunuka a lullu6e kore sharrr ga gonakin zaitun to za kasan cewa tabbas nan ne aljannar duniya, sai dai yahudu da nasara sun sanya wurin a gaba, sai dai kawai mu ce ALLAH ya kyauta amin,
kasar sham, Ina ƙara faɗa mu ku cewa:- ƙasa ce mai albarka,
Sir Babawo Fadan Chawai.