Taswira

Taswira Ku kasance da Shafin Tswira domin samun ingantatun labarai da rahotanni cikin harshen Haisa.

Ga sarki da Yariman sa a fada.
07/08/2026

Ga sarki da Yariman sa a fada.

BAN TABA GANIN INDA ANGOLA YA KORI DAN MAI GIDA BAAbdulmajid Dan Bilki Kwamanda ya mayar da martani kan sanarwar kan kor...
07/08/2026

BAN TABA GANIN INDA ANGOLA YA KORI DAN MAI GIDA BA

Abdulmajid Dan Bilki Kwamanda ya mayar da martani kan sanarwar kan korarsa daga jam’iyyar APC, inda ya bayyana cewa babu wanda ya isa ya kore shi daga jam’iyyar.

A wata sanarwa da ya wallafa, Dan Bilki ya ce agola ba zai iya korar mai gida ba.

Kalaman nasa na zuwa ne sa’o’i kaɗan bayan Kakakin APC na Jihar Kano, Auwalu Abdullahi Soja, ya sanar da cewa jam’iyyar ta kori Kwamanda bisa zargin kalamai da s**a saba wa dokoki da ƙa’idojin jam’iyyar.

07/08/2026
Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar SDP, Adewole Adebayo, ya ce za a iya kawo karshen matsalolin Najeriya cikin sheka...
07/08/2026

Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar SDP, Adewole Adebayo, ya ce za a iya kawo karshen matsalolin Najeriya cikin shekaru uku

Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Social Democratic Party (SDP), Dr. Prince Adewole Adebayo, ya bayyana cewa za a iya magance matsalolin rashin tsaro, cin hanci da rashawa da kuma matsin tattalin arziki da Najeriya ke fuskanta cikin shekaru uku, idan aka zabi shugabanni masu kwarewa da gaskiya.

Adebayo ya bayyana hakan ne a taron Arewa Awareness Summit on Unity Against Insecurity da aka gudanar a Kaduna, inda ya ce matsalolin kasar sun dade ne saboda rashin kyakkyawan shugabanci.

Ya ce hanyoyin magance matsalolin Najeriya a bayyane suke, abin da ake bukata kawai shi ne shugabannin da za su mayar da hankali wajen samar da mafita.

Dan takarar SDP ya kuma bayyana Arewacin Najeriya a matsayin ginshikin makomar kasar, yana mai cewa yawan al’umma da dimbin albarkatun kasa da yankin ke da su za su iya zama babbar hanyar bunkasa tattalin arziki idan aka samu shugabanci nagari.

Ya kuma bukaci ‘yan Najeriya da kada su dauki kansu a matsayin marasa karfi, domin dimokuradiyya ta ba su damar zabar shugabannin da za su magance matsalolinsu.

Kwankwaso ya jagoranci taron masu ruwa da tsaki na NDC a KanoƊan takarar mataimakin shugaban ƙasa na jam'iyyar NDC, Sana...
06/08/2026

Kwankwaso ya jagoranci taron masu ruwa da tsaki na NDC a Kano

Ɗan takarar mataimakin shugaban ƙasa na jam'iyyar NDC, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, PhD, FNSE, ya jagoranci taron masu ruwa da tsaki na jam'iyyar a Jihar Kano, wanda aka gudanar a gidansa da ke kan titin Miller Road.

Taron ya haɗa da ɗan takarar gwamna da mataimakinsa, 'yan takarar Majalisar Dattawa, Majalisar Wakilai da Majalisar Dokokin Jihar Kano.

Taron na daga cikin shirye-shiryen jam'iyyar na ci gaba da haɗa kai da tsara dabarun tunkarar zaben 2027 da ke tafe.

RIGIMAR ’YAN KALLO A KAN ’YAN FILMTsakanin shekarar 2000 zuwa 2007, an sha samun hatsaniya tsakanin masoyan waɗannan jar...
06/08/2026

RIGIMAR ’YAN KALLO A KAN ’YAN FILM

Tsakanin shekarar 2000 zuwa 2007, an sha samun hatsaniya tsakanin masoyan waɗannan jarumai. Har ta kai ga ana ba hammata iska, musamman idan aka haɗa su a film, aka yi wata rawa a cikin wata waka, ko kuma ɗaya daga cikinsu ya nuna ƙwarewa fiye da ɗayan.

Wannan ya sa magoya bayansu ke ta muhawara da ce-ce-ku-ce, kowa yana ganin jarumin da yake so shi ne ya fi kowa.

Me kuke ganin ya sauya tunanin mutane yanzu aka rage irin wanchan soyayya

Ko Kuna Fatan Vinicius Jr. Ya Bar Real Madrid Zuwa Arsenal?
06/08/2026

Ko Kuna Fatan Vinicius Jr. Ya Bar Real Madrid Zuwa Arsenal?

Mai Adaidaita Sahu Ya Buge Kamaye Na Dadin Kowa, Ya Karya Masa Ƙafa Sannan Ya TsereRahotanni sun nuna cewa Kamaye Na Dad...
06/08/2026

Mai Adaidaita Sahu Ya Buge Kamaye Na Dadin Kowa, Ya Karya Masa Ƙafa Sannan Ya Tsere

Rahotanni sun nuna cewa Kamaye Na Dadin Kowa ya samu mummunan rauni bayan wani direban Adaidaita Sahu ya buge shi, lamarin da ya yi sanadin karyewar ƙafarsa. Bayan aukuwar haɗarin, an ce direban ya tsere daga wurin ba tare da ya tsaya ba.

Bayanan da s**a fito sun ce Kamaye ya bayyana cewa ba zai yafe wa direban ba har sai ya zo ya same shi da kansa ya kuma nemi afuwa kan abin da ya faru.

Iyalan Kamaye da na kusa da shi sun yi kira ga al'umma da su taya shi da addu'ar Allah Maɗaukakin Sarki Ya ba shi lafiya cikin gaggawa. Sun kuma roƙi jama'a da su yaɗa labarin domin idan ya kai ga direban, hakan na iya sa ya fito ya ɗauki alhakin abin da ya faru tare da neman yafiya.

Ana ci gaba da fatan Allah Ya ba Kamaye Na Dadin Kowa cikakkiyar lafiya, Ya kuma kare al'umma daga aukuwar irin waɗannan haɗurran a nan gaba.

06/08/2026

Wasu fusatattun matasa sun ƙona motar aikin Hukumar KAROTA a yankin Kwanar Dawaki da ke kan hanyar Kano zuwa Zariya, bayan wani hatsarin mota da ya faru a yankin.

Mataimakin Manajan-Daraktan KAROTA, Auwal Lawal Aranposu, ya ce hatsarin ya faru ne tsakanin wata motar Sharon da tirela, inda direban tirelar ya tsere bayan haɗarin. Ya ce wasu matasa sun zargi jami'an KAROTA da haddasa lamarin, s**a kai musu hari tare da ƙona motar hukumar.

Aranposu ya musanta zargin, yana mai cewa jami'an KAROTA sun taimaka wajen ceto waɗanda hatsarin ya rutsa da su tare da kai su asibiti domin samun kulawar likitoci.

Address

Kaduna

Telephone

+2349072512499

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Taswira posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Shortcuts

Share