06/07/2026
Mulkin Tinubu cike ya ke da rikici - Atiku
Dan takarar shugaban kasa na jam'iyyar ADC, Atiku Abubakar, ya ce gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu na kara fuskantar zarge-zargen badakala fiye da mayar da hankali kan gudanar da mulki.
A cikin wata sanarwa da mai taimaka masa kan harkokin yaɗa labarai, Phrank Shaibu, ya fitar, Atiku ya ce cece-kucen da s**a dabaibaye abin da ake kira Presidential Foreign Intervention Promotion Council (PFIPC) na nuna yadda ake yawan samun batutuwan da ba a warware ba a gwamnatin Tinubu.
Tsohon mataimakin shugaban kasar ya zargi gwamnatin da nuna son kai wajen gudanar da bincike kan zarge-zargen cin hanci da rashawa, yana mai cewa ana saurin daukar mataki idan wadanda ake zargi ba su da karfin siyasa, amma idan lamarin ya shafi masu kusanci da gwamnati, binciken kan tsaya cik.
Ya kuma ambaci batutuwan da s**a shafi dakatar da tsohuwar ministar jin kai, zarge-zargen satar danyen mai, kashe kudaden gyaran matatun mai, da kuma tambayoyi kan ayyukan NNPC a matsayin misalan batutuwan da har yanzu ba a yi musu cikakken bayani ba.
Atiku ya bukaci Shugaba Tinubu ya fito ya yi cikakken bayani kan wadannan batutuwa da kuma wasu cece-kuce da s**a shafi tarihinsa, yana mai cewa gaskiya da rikon amana su ne ginshikin shugabanci nagari. Ya gargadi cewa ci gaba da yin shiru kan irin wadannan zarge-zarge zai kara raunana amincewar jama'a da gwamnati.