30/05/2025
AL'UMMAR ƘARAMAR HUKUMAR NASARAWA, SUN GAMSU DA AYYUKAN WAKILCIN DA HONOURABLE HASSAN SHEHU HUSSAINI, A CIKIN SHEKARU BIYU
Daga Ibrahim Muhammad.
Dan majalisar tarayya mai wakiltar Karamar Hukumar Nasarawa, wato Honourable Hassan Shehu Hussain, daya ne daga yan majalisu da ya ke samun kyakkyawan shaida na gudanar da ayyuka daban daban a mazabarsa.
Al'ummar karamar Hukumar Nasarawa har da yan adawa, suna da kyakkyawan shaida a kansa na gudanar da ayyuka da yake yi musu a fannoni daban daban, da babu mai musun haka duk da cewa wannan shine zuwansa majalisar tarayya na farko.
Sannanen abu ne a kundin tsarin mulkin Nijeriya, babban aikin dan majalisa a kowane mataki shine ya kai kudiri akan abinda ya shafi cigaban al'umma ayi duba akan muhimmancinsa da amfaninsa ga cigaba ayi masa karatu ayi doka akai ko a yan kwanakin nan ya gabatar da kudirin na neman Gwamnatin tarayya ta kawo daukin gaggawa ga masana'antun Kano ta tallafa musu da inganta harkar wutar lantarki.
Sannan akwai kudirin da yakai domin bunkasa Asibitin koyarwa na Malam Aminu Kano da kuma samar da cibiyar kula cutukan zuciya a Asibitin.
Kai irin wannan kudiri ba kowane dan majalisa ne ke iya mikewa ya yi ba ,hatta yan majalisu da s**a jima suna zuwa majalisar wasu basu taba wani motsi don gabatar da wani kuduri ba,sanannen abu ne ga al',ummar jihar Kano dan majalisa tarayya mai wakiltar karamar Hukumar Nasarawa Hon.Hassan Shehu Husaini yana daga cikin wadanda s**a ciri tuta wajen kai kudiri farfajiyar majalisar tarayya akan abinda ya shafi al'ummarsa da cigaban jihar Kano.
Zuwan sa majalisa don wakiltar alummar karamar hukumar Nasarawa ya shigar da kudurori da dama da s**a tsallake karatu har s**a tabbata.
A bangaren ayyuka kuwa irin gudunmawar da yake bayarwa a bangaren Ilimi ya haɗa da samawa matasa Maza da Mata gurbi a manyan makarantu da biya musu kudaden makarantun a kwalejin ilimi na saadatu Abubakar Rimi da Kano polytechnic da collage of art and remedial studies
School of health and technology.
dalibai 600 sun ci gajiya.Ya kuma biya kudin jarabawar WAEC,NECO ,JAMB na mutun 1800..Sannan ya dauki nauyin karatun marayu 150 tun daga makarantar renon ' nursery' har zuwa makarantar gaba da sakandire..
Haka fannin samar da Ruwan sha ya gina Rijiiyoyin burtatse guda 30 a mazabun karamar hukumar Nasarawa 11.Ya samar da tituna
masu tsawan kilomita Biyu-biyu a mazabun Gama da tudun wada.Haka a mazabar Gawuna,
da tudun murtala da mazabar hotoran kudu ya samar da tituna masu tsawon kilomita daya.
A bangaren inganta samar da wutar lantarki ya samar tiransifoma na wuta mai karfin KW 500 a mazabar Gwagwarwa da mazabar hotoran arewa da mazabar hotoron kudu.
A bangaren gine -gine ya gina rukunin ajujuwa 3 a makarantar. firamare na lLadanai a mazabar hotoron Arewa .ya samar da gini mai ajujuwa Biyu a makarantar community school a unguwar Tishama, Hotoron Arewa ya
gina ajujuwa Biyu a makarantar sakandire da ke Dakata.
A bangaren inganta lafiya ya samar da ginin Asibitin sha ka tafi "Clinic hospital" da kayan aiki a unguwar Yandodo Hotoran Arewa.Sannan ya samar da fitilu masu amfani da hasken Rana a dukkanin mazabu 11 na karamar hukumar Nasarawa.
Hon.Hassan Shehu Husaini a karkashin wannan wakilcin nasa ya samawa matasa aikin yi a mataki na Gwamnatin jiha dana tarayya kimanin mutum 20.
Sannan yana bayar da tallafi domin Gina rayuwar alumma a bangarori da dama da matasa maza da mata da iyaye da dama s**a anfana sannan a cikin watan azumin da na sallah ya tallafawa al umma da abubuwan more rayuwa ta fannoni daban daban domin gina rayuwar su.
Duk wadannan ayyuka da dan majalisar tarayya na Nasarawa Hon.Hassan Shehu Husaini yake sauke nauyi ne na al'ummar da s**a zabe shi ,wanda a ma'auni na adalci yana yin abinda ya dace da ya shafi cigaban alummar sa..
Wasu yan siyasa sun ce Idan aka samu wasu na kalubalantar sa a iya cewa suna yine kawai saboda wani abu da ya haɗa su dashi akan kansu, amma ba don gazawa a wajen a sauke nauyin wakilci da al'ummar ƙaramar hukumar Nasarawa s**a dora masa ba a majalisar tarayya.
Muhimmin aikinsa da doka ta tanada masa shine kai kudiri, yin ayyukan alummar sa kuma yana yi suma masu s**ar sa, basa zarginsa da gazawa a wannan bangaren..
Sai da Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya jinjinawa kokarin da dan majalisar yake a wani taro na bude hanyoyi da dan majalisar yayi har yayi jan hankali.ga sauran yan majalisu suyi koyi dashi