Idon Mikiya News

Idon Mikiya News Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from Idon Mikiya News, Media/News Company, Kaduna, Kaduna.

Kafar sadarwa ta Jaridar Idon Mikiya za ta tsayu wajen zama hanyar samun sahihan labarai na ciki da wajen kasar nan, tare da zama hanyar isar da sakonni daga masu mulki zuwa wadanda ake mulka ba tare da tauye wa wani hakkinsa na fada a ji ba.

09/06/2025

This is happening in almost every government hospital throughout Nigeria...Negligence of duty in highest order!!

ABBA KABIR YUSUF SHEKARA BIYU A KAN KARAGAR MULKIN JIHAR KANO TA SAMU GAGARUMAR NASARA - Inji Alhaji Habu Muhammad Fagge...
02/06/2025

ABBA KABIR YUSUF SHEKARA BIYU A KAN KARAGAR MULKIN JIHAR KANO TA SAMU GAGARUMAR NASARA -
Inji Alhaji Habu Muhammad Fagge.

_Daga Ibrahim Muhammad_

Gwamnatin jihar Kano karkashin jagorancin gwamna Abba Kabir Yusuf, ta yi wani gagarumin yunkuri na biyan hakkokin ‘yan fansho da s**a kammala aiki shekaru 35 da kuma wadanda s**a rasu a lokacin da suke aiki. Wadannan ‘yan fansho dai sun shafe shekaru takwas ba tare da biyan su ba a Gwamnatin da ta gabata.

Alhaji Habu Muhammad Fagge, shugaban amintattu na asusun fansho na jihar Kano, ne ya bayyana hakan yace Gwamnatin Abba Kabir Yusuf ta kawar da matsalolin yan fansho ta biya makudan kudaden yan fansho Naira biliyan 16 yanzu haka ma akwai Naira Biliyan Biyar da da suke a kasa kadan da za a biya.A.cikin shekaru biyun farko da ga rantsar dashi wanda ya kawo dauki ga daruruwan ‘yan fansho da iyalansu.

A karkashin jagorancin Gwamna Abba Kabir Yusuf, jihar Kano ta samu gagarumin sauyi a harkokin mulki da samar da ayyuka da kuma jagoranci.Jihar ta aiwatar da aikace aikace da inganta ababen more rayuwa, farfado da ilimi, inganta harkokin kiwon lafiya, da tsare-tsare na karfafa matasa, wanda hakan ya sa yake samun kyakkyawan shaidar yabo a kasar baki daya.

Fitattun nasarori sun hada da: ayyana dokar ta baci a fannin ilimi da sanya kaso mai yawa a kasafin kudin 2024 da na 2025 ga ilimi da.ake ta aiwatar da ayyuka dake inganta tsarin ilimi.Ana habaka tsarin kiwon lafiya da inganta Asibitoci da cibiyoyin kiwon lafiya na matakin farko.

Alhaji Habu Muhammad Fagge ya danganta wadannan nasarorin da irin yadda Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya jajirce wajen kyautata rayuwar al’ummar Kano da kuma dogon hangen nesansa na samar da cigaba mai dorewa.

Shugaban hukumar asusun amintattu na fansho na jihar Kano.Alhaji Habu Muhammad Fagge ya yi addu’ar Allah ya cigaba da yi wa Gwamnan Jihar Kano da dukkan mukarraban Gwamnatinsa jan gora wajen cigaba da hidimtawa bunkasa cigaban al'ummar Jihar Kano.

AL'UMMAR ƘARAMAR HUKUMAR NASARAWA, SUN GAMSU DA AYYUKAN  WAKILCIN DA HONOURABLE HASSAN SHEHU HUSSAINI, A CIKIN SHEKARU B...
30/05/2025

AL'UMMAR ƘARAMAR HUKUMAR NASARAWA, SUN GAMSU DA AYYUKAN WAKILCIN DA HONOURABLE HASSAN SHEHU HUSSAINI, A CIKIN SHEKARU BIYU

Daga Ibrahim Muhammad.

Dan majalisar tarayya mai wakiltar Karamar Hukumar Nasarawa, wato Honourable Hassan Shehu Hussain, daya ne daga yan majalisu da ya ke samun kyakkyawan shaida na gudanar da ayyuka daban daban a mazabarsa.

Al'ummar karamar Hukumar Nasarawa har da yan adawa, suna da kyakkyawan shaida a kansa na gudanar da ayyuka da yake yi musu a fannoni daban daban, da babu mai musun haka duk da cewa wannan shine zuwansa majalisar tarayya na farko.

Sannanen abu ne a kundin tsarin mulkin Nijeriya, babban aikin dan majalisa a kowane mataki shine ya kai kudiri akan abinda ya shafi cigaban al'umma ayi duba akan muhimmancinsa da amfaninsa ga cigaba ayi masa karatu ayi doka akai ko a yan kwanakin nan ya gabatar da kudirin na neman Gwamnatin tarayya ta kawo daukin gaggawa ga masana'antun Kano ta tallafa musu da inganta harkar wutar lantarki.
Sannan akwai kudirin da yakai domin bunkasa Asibitin koyarwa na Malam Aminu Kano da kuma samar da cibiyar kula cutukan zuciya a Asibitin.

Kai irin wannan kudiri ba kowane dan majalisa ne ke iya mikewa ya yi ba ,hatta yan majalisu da s**a jima suna zuwa majalisar wasu basu taba wani motsi don gabatar da wani kuduri ba,sanannen abu ne ga al',ummar jihar Kano dan majalisa tarayya mai wakiltar karamar Hukumar Nasarawa Hon.Hassan Shehu Husaini yana daga cikin wadanda s**a ciri tuta wajen kai kudiri farfajiyar majalisar tarayya akan abinda ya shafi al'ummarsa da cigaban jihar Kano.

Zuwan sa majalisa don wakiltar alummar karamar hukumar Nasarawa ya shigar da kudurori da dama da s**a tsallake karatu har s**a tabbata.

A bangaren ayyuka kuwa irin gudunmawar da yake bayarwa a bangaren Ilimi ya haɗa da samawa matasa Maza da Mata gurbi a manyan makarantu da biya musu kudaden makarantun a kwalejin ilimi na saadatu Abubakar Rimi da Kano polytechnic da collage of art and remedial studies
School of health and technology.
dalibai 600 sun ci gajiya.Ya kuma biya kudin jarabawar WAEC,NECO ,JAMB na mutun 1800..Sannan ya dauki nauyin karatun marayu 150 tun daga makarantar renon ' nursery' har zuwa makarantar gaba da sakandire..

Haka fannin samar da Ruwan sha ya gina Rijiiyoyin burtatse guda 30 a mazabun karamar hukumar Nasarawa 11.Ya samar da tituna
masu tsawan kilomita Biyu-biyu a mazabun Gama da tudun wada.Haka a mazabar Gawuna,
da tudun murtala da mazabar hotoran kudu ya samar da tituna masu tsawon kilomita daya.

A bangaren inganta samar da wutar lantarki ya samar tiransifoma na wuta mai karfin KW 500 a mazabar Gwagwarwa da mazabar hotoran arewa da mazabar hotoron kudu.

A bangaren gine -gine ya gina rukunin ajujuwa 3 a makarantar. firamare na lLadanai a mazabar hotoron Arewa .ya samar da gini mai ajujuwa Biyu a makarantar community school a unguwar Tishama, Hotoron Arewa ya
gina ajujuwa Biyu a makarantar sakandire da ke Dakata.

A bangaren inganta lafiya ya samar da ginin Asibitin sha ka tafi "Clinic hospital" da kayan aiki a unguwar Yandodo Hotoran Arewa.Sannan ya samar da fitilu masu amfani da hasken Rana a dukkanin mazabu 11 na karamar hukumar Nasarawa.

Hon.Hassan Shehu Husaini a karkashin wannan wakilcin nasa ya samawa matasa aikin yi a mataki na Gwamnatin jiha dana tarayya kimanin mutum 20.

Sannan yana bayar da tallafi domin Gina rayuwar alumma a bangarori da dama da matasa maza da mata da iyaye da dama s**a anfana sannan a cikin watan azumin da na sallah ya tallafawa al umma da abubuwan more rayuwa ta fannoni daban daban domin gina rayuwar su.

Duk wadannan ayyuka da dan majalisar tarayya na Nasarawa Hon.Hassan Shehu Husaini yake sauke nauyi ne na al'ummar da s**a zabe shi ,wanda a ma'auni na adalci yana yin abinda ya dace da ya shafi cigaban alummar sa..

Wasu yan siyasa sun ce Idan aka samu wasu na kalubalantar sa a iya cewa suna yine kawai saboda wani abu da ya haɗa su dashi akan kansu, amma ba don gazawa a wajen a sauke nauyin wakilci da al'ummar ƙaramar hukumar Nasarawa s**a dora masa ba a majalisar tarayya.

Muhimmin aikinsa da doka ta tanada masa shine kai kudiri, yin ayyukan alummar sa kuma yana yi suma masu s**ar sa, basa zarginsa da gazawa a wannan bangaren..
Sai da Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya jinjinawa kokarin da dan majalisar yake a wani taro na bude hanyoyi da dan majalisar yayi har yayi jan hankali.ga sauran yan majalisu suyi koyi dashi

WATA KOTU TA AIKE DA WASU  MATASA HUDU YAN TIKTOK GIDAN GYARAN HALI A JIHAR KANO Daga Ibrahim Muhammad Shugaban Hukumar ...
29/05/2025

WATA KOTU TA AIKE DA WASU MATASA HUDU YAN TIKTOK GIDAN GYARAN HALI A JIHAR KANO

Daga Ibrahim Muhammad

Shugaban Hukumar tace fina-finai da Dab'i ta Jahar Kano, Alh. Abba Almustapha, ya jaddada aniyarsa ta kawo karshen ayyukan rashin da'a da ke yawaita a kafafen sada zumunta na zamani a Jahar Kano, inda a yau Hukumar ta samu nasarar k**a wasu matasa guda 4 masu amfani da manhajar TikTok da ake zargi da nuna rashin tarbiya tare da kalamai mara sa ma'ana, inda yin hakan laifi ne a dokar Hukumar.

Hukumar ta
yanke shawarar kaisu gaban kotu domin girbar abinda s**a shuka.

Tunda farko bayan mai gabatar da Kara Brr. Garzali Maigari Bichi, ya karanto wa wanda ake zargi tuhume-tuhumensu wato *Hafsa Hamisu (Zoom Zoom), Usman Majidadi (Majidadi) Sumayya Muhammad (Summy Beby) da Usman Ibrahim (Maikalar Kudi)* inda dukkanninsu nan take s**a amsa, saidai mai shari'ar dake kotun no-man's-land Hajiya Halima wali ta dage sauraran karar daga 28/5/2025 zuwa 2/6/2025 tare da bada umarnin a ajiyesu a gidan gyaran hali har ranar da za'a dawo domin yanke hukunci.

Idan ba'a mantaba a watanin da s**a gabata Hukumar tace fina-finai da Dab'i ta Jahar Kano ta aike da irin wannan matasa gaban kotu domin ladaftar dasu inda kotun bayan samunsu da laifi kotun ta yanke musu hukuncin daurin shekara daya ko zabin biyan tara na kudi nera dubu Dari daya (100,000) tare da wanda zasu karbesu da sharadin irin haka bazai kara faruwa dasu ba.

Wannan de wani yunkuri ne da Hukumar tace fina-finai ta Jahar Kano ke yi tsawon lokaci domin kawo gyara tare da dakile irin rashin tarbiyar da wasu matasa ke nunawa a kafafen sada zumunta a Jahar Kano wanda yin hakan yaci karo da tsarin al'ada tare da koyarwar addinin musulunci.

wannan na kunshe ne a cikin Sanarwa da
Abdullahi Sani Sulaiman Jami'in yada labarai na Hukumar tace fina-finai da Dab'i ta Jahar Kano ya rabawa manema labarai.

Sanarwar ta kara da cewa domin haka hukumar ta kai su gaban kotu domin girbar abinda s**a shuka.

YADDA AMBASADA HAJIYA SAMIRA BALA USMAN, TA KARBI SHAIDAR ZAMA TAURARUWAR HAUSA  *Daga Ibrahim Muhammad* Sak**akon kyakk...
25/05/2025

YADDA AMBASADA HAJIYA SAMIRA BALA USMAN, TA KARBI SHAIDAR ZAMA TAURARUWAR HAUSA

*Daga Ibrahim Muhammad*

Sak**akon kyakkyawar shaida ta irin gudunmuwa da al'umma s**a shaidi Hajiya Samira Bala Usman, na bayarwa ga cigaban al'umma Gidauniyar Hausa da hadin kan Hausawan Duniya" charity" ta tabbatar mata da bata matsayin Tauraruwar Hausa da cigaban Hausawan Duniya, a yayin wani taro da aka gudanar na Gidauniyar a jihar Kano.

Da take zantawa da yan jarida bayan karbar shaidar na tabbatar mata da matsayinta na tauraruwar Hausa da hadin kan Hausa Hajiya Samira Bala Usman, ta bayyana mutukar farin cikinta game da wannan shaida da aka bata na zama daga cikin shugabanni a Gidauniyar Hausa da Hausawan Duniya "charity.

Ta ce Gidauniyar ta Hausa da hadin kan Hausa tana da himma, kwazo da kuma kishi wajen samawa Hausawan Duniya hadin kai da cigaba a tsarin tafiyar da rayuwar su a duk inda suke.

Ta kara da cewa ta yi mutukar gamsuwa sosai da irin tsare-tsare da Gidauniyar take yi masu dinbin ma'ana wajen tallafawa gina cigaban al'umma musamman kokarin da take. wajen hana barace barace da tallafawa marayu da kuma hada kan al'ummar Hausawa a duk inda s**a samu kansu a duniya, kowa ya san dan'uwansa sanan suna kuma bunkasa al'adu da harshen Hausa wacce ta watsu a duniya.

Ambasada Hajiya Samira Bala Usman, Tauraruwar ta Hausa da Hausawan Duniya ta kara da nuni da cewa dama ita wannan Gidauniyar ta Hausa da hadin kan Hausawa ta Duniya tana da jajicewa wajen taga cigaban al'ummar Hausawa suma da s**a zama daga mambobinta za su bada irin tasu gudunmawa sosai domin cigaba ganin ana samun nasarar hada kan al'ummar Hausawa a ko'ina a kowace kasa a fadin Duniya .

Daga karshe Tauraruwar ta Hausa ta kara da godewa dukkan wadanda s**a zo don taya ta murna a wannan matsayi da kuma yin kira ga dukkan yan kungiyar su cigaba da bada misali na kyakkyawan hadin kai a tsakaninsu don gina cigaban Gidauniyar.

INNA LILLAHI WA INNA ILAIHI RAJI'UNAllah Ya yi wa Mahaifin Babban Editan Jaridar Almizan, Malam Ibrahim Musa, Rasuwa. Ma...
21/05/2025

INNA LILLAHI WA INNA ILAIHI RAJI'UN

Allah Ya yi wa Mahaifin Babban Editan Jaridar Almizan, Malam Ibrahim Musa, Rasuwa. Mahaifinsa mai suna Malam Musa Ibrahim, yayi fama da jinya Wanda har ya kwanta a babban asibitin kasa dake Abuja.

Muna rokon Allah ya Gafarta mashi ya sanya Aljannah ta Zamo makomarshi.

AN FARA SAMUN SASANCI TSAKANIN KUNGIYAR MASU SHIRYA FINA-FINAI DA MA'AIKATAR TACE FINA-FINAI RESHEN JIHAR KANOJaridar ID...
19/05/2025

AN FARA SAMUN SASANCI TSAKANIN KUNGIYAR MASU SHIRYA FINA-FINAI DA MA'AIKATAR TACE FINA-FINAI RESHEN JIHAR KANO

Jaridar IDON MIKIYA, ta samu zantawa kai tsaye da shugaban kungiyar masu shirya Fina-Finai ta kasa (MOPPAN) reshen Jihar Kano, Wato Alhaji Ado Ahmad Gidan DABINO, bisa takardar da kungiyar TA fitar yau Litinin 19 ga watan Mayu 2025, akan zaman sasanci da s**a fara tattaunawa da ma'aikatar tace Fina-Finai s**a fara a inda har s**a cin ma matsaya akan cewa dukkan kanfanonin da ake tuhuma an kara masu mako daya da su ci gaba da nuna fina finan su har zuwa mako me zuwa kafin a cimma matsaya ta bai daya.

Alhaji Ado Ahmad Gidan Dabino, ya shaida mana cewa zasu ci gaba da fafutuka har sai an cimma daidato nan ba da jimawa ba.

WANI ALKALIN A GARIN ZARIYA YANA CIN ZARAFIN JAMA'A A KOTUNSAAlkalin kotun Shari'ah dake cikin garin Zaria, Wato Shari'a...
19/05/2025

WANI ALKALIN A GARIN ZARIYA YANA CIN ZARAFIN JAMA'A A KOTUNSA

Alkalin kotun Shari'ah dake cikin garin Zaria, Wato Shari'ah Court II, Yan Tukwane dake Babban Dodo Zaria, yana cin zarafin jama'ar da suke kawo kara ko korafi a wannan kotu ta Yan Tukwane.

Jama'a da dama suna korafi bisa irin yadda yake tafiyar da yi ma jama'a Shari'ah, inda suke korafin cewa idan har baka bashi kudi ba zai dinga Jan shari'ar komin gaskiyarka, haka nan komi laifin mutum zai iya Kare shi ya kuma bashi gaskiya.

A wata shari'ar da aka kai masa, sai da ya kwashe wata hudu, sannan sai da aka yi shiga sau shida amma Wadanda ake tuhuma da laifin sata, zamba cikin aminci, yunkurin kisan kai basu taba zuwa kotu ba, amma duk da haka ya kyale suna ci gaba da cin zarafin mai kara.

Akwai yunkurin kisan kai Wanda aka soka ma wani bawan Allah wuka a fuska, bayan da Yan sanda s**a gama bincike s**a aiko masa, nan take ya bayar da belin mai lefin ga lauyan sa ba tare da wani rabutu ba, kawai cewa yayi 'tafi da shi na baka belinsa' inda yanzu haka shi me laifin yana can yana walawarshi a gari, inda har yana barazanar babu Wanda ya isa ya taba.

Jama'a dai suna ta Allah wadai da irin yadda wannan Alkalin yake tafiyar da aikin shari'ar shi inda suke ganin k**ar babu kwarewa wasu kuma suna ganin k**ar yana da daurin gindi ne daga sama shi ya sanya yake abinda ya ga dama.

*GOBARA TA TASHI A BABBAR KWALEJIN SHAIKH DAHIRU USMAN BAUCHI* Gobara ta tashi a Babbar Kwalejin Al-ƙur’ani da ilimin Ad...
19/05/2025

*GOBARA TA TASHI A BABBAR KWALEJIN SHAIKH DAHIRU USMAN BAUCHI*

Gobara ta tashi a Babbar Kwalejin Al-ƙur’ani da ilimin Addinin Musulunci ta Sheikh Dahiru Usman Bauchi, da ke Rafin Albasa a Jihar Bauchi.

Jiya Lahadi, 18 ga watan Mayu 2025, ne gobarar tashi a wani sashi na Makarantar inda ta lalata wasu manyan Littafan da Shaikh din ya wallafa da hannun tare da wasu manyan Littafan babban dansa, Wato marigayi Shaikh Dr. Hadi Shaikh Dahiru Usman Bauchi.

Gobarar ba littafai kadai ta lalata ba, Akwai muhimman kayayyakin koyo da koyarwa na musamman da sauran wasu manyan kayan Kwalejin.

KUNGIYAR IZALATUL BIDI'A TA RABA WA MARAYU TALLAFIN ABINCI DA SUTURA A JIHAR KANODaga Ibrahim Muhammad Kano.Kungiyar Iza...
27/03/2025

KUNGIYAR IZALATUL BIDI'A TA RABA WA MARAYU TALLAFIN ABINCI DA SUTURA A JIHAR KANO

Daga Ibrahim Muhammad Kano.

Kungiyar Izalatil Bidi'a reshen jihar Kano karkashin jagorancin Furofesa Imam Abdallah Saleh Pakistan,, kuma shugaban hukumar aikin Hajji ta kasa ta raba kayan abinci da sutura ga marayu.
Taron kaddamar da rabon tallafi an gudanar da shi ne a harabar masallacin Juma'a na marigayi Sheikh Ja'afar Mahmud Adam dake unguwar Tudun Murtala.

Da yake jawabi a madadin shugaban kungiyar Izala na Jihar Kano furofesa Abdalla Saleh Pakistan, wanda ya sami wakilcin mataimakin shugaban kungiyar wato Malam Muhammad Ahmad Usman Bichi, yace a baya shugaban kungiyar ne ke jagorantar rabon tallafin, amma wannan karon saboda hidimar kasa da aka dora masa na aikin hajji bai sami dama ba, don haka yake kaddamar da rabon a madadinsa.

Ya ce ana raba kaya da yawa a baya amma kowane yanayi da yanda yake zuwa, saboda haka abin ya sawwaka shi aka bayar.
Ya ja hankalin al'umma talakawa da masu hali akan su rika kokarin tallafawa marayu da abinda suke dashi domin kullum marayu kara yawa suke zaka tarar akwai mutane da ake tare dasu bara bana babu su sun tafi sun bar marayu.

Malam Ahmad Muhammad Usman Bichi ya yi kira ga masu kula da marayu su daure suyi hakuri su basu tarbiyya ta gari da kyakkyawan kulawa yanda zasu taso su zama masu amfani a cikin al'umma.

A nasa jawabin sakataren kwamitin rabon tallafin marayun.Malam Sani Jibrin Tudun Wada ya ce a bana ma sun tattara, tallafi da suke samu na kwamitin masallaci dana daidaikun mutane da kuma wanda suke samu daga wasu fitattun mutane..

Ya ce daga gudummawa da s**a samu akwai kudi ₦5,000,000 daga Alhaji Aminu Dantata da N1,000,000 daga Alhaji Ibrahim Danyaro . Alhaji Haruna Tahir Hungu N1,000,000 Shugaban hukumar aikin hajji na jasa.Farfesa Imam Abdallah Saleh Pakistan ya bada ₦200,000.

Ya kara da cewa akwai mutane da dama da s**a bada gudunmuwa.Haka Alhaji Auwal Abdullahi Rano bana ya bayar da buhunan shinkafa 150.Tsohon mataimakin Gwamnan Kano Dakta Nasir Yusuf Gawuna na daga wafanda s**a bada gudunmuwa.

Malam Sani Jibrin ya ce a bana an sami tara kaya da kudi na sama da ₦16,000,000 kuma marayu sama da 3000 ne s**a amfana daga kananan hukumomi 44 na jahar Kano.A tsarin ranan na bana, wasu an basu kayan abinci da kudin cefane wasu kuma an basu sutura sannan akwai shiri na horar da marayu akan sana'o'i na dogaro da kai.

Pic .Wani sashe a yayin rabon tallafin marayun da kungiyar Izala ta jihar Kano ta yi.

SABON KWAMISHINAN YAN SANDAN JIHAR KANO YA ZIYARCI  MATAIMAKIN SUFETO JANAR Daga Ibrahim Muhammad.Sabon Kwamishinan Yan ...
24/03/2025

SABON KWAMISHINAN YAN SANDAN JIHAR KANO YA ZIYARCI
MATAIMAKIN SUFETO JANAR

Daga Ibrahim Muhammad.
Sabon Kwamishinan Yan sandan Jihar Kano CP. Ibrahim Adamu Bakori ya kaiwa Mataimakin Sifetan Yan sanda Mai Kula da Shiyya Ta Daya AIG. Ahmed Ammani ziyara a Ofishinsa.

CP. Ibrahim Adamu Bakori yace ya kai ziyarar ne domin samun dabaru da kuma Shawarwari daga AIG Ahmed Ammani kasancewar yana karkashin Kulawarsa.

Yace zai yi aiki Kafada da kadada da Shiyya ta daya domin samun nasarar ayyukan sa a matsayinsa na Sabon Kwamishinan Yan sandan Jihar kano.

Anasa bangaren AIG Ahmed Ammani yace kofarsa a bude take wajen samun goyon baya da hadin kai ga sabon kwamishinan da aka turo Kano wajen sauke nauyin da aka dora masa.

Kakakin Rundunar Yan sandan shiyya ta daya Zone CSP Bashir Muhamad ya aikowa jaridar idon yace, AIG Ahmed Ammani ya kuma bukaci Kwamishinan da sauran masu taimaka Masa suyi aiki da gaskiya da rikon amana da kuma kwarewa wajen kare rayuka da dukiyoyin Al'umama.'

*GWAMNAN JIHAR KANO ABBA KABIR YUSUF, YA RANTSAR DA SABON KWAMISHINAN  GIDAJE* Daga Ibrahim MuhammadGwamna Abba Kabir Yu...
24/03/2025

*GWAMNAN JIHAR KANO ABBA KABIR YUSUF, YA RANTSAR DA SABON KWAMISHINAN GIDAJE*

Daga Ibrahim Muhammad

Gwamna Abba Kabir Yusuf na jihar Kano ya fadada majalisar zartarwarsa tare da rantsar da Ibrahim Yakubu Adamu a matsayin sabon kwamishinan raya gidaje.

A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sanusi Bature Dawakin Tofa ya fitar, babban mai shari’a na jihar Kano, Haruna Isah Dederi ya gudanar da bikin rantsarwar a ranar Litinin.

Kafin nadin nasa, Adamu ya rike mukamin Manajan Darakta na Hukumar Tsare-Tsare da Cigaban Birane ta Kano (KNUPDA).

Da yake jawabi a wajen taron, Gwamna Yusuf ya yaba da kwarewar sabon kwamishinan da irin gudunmawar da ya bayar wajen ci gaban Kano.

Ya bayyana muhimmiyar rawar da Adamu ya taka wajen tsarawa da raya garuruwan Kwankwasiyya, Amana, da Bandirawo tsakanin 2013 zuwa 2015 a karkashin gwamnatin Sanata Rabiu Musa Kwankwaso.

Address

Kaduna
Kaduna

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Idon Mikiya News posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Idon Mikiya News:

Share