ALFIJIR NEWS

ALFIJIR NEWS Idan kuna bukatar tallace - tallace za ku iya tuntubar mu ta wannan lambar kai tsaye kira ko WhatsApp.
👉🏾 08108940039

A yayin da ake ta ce-ce-ku-ce kan zaɓen 2027, Gwamnatin Tarayya ta jaddada cewa Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ba zai b...
09/07/2025

A yayin da ake ta ce-ce-ku-ce kan zaɓen 2027, Gwamnatin Tarayya ta jaddada cewa Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ba zai bari hayaniyar siyasa ta karkatar da shi daga aikin sa na kawo sauye-sauye masu ma’ana da farfaɗo da tattalin arzikin ƙasa domin amfanin ɗaukacin ‘yan Nijeriya ba.

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, shi ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar a Abuja a ranar Talata, inda ya ce gwamnatin na ci gaba da aiwatar da muhimman manufofin da s**a shafi cigaban tattalin arziki da jin daɗin al’umma, tare da nisantar duk wata hayaniya ta siyasa da ka iya janyo koma baya.

Idan an tuna, hayaniya ta turnuƙe kwanan nan kan wata haɗaka da waɗanda 'yan siyasar adawa s**a yi da nufin ƙwace ƙwaryar mulkin ƙasar nan daga hannun gwamnati mai ci yanzu a babban zaɓe mai zuwa.

Idris ya ce: "Ko da yake muna jaddada ‘yancin kowane ɗan Nijeriya na amfani da ‘yancin sa na shiga ko kafa ƙungiya da faɗar albarkacin baki k**ar yadda kundin tsarin mulki ya tanada, yana da muhimmanci a fayyace cewa gwamnatin Shugaba Tinubu ba za ta bari harkokin siyasa ko hayaniyar ‘yan siyasa su karkatar da ita daga aikin da ta sa a gaba ba."

Ministan ya ce ko da yake ana ta raɗe-raɗi a kafafen yaɗa labarai game da sabuwar haɗakar siyasar adawa da ke tasowa, Shugaban Ƙasa Tinubu yana ci gaba da maida hankali ne kan Shirin Sabunta Fata domin ciyar da ƙasa gaba.

"Hayaniya a kafafen yaɗa labarai kan fitowar wata sabuwar haɗakar siyasa abin fahimta ne, amma ‘yan Nijeriya sun damƙa wa Shugaba Tinubu wata gagarumar amanar sauyi, wadda aka gina bisa Shirin Sabunta Fata," inji shi.

A cewar sa, shekaru biyu kacal bayan hawan Tinubu mulki, gwamnatin ta fara samun gagarumin cigaba a fannonin tattalin arziki da tsaro inda ake samun raguwar satar ɗanyen mai, hauhawar farashin kaya na raguwa, Naira na daidaita, da kuma ƙarin ƙwarin gwiwar masu zuba jari a ɓangaren man fetur da gas.

"Fasa bututun man fetur ya ragu ƙwarai, ƙwarin gwiwar masu zuba jari a ɓangaren man fetur da gas na dawowa, hauhawar farashin kaya na raguwa, Naira na samun daidaito, ana fuskantar matsalolin tsaro kai-tsaye, kuma miliyoyin ‘yan Nijeriya — iyalai, ɗalibai, masu aikin hannu, da ‘yan ƙananan sana’o’i — na amfana daga shirye-shirye irin su lamunin karatu, samun bashi na kayayyakin masarufi, sauya motocin haya zuwa masu aiki da iskar gas, da ingantattun ayyukan gwamnati da ababen more rayuwa," inji Ministan.

Ya kuma bayyana wasu muhimman matakai da aka ɗauka kwanan nan, ciki har da rattaba hannu kan dokoki huɗu na gyaran haraji da za a fara aiwatar da su daga shekarar 2026, da kuma ƙaddamar da mafi girman shirin amfani da injuna a aikin gona da aka taɓa yi a Nijeriya.

"Makonni biyu da s**a wuce, Shugaban Ƙasa ya rattaba hannu kan dokoki huɗu masu muhimmanci na gyaran haraji, wanda ke zama ɗaya daga cikin manyan sauye-sauyen tsarin kuɗi da aka taɓa yi a tarihin Nijeriya. Ana sa ran waɗannan gyare-gyare za su haɓaka walwala da cigaban iyalai da ‘yan kasuwa a faɗin ƙasar nan," inji shi.

"Kafin hakan, Shugaban Ƙasa ya ƙaddamar da mafi girman shirin amfani da injuna a aikin gona da aka taɓa yi a tarihin Nijeriya — wanda ya kasance fara aiwatar da Shirin Sabunta Fata na amfani da injuna a aikin gona. Wannan kuwa yana daga cikin jerin manyan shirye-shiryen amfani da injuna a aikin gona da ake aiwatarwa domin tabbatar da wadatar abinci," inji shi.

Ministan ya zargi wasu ‘yan siyasa da ƙoƙarin dagula hankali domin a ɗauke hankalin gwamnati daga cigaban da ake samu. Ya ce gwamnati ba za ta amince da hakan ba.

"Ba abin mamaki ba ne cewa sababbin haɗakar siyasa da ƙungiyoyin adawa ba sa son a ci gaba da maida hankali kan irin cigaban da Nijeriya take samu. Sai dai gwamnati ba za ta bari a jawo ta cikin hayaniyar da waɗanda ke son Nijeriya ta tsaya cak maimakon ta ci gaba da samun sauyi s**a ƙirƙira ba," inji shi.

A ƙarshe, Idris ya tabbatar da cewa gwamnatin Tinubu za ta ci gaba da aiwatar da ƙudirin ta na inganta rayuwar al’umma.

Ya ce: "Gwamnatin Tinubu tana maida hankali sosai tare da jajircewa wajen gina Nijeriya mai wadata ga kowa da kowa."

Buri Na Kayan Hatsi Su Ci Gaba Da Karye Wa A Najeriya - Matashi Aminu
08/07/2025

Buri Na Kayan Hatsi Su Ci Gaba Da Karye Wa A Najeriya - Matashi Aminu

TÁLLAH: Manhajar Ksbdata Ya Kawo Maku Tsarika Masu Sauki Kan FarashiIdan Ku Ká Fará Amfäní Da Kamfanín Käsuwancín Datá D...
08/07/2025

TÁLLAH: Manhajar Ksbdata Ya Kawo Maku Tsarika Masu Sauki Kan Farashi

Idan Ku Ká Fará Amfäní Da Kamfanín Käsuwancín Datá Da Katín Wayá Na KSBDATA Ba Za Ku Sáke Amfäní Da Wani Kamfanín Ba

Duba línk a comment section
👇👇👇

Ina masu sána'ar dáta da katín wáya ga dama ta samu, KSBDATA mun shírya ba ku ríbá mai yawa, za ku iya síyan dáta ku saka wa kánku da wannan ápplícatíon ɗin námu na KSBDATA, muddin ku ka fára amfani da KSBDATA ba za ku iya daínawa ba saboda íngancín dátar mu.

Dámúwárku game da mátsálár dáta ko sáyán katín wáya ta zo ƙarshe idan har ku ka fará aíki da mánhájármu ta Ksbdata wato ‘Applícátíon na Kamfanín ‘KSBDATA. Dátar mu tana da ingancí sosai za ku jima kuna amfani da íta ba ta ƙare ba.

Ku sáuke “Applícátíon” ɗin mu na Ksbdata a “Pláystore” zuwa kán wáyoyínku:

Duba línk a comment section
👇👇👇

AL-AJWA Magani Ne Dake Wulaƙanta Tsutsar Ciki Da Macijin Ciki Nan Take Wannan maganin yana magunguna k**ar haka, tsutsar...
08/07/2025

AL-AJWA Magani Ne Dake Wulaƙanta Tsutsar Ciki Da Macijin Ciki Nan Take

Wannan maganin yana magunguna k**ar haka, tsutsar ciki, macijin ciki, dattin mara, basir, matacciyar majina, rashin cin abinci, dattin ciki, yawan tashin zuciya, wannan magani yana wanke dukan wani dattin ciki.

Kuma wannan maganin yana zuwa da murfi kala-kala k**ar yadda kuke ganin hoton maganin, muna tura kaya ga masu sari a duk inda suke a faɗin Nijeriya da sauran ƙasashe, mai kaya ne zai biya mai mota.”

Bayan haka wannan Kamfani yana bada magunguna na musamman k**ar haka, ciwon hàntà, cìwòn zùcìyà, ciwon ƙòdà, cìwon hunhu, hawan jini.

Domin shiga shafin FALAKIN ZAMANI TV wato sanin hakikanin BURUJIN KA da sanin hanyar arzikin ka da sana'ar da tafi dacewa dakai da matar da tafi dacewa dakai,da masu son sanin hakikanin larurar da suke fama da ita,etc,to ka shiga wannan link din
👇🏽
https://www.facebook.com/share/12KM5Z9s5cm/

Don neman karin bayani
👇🏽
Call & WhatsApp:
08060738621
08092178079
Email:
👇🏽
Email:[email protected]

Mali ta zama kasa ta farko a fadin Afirika da ba'abinta bashi, ta biya duk basuss**a da wata kasa daga waje ko wata ma'a...
08/07/2025

Mali ta zama kasa ta farko a fadin Afirika da ba'abinta bashi, ta biya duk basuss**a da wata kasa daga waje ko wata ma'aikata na cikin gida ta ke binta.

Al'ummar Samaru A Zariya Sun Gabatar Da Sallar Rokon Ruwa.Da safiyar yau Talata 8/08/2025 al'ummar garin Samarun Zariya ...
08/07/2025

Al'ummar Samaru A Zariya Sun Gabatar Da Sallar Rokon Ruwa.

Da safiyar yau Talata 8/08/2025 al'ummar garin Samarun Zariya Jihar Kaduna da kewaye su ka fito Sallar rokon ruwa.

Babban malamin addinin Musulunci na garin Samaru Imam Shamwilu Muhammad Nasir, ya bayyana cewar Sallar rokon ruwa Sunnah ce, Inda ya yi kira ga al'ummar Musulmi da aji tsoron Allah a tuba a daina zalunci da cin amana, a wasu lokuta sabon Allah na jawo rashin ruwa a kasa duk a cikin jawaban malamin.

TALLA: Domin fara sána'ár DATA ko kuma ku dinga saka wa kanku, ku sáuké Mánhájar KSBDATA a PláyStore.
👇👇👇
https://play.google.com/store/apps/details?id=com.ksbdata.app

Website
👇👇👇
https://app.ksbdata.com

WhatsApp
👇👇👇
https://wa.me/2349018986971

DA DUMI DUMI: Kungiyar Malaman Jami'oi Za Ta Tsunduma Yajin Aiki.Kungiyar malaman jami'oi ta Najeriya ASUU, ta fara shel...
08/07/2025

DA DUMI DUMI: Kungiyar Malaman Jami'oi Za Ta Tsunduma Yajin Aiki.

Kungiyar malaman jami'oi ta Najeriya ASUU, ta fara shelan tsunduma yajin aiki a Najeriya na har sai mama ta gani saboda rashin kyakyawar albashi ga malaman jami'oin Najeriya da suke fama da shi a kasar nan.

TALLA: Domin fara sána'ár DATA ko kuma ku dinga saka wa kanku, ku sáuké Mánhájar KSBDATA a PláyStore.
👇👇👇
https://play.google.com/store/apps/details?id=com.ksbdata.app

Website
👇👇👇
https://app.ksbdata.com

WhatsApp
👇👇👇
https://wa.me/2349018986971

'Yan Wasan Kano Pillers Sun Rabauta Da Sabbin Motoci Daga Ahmad Musa.Ahmad Musa ya raba wa wasu daga cikin 'yan wasa na ...
08/07/2025

'Yan Wasan Kano Pillers Sun Rabauta Da Sabbin Motoci Daga Ahmad Musa.

Ahmad Musa ya raba wa wasu daga cikin 'yan wasa na Kano Pillers sababbin motoci kirar “Land Cruiser“ jim bayan k**a aiki a babban ofishinsa na Shugaban Ƙungiyar ta kwallon kafa din wato Kano Pillers da gwamnar Jihar Kano Eng. Abba Kabir Yusuf ya nadasa.

TALLA: Domin fara sána'ár DATA ko kuma ku dinga saka wa kanku, ku sáuké Mánhájar KSBDATA a PláyStore.
👇👇👇
https://play.google.com/store/apps/details?id=com.ksbdata.app

Website
👇👇👇
https://app.ksbdata.com

WhatsApp
👇👇👇
https://wa.me/2349018986971

Ahmed Musa Ya Shiga Ofis A Matsayin Sabon Shugaban Kano Pillars.Fitaccen ɗan wasan ƙwallon ƙafa a Nijeriya Ahmed Musa MO...
08/07/2025

Ahmed Musa Ya Shiga Ofis A Matsayin Sabon Shugaban Kano Pillars.

Fitaccen ɗan wasan ƙwallon ƙafa a Nijeriya Ahmed Musa MON, ya k**a aiki a matsayin sabon shugaban gudunmawar na Kano Pillars a ranar Litinin, inda ya yi alkawarin farfaɗo da martabar kulob ɗin.

A taron da ya jagoranta a karon farko tare da shugabannin kulob ɗin, Musa ya bayyana niyyarsa na sauya fasalin Pillars zuwa matakin duniya, yana mai tabbatar da cewa haɗin kan abokan aiki gami da ƙwarin gwiwa da kuma gogewa da ƙwarewar da ya ke da su za su taka rawa wajen cimma wannan buri.

TALLA: Domin fara sána'ár DATA ko kuma ku dinga saka wa kanku, ku sáuké Mánhájar KSBDATA a PláyStore.
👇👇👇
https://play.google.com/store/apps/details?id=com.ksbdata.app

Website
👇👇👇
https://app.ksbdata.com

WhatsApp
👇👇👇
https://wa.me/2349018986971

Ku Daina Roƙa Wa Buhari Masifa- Mawaƙi Usman Nasir MandelaFitaccen Mawakin siyasa Usman Nasir Mandela ya yi addu'ar Alla...
07/07/2025

Ku Daina Roƙa Wa Buhari Masifa
- Mawaƙi Usman Nasir Mandela

Fitaccen Mawakin siyasa Usman Nasir Mandela ya yi addu'ar Allah ya ba tsohon shugaban ƙasa Muhammadu Buhari lafiya.

Mawaƙin ya yi kira ga al'umma su dena roƙawa Buhari masifa, domin Allah baya karɓar mummunar addu'a, kuma ko ba komai Buhari Musulmi ne, Inji shi.

Address

RC: 6941227, SUIN: 1931538, No 31 'Yan Tabarmi Zariya

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when ALFIJIR NEWS posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Shortcuts

  • Address
  • Alerts
  • Claim ownership or report listing
  • Want your business to be the top-listed Media Company?

Share