ALFIJIR NEWS

ALFIJIR NEWS RC NO: 6941227

Ku Saya Data Mai Inganci Da Arhar A Wurin Mu A Manhajar Ksbdata.Ina masu sana'ar data  da katin waya ga dama ta samu KSB...
14/05/2026

Ku Saya Data Mai Inganci Da Arhar A Wurin Mu A Manhajar Ksbdata.

Ina masu sana'ar data da katin waya ga dama ta samu KSBDATA mun shirya ba ku rìbà mai yawa, za ku iya siyan data ku saka wa kanku da wannan application din namu na KSBDATA, muddin kuka fara amfani da KSBDATA ba za ku iya dainawa ba saboda ingancin datarmu.

Dàmùwàrku game da màtsàlàr data ko sàyàn katin waya ta zo ƙarshe idan har kuka fara aiki da manhajarmu ta Ksbdata’ wato ‘Application na kamfanin ‘KSBDATA. Datarmu tana da inganci sosai za ku jima kuna amfani ba ta ƙare ba

Ku sauke “Application” ɗin mu na ksbdata a “Playstore” zuwa kan wayoyinku.
👇🏽
https://play.google.com/store/apps/details?id=com.ksbdata.app

Ku tuntuɓe mu ta WhatsApp
👇🏽
https://wa.me/2349018986971

TIRKASHI: An Bankado Shekarun Hon Abun Al'ajabin Zazzau..Wani Fasfo dake Yawo a Yanar Gizo ya bayyana gaskiyar Shekarun ...
14/05/2026

TIRKASHI: An Bankado Shekarun Hon Abun Al'ajabin Zazzau..

Wani Fasfo dake Yawo a Yanar Gizo ya bayyana gaskiyar Shekarun Abun Al'ajabin Zazzau Hon Mahmud Sadis Buba,inda ya nuna an Haifeshi a Shekara ta 2010,wanda zuwa yau Shekarunsa 16 kenan.

A wata Tattaunawa da aka yi da Hon Abun Al'ajabin Zazzau ya bayyana cewa Shekarunsa 30,Lamarin da ya Haifar Da Ce-ce-ku-ce,Sai gashi An samu Fasfo mai Dauke da Sahihan Bayanai akansa dake Nuni da Gaskiyar Shekarunsa 13.

A Dokar Zabe a Nijeriya Sai Mutum ya kai Shekaru 25 kafin ya iya Tsayawa Takara. Bisa haka jama'a ke tambaya ina Makomar Form din da Abun Al'ajabi ya siya bayan ta bayyana Cewa Shekarunsa 13?

Me za ku ce?

Jam'iyyar ADC A Zariya Za Ta Gudanar Da Gagarumin Taro.Jam'iyyar ADC reshen karamar hukumar Zariya Na farin cikin gayyat...
14/05/2026

Jam'iyyar ADC A Zariya Za Ta Gudanar Da Gagarumin Taro.

Jam'iyyar ADC reshen karamar hukumar Zariya Na farin cikin gayyatar Al-ummar garin Zaria tare da dukkan ‘ya’yan jam'iyyar ADC na Karamar Hukumar Zaria zuwa babban taron karrama shugabannin ƙaramar Hukumar Zaria tare da shugabannin gundumoni 13 na karamar Hukumar Zaria, wanda shugabannin ƙungiyar ADC National update matakin Karamar Hukumar Zaria s**a shirya.

Za a gudanar da taron ne kamar haka:

🗓 Rana : Lahadi, 18/05/2026
⏰ Lokaci v 10:00 na safe
📍 Wuri......

Domin Karin bayani zaku iya tun tubar nambobi kamar haka:

(1)Abdulkarim Adam
08035126501
(Chairman)

(2)BATURE ISHAK ABDU
0903 791 5747
(Secretary)

Allah Ya bada ikon halarta. Amin.

✍️ Sanarwa:
Prince Kabir Sani Yero
(TREASURER)
ADC National Update Zaria L.G chapter

DA DUMI-DUMI ll Yadda uwargidan Gwamnar Jihar Bauchi Aisha Bala Abdulkadir ta kai ziyarar bazata zuwa Makarantar Sheikh ...
14/05/2026

DA DUMI-DUMI ll Yadda uwargidan Gwamnar Jihar Bauchi Aisha Bala Abdulkadir ta kai ziyarar bazata zuwa Makarantar Sheikh Juanidu Bauchi wato Al-irfan domin dubiyar dalibai da kuma lura da yanayin kwazon daliban da dai makamantansu.
TALLAH: KSBDATA kamfanin da ya yi fice wajen kasuwancin data da katin waya

Domin fara sana'ar DATA ko kuma ku dinga saka wa kanku, ku sauke Manhajar KSBDATA a PlayStore.
👇🏽
https://play.google.com/store/apps/details?id=com.ksbdata.app

Ku tuntuɓe mu ta WhatsApp
👇🏽
https://wa.me/2349018986971

DA DUMI-DUMI ll Wannan yarinya Hadiza Gabon babu abinda zance mata sai dai Allah ya saka mata da alkairi.Abubuwan da tak...
14/05/2026

DA DUMI-DUMI ll Wannan yarinya Hadiza Gabon babu abinda zance mata sai dai Allah ya saka mata da alkairi.

Abubuwan da take min a boye ba tare da ma tana so wani ya sani ba suna da yawa, baya ga tallafa min a rashin lafiya ta, hatta gidan da nake ciki dakuna kusan uku da kudinta na samu na rufa su.

Haka kawai take zuwa a boye gidana timing alkairi ba tare da kowa ya sani ba, ni dai Hadiza yata ce amma a Kannywood ta zama uwa gareni mai share min kuka

Inji jarumin Kannywood Sani Moda
TALLAH: KSBDATA kamfanin da ya yi fice wajen kasuwancin data da katin waya

Domin fara sana'ar DATA ko kuma ku dinga saka wa kanku, ku sauke Manhajar KSBDATA a PlayStore.
👇🏽
https://play.google.com/store/apps/details?id=com.ksbdata.app

Ku tuntuɓe mu ta WhatsApp
👇🏽
https://wa.me/2349018986971

DA DUMI-DUMI ll Shugaban ƙasar Ruwanda, Paul Kagame, ya karɓi baƙuncin Shugaba Bola Ahmed Tinubu a fadar shugaban ƙasa t...
14/05/2026

DA DUMI-DUMI ll Shugaban ƙasar Ruwanda, Paul Kagame, ya karɓi baƙuncin Shugaba Bola Ahmed Tinubu a fadar shugaban ƙasa ta Urugwiro.
TALLAH: KSBDATA kamfanin da ya yi fice wajen kasuwancin data da katin waya

Domin fara sana'ar DATA ko kuma ku dinga saka wa kanku, ku sauke Manhajar KSBDATA a PlayStore.
👇🏽
https://play.google.com/store/apps/details?id=com.ksbdata.app

Ku tuntuɓe mu ta WhatsApp
👇🏽
https://wa.me/2349018986971

14/05/2026

Akwai matsala fa!

Samarin yanzu yawancinsu iya matakin secondary suke tsaya da karatu su tafi Neman kudi.

DA DUMI-DUMI ll Nijeriya za ta ƙaddamar da sabon tsarin watsa shirye-shiryen talbijin daga analog zuwa dijital a Yuni - ...
13/05/2026

DA DUMI-DUMI ll Nijeriya za ta ƙaddamar da sabon tsarin watsa shirye-shiryen talbijin daga analog zuwa dijital a Yuni - Idris

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya bayyana cewa shirin nan da aka daɗe ana jira na sauya tsarin watsa shirye-shiryen talbijin daga analog zuwa dijital (wato Digital Switch Over, DSO) a Nijeriya, an kammala shi tsaf, sai ƙaddamarwa a watan gobe.

Ministan ya bayyana haka ne lokacin da ya kai ziyarar musamman a cibiyoyin aiki na NIGCOMSAT da ke Cibiyar Sararin Samaniya ta Obasanjo a Abuja ranar Laraba.

Da yake bayyana wannan cigaban a matsayin wani muhimmin sauyi a fannin watsa shirye-shirye a Nijeriya, Ministan ya bayyana lamarin da wani babban cigaba a ajandar gyaran da Shugaba Bola Ahmed Tinubu yake yi a fannin yaɗa labarai.

Ya ce: “Ina ganin wannan wata sabuwar alfijir ce ga ƙasar mu. Alƙawarin da Shugaba Tinubu ya yi na gyaran dukkan fannoni yanzu ana ganin yadda ake aiwatar da shi a masana’antar watsa shirye-shiryen talbijin.”

Ya ƙara da cewa bayan shekaru masu yawa ana jinkiri, yanzu Nijeriya ta shirya kammala sauya tsarin daga analog zuwa dijital, yana mai cewa za a ƙaddamar da tsarin na DSO ne a ranar 17 ga Yuni, 2026.

Da yake bayani kan alfanun sabon tsarin, Ministan ya ce: “Wannan zai kawo fa’idoji masu yawa ga gidajen watsa shirye-shirye, masu kallo, da masu talla. Idan ana kallon wata tasha ta musamman, za a san su wanene ke kallo, abin da suke kallo, da kuma yawan masu kallon.”

A cewar sa, sabon tsarin zai samar da ingantattun bayanai da nazarin masu kallo, wanda zai taimaka wa masu talla da gidajen watsa shirye-shirye wajen yanke shawara mai kyau kan shirye-shirye da zuba jari, tare da inganta isar da abubuwan kallo ga ’yan Nijeriya.

Idris ya jaddada tasirin wannan shiri ga tattalin arziki da fasaha, yana mai cewa tsarin zai ƙara haifar da gasa a masana’antar watsa shirye-shirye, ya faɗaɗa damar kallon talbijin kyauta, tare da ɗaga ingancin kallo a Nijeriya da yankin Afrika mai hamadar Sahara.

Ya ce: "An karya tsarin mamayar kamfani guda a fagen. Kowa zai shiga gasa. Abubuwan kallo za su ƙaru, masu kallo za su ƙaru, kuma Nijeriya yanzu tana komawa daga SD zuwa HD wajen watsa shirye-shirye.”

Ya ƙara da cewa yanzu ’yan Nijeriya za su more ingantaccen siginar talbijin ta satalayit, wato tauraron ɗan'adam, da kuma manhajojin wayar hannu da fasahar NIGCOMSAT take samarwa.

A nasa jawabin a yayin ziyarar, Darakta-Janar na Hukumar Kula da Watsa Shirye-shiryen Rediyo da Talbijin ta Ƙasa (NBC), Mista Charles Ebuebu, ya ce an yi sabon tsarin DSO ne domin ya dace da sababbin fasahohi da yadda mutane suke kallon shirye-shirye a wannan zamani.

Ya bayyana cewa sabon tsarin yana amfani da watsa shirye-shiryen satalayit da manhajojin wayar hannu domin tabbatar da cewa jama’a a ko’ina za su iya samun damar amfani da shi, ba kamar tsohon gwajin DSO da ya tsaya a wasu birane kaɗai ba.

Ya ce: “Za mu fara da tashoshi 100 a ranar ƙaddamarwa, ko ma fiye da haka, domin masu samar da abubuwan kallo da dama suna tattaunawa da mu. Muna son samar da kasuwa guda da dandali guda ga Nijeriya.”

Ya bayyana cewa an kafa cibiyoyin samar da shirye-shirye na yankuna daban-daban da cibiyoyin tallafin kwastomomi masu harsuna daban-daban a faɗin ƙasar nan.

Ita ma da take jawabi yayin ziyarar, Manajar Darakta kuma Shugabar NIGCOMSAT, Jane Egerton-Idehen, ta bayyana haɗin gwiwar NIGCOMSAT da NBC a matsayin dabarar haɗin kai mai ƙarfi da ta inganta ayyuka da ɗaga ƙa’idojin aiki a fannin watsa shirye-shiryen dijital a Nijeriya.

A cewar ta, zuba jari da ake ci gaba da yi da kuma shirye-shiryen faɗaɗa ayyukan satalayit a ƙarƙashin wannan gwamnati za su tabbatar da ingantaccen cigaba da bayar da gamsasshen sabis.

Ta ce, “Aikin fa yanzu ne kawai ya fara. Aikin fa yanzu ne kawai ya soma."

Daga cikin waɗanda s**a raka Ministan a ziyarar akwai Darakta Janar na Hukumar Talbijin ta Nijeriya (NTA), Salihu Abdullahi Dembos; Darakta Janar na Muryar Nijeriya (VON), Jibrin Baba Ndace; Darakta Janar na Gidan Rediyon Tarayyar Nijeriya (FRCN), Mohammed Bulama, da Darakta Janar na Hukumar Wayar da Kai (NOA), Lanre Issa-Onilu, tare da sauran manyan jami’an gwamnati da manyan baƙi.

Address

RC: 6941227, SUIN: 1931538, No 31 'Yan Tabarmi Zariya
Kaduna

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when ALFIJIR NEWS posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share