Adamsy Gimbiya News24

Adamsy Gimbiya News24 Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from Adamsy Gimbiya News24, Newspaper, KADUNA, Kaduna.

SUBHANALLAHI! KO KUNSAN MASIFAR DA SHEIK SANI KHALIFA KE CIKI TAFI WACCE EL-RUFAI KE CIKI👇Juyin Mulki (Coup)Juyin mulki ...
23/02/2026

SUBHANALLAHI! KO KUNSAN MASIFAR DA SHEIK SANI KHALIFA KE CIKI TAFI WACCE EL-RUFAI KE CIKI👇

Juyin Mulki (Coup)
Juyin mulki ana daukarsa a matsayin:
-Barazana ga tsaron kasa
-Cin amanar kasa
-Yunkurin kifar da gwamnati

A kasashe da dama, hukuncinsa na iya kaiwa:
-Daurewa na dogon lokaci
Rai da rai (life imprisonment)
-Ko hukuncin kisa a wasu kasashe

Misali:
A Nigeria, juyin mulki ana daukarsa babban laifi na cin amanar kasa.

A Turkey bayan yunƙurin juyin mulki na 2016, an daure dubban mutane.

Satar Kudi (Financial Crime / Corruption)
Satar kudi ma babban laifi ne, amma yawanci:

-Ana iya samun beli
-Ana iya daure mutum shekaru
-Wani lokaci ana iya kwato kudin a rage hukunci

Misali:
A Brazil an daure manyan shugabanni kan zargin cin hanci.

A South Africa ma an gurfanar da tsofaffin shugabanni kan cin hanci.

Don haka wa yafi shiga matsala?

✔ Idan aka tabbatar:
- Juyin mulki yafi hadari kuma hukuncinsa yafi tsanani.
- Satar kudi ma laifi ne mai tsanani,

amma yawanci baya kaiwa matakin hukuncin juyin mulki.

Jama’a Sun Bukaci A Binciki Zargin Tsadar Kuɗaɗen Jinya a Asibitin Dantsoho Memorial College, Kaduna.An fara samun koraf...
04/02/2026

Jama’a Sun Bukaci A Binciki Zargin Tsadar Kuɗaɗen Jinya a Asibitin Dantsoho Memorial College, Kaduna.

An fara samun korafe-korafe daga wasu jama’a a Jihar Kaduna dangane da yadda ake tafiyar da ayyukan jinya a Asibitin Dantsoho Memorial College, inda suke zargin cewa ana ɗora wa marasa lafiya kuɗaɗe masu yawa.

Masu korafin sun bayyana cewa ana karɓar kuɗin gadon asibiti har kimanin ₦30,000, tare da kuɗin buɗe kati da ake cewa ya kai ₦10,000. Sun ce irin wannan tsari na sanya wasu marasa lafiya cikin ƙunci, musamman masu ƙaramin ƙarfi.

Haka zalika, wasu daga cikin masu amfani da asibitin sun yi zargin cewa ba a amince da biyan kuɗi ta hanyar transfer ko amfani da POS, sai dai a biya kuɗi da hannu. Sun ce hakan na ƙara jefa su cikin wahala, musamman idan ba su da tsabar kuɗi a hannu.

Wasu daga cikin jama’ar sun bayyana cewa saboda waɗannan matsaloli, wasu na zaɓar zuwa asibitocin kuɗi, inda suke ganin ana ba su kulawa mai kyau duk da bambancin kuɗin jinya bai yi yawa ba.

Har zuwa lokacin tattara wannan rahoto, ba a samu martani daga mahukuntan asibitin ko hukumomin lafiya na jihar ba. Jama’a na ci gaba da kira ga gwamnati da ta binciki lamarin domin tabbatar da ingantacciyar.... kulawar lafiya ga al’umma.

Labarin Abin Da Dalung Ya Ji Daga Wani Dan Fashi👇👇A daren wata Talata, Solomon Dalung – tsohon Ministan Wasanni – ya zau...
29/11/2025

Labarin Abin Da Dalung Ya Ji Daga Wani Dan Fashi👇👇

A daren wata Talata, Solomon Dalung – tsohon Ministan Wasanni – ya zauna cikin nutsuwa yana yawo a TikTok k**ar kowa. Ba ya zaton wannan nishaɗi zai kai shi ga tattaunawa da wani mutum da ya ce kansa ɗan fashi ne, mai rayuwa a cikin dazuzzuka.

Cikin sanyin murya, matashin ya gaya masa:

“Sunana ba muhimmanci bane. Amma ka sani, ni ɗan fashi ne daga daji.”

Dalung ya tsaya. Sha’awa da mamaki s**a lullube shi. Ya ce ya tsinci kansa yana tambaya:

“To me ya sa kuke kashe mutane?”

Matashin ɗan fashin ya ja dogon numfashi, k**ar wanda yake tuna wani zafi a zuciyarsa.

“Ai suma suna kashe mu,” in ji shi.
“’Yan sa-kai suna kwace mana shanu, suna kashe ‘yan uwammu. Don haka mu ma muka ɗauki makami muka koma daji.”

Dalung ya cigaba da tambaya cikin mamaki:

“Amma ku ma kuna kashe Fulani k**ar ku, kuna sace musu shanu.”

Sai saurayin ya yi murmushin da ya cika da tsoro da rashin tausayi.

“Fulani da muke sani na cikin daji ne. Duk wanda ya koma gari – ba Fulani ba ne. Idan muka gan su, ko sun ce Fulani ne, za mu kashe su.”

Wannan magana ta sa jikin Dalung ya yi sanyi. Ya yi shiru na ɗan lokaci kafin ya sake tambaya:

“To ta yaya za mu kawo ƙarshen wannan kashe-kashe?”

Matashin ya gyara zamansa, ya dubi kyamarar wayarsa tamkar yana kallon Dalung a ido:

“Idan gwamnati tana son zaman lafiya, za mu tattauna. Za mu iya aje mak**ai. Amma sai dai a zo da gaskiya.”

Dalung ya ce abin da ya fi firgita shi ba kalaman saurayin bane, sauƙin yadda yake magana, k**ar wanda yake da tabbacin cewa babu wanda zai iya shafar sa.

A ƙarshe, Dalung ya yi kira ga majalisar dokoki da ta gyara kundin tsarin mulki; ya ce lokaci ya yi da ’yan kasa su samu damar mallakar makami domin kare rayukansu daga irin waɗannan ɓarayi.

Yadda Wani Kansila Ya Gwangwaje Wasu Mutane Da Tallafin Naira Dubu Dubu Domin Rage Radadin Rayuwa.
28/11/2025

Yadda Wani Kansila Ya Gwangwaje Wasu Mutane Da Tallafin Naira Dubu Dubu Domin Rage Radadin Rayuwa.

In kana da waɗannan Applications a wayarka…💰 to kai a cikin masifa kake, kuma Allah kaɗai yasan ranar da zaka fita!Okash...
18/11/2025

In kana da waɗannan Applications a wayarka…💰 to kai a cikin masifa kake, kuma Allah kaɗai yasan ranar da zaka fita!

Okash
Easemoni
Easy Money
PalmPay (Credit)
Kasha-Kash
RenMoney
FairMoney
PalmCredit
Kudi
NewsCredit
FlashCredit
Branch
SilkLoan
Keke Cash
Nemo Money
KashFlex
Pocket Loan
Carbon
Flexi Cash
Cowrywise
9Credit
Pal Loan
TLoan

Waɗannan su ne manyan apps ɗin da ke ba mutane bashi daga ₦2,000 zuwa ₦500,000, ta hanyar Online. Suna bada bashin ne tare da masifar kuɗin ruwa marar fasali,ga takura da ƙarin kuɗin ruwa na kusan 20% ko wacce ranar akan abinda ka karba in baka biya akan lokaci ba.
A zahiri, wadannan loan apps suna lalata rayuwar mutane fiye da yadda ake tunani.
Da zarar ka fara karɓar bashi daga cikinsu, shikenan baza ka iya dainawa ba.

Yawanci waɗannan Loan Apps ɗin masu shi daga! 👇
⚠️ Yan damfara (Yahoo boys)
⚠️ Loan Sharks masu cin moriyar arzikin mutum ta hanyar matsi

Idan kana amfani da su, ka kula sosai kada su jefa ka cikin halaka.
Idan baka fara ba, ka guje musu gaba ɗaya.

Wallahi karɓar bashi a waya babbar masifa ne.. A kiyaye.

Allah Ya tsare mu. ✅

AYYUKAN GAGGAWA GUDA (5) BIYAR DA AKESO AYIMA WANDA KARE YA CIZA. (Gudun Kamuwa Da Cutar Rabies Virus).1. Wanke rauni na...
01/11/2025

AYYUKAN GAGGAWA GUDA (5) BIYAR DA AKESO AYIMA WANDA KARE YA CIZA.

(Gudun Kamuwa Da Cutar Rabies Virus).

1. Wanke rauni nan da nan:

Wanke yankin da abin ya shafa nan da nan tare da sabulu mai tsabta da ruwa na akalla mintina 15 Wannan yana taimaka wajan fitar da kwayar cutar.

2. Shafa Ruwan Sifirit ko aidin:

Bayan tsaftace rauni, ana amfani da Sifirit ko alcohol, dettol ko aidin a kai don hakan na cire ƙwayoyin cutar, domin akawar da su.

3. Aziyarci Babbar asibiti mafi kusa kai tsaye:

Atuntuɓi likita kuma ku gaya masa cewa kare ne yayi cizo, koda kuwa raunin karamine ne.

4. Yana da matukar muhimmanci a fara alurar riga kafi.

Yawancin lokaci jadawalin masu zuwa shine:

Rana ta 0: Alurar rigakafin farko.
Rana ta 3: rigakafi na biyu
Rana ta 7: Alamar ta uku
Rana ta 14: rigakafi huɗu.
Rana ta 28: Alurar-biyar ta al'ada.

5. Anayin Alurrar (Rabies Immunoglobulin) Ga wanda yasamu cizon kare mai zurfi ko a kan wani yanki mai mahimmanci k**ar fuskar, wuya ko hannaye.
(sau ɗai kawai akeyinta a ranar da akayi cizon).

Don kariya daga cutar Rabbies Virus.

BABBAN MUHIMMIN LAMARI SHINE:-

Karka taɓa jinkirta karbar magani.

Kar ka dogara da magungunan gargajiya.

Kammala karbar maganin rigakafi, koda kuwa ciwon yafara warkewa.

Allah ya tsaremu baki daya..!!!

Gwamnatin Kano ta sauyawa makarantar mata ta Mai Kwatashi matsuguni zuwa Kaura Goje Ma'aikatar Ilimi ta Jihar Kano ta ɗa...
28/10/2025

Gwamnatin Kano ta sauyawa makarantar mata ta Mai Kwatashi matsuguni zuwa Kaura Goje

Ma'aikatar Ilimi ta Jihar Kano ta ɗauke Karantar Sakandare ta Mata ta Mai Kwatashi daga titin France Road, Sabongari zuwa unguwar Kaura Goje a karamar hukumar Nassarawa.

Freedom Radio ta rawaito cewa Gwamnan jihar, Abba Kabir Yusuf ne ya bada umarnin sakewa makarantar matsuguni biyo bayan koken ƴan unguwar Kaura Goje da kewayenta akan zargin yadda ake wa ɗaliban makarantar kwace da sauran su.

Tuni dai kungiyar cigaban unguwannin Kaura Goje, Gwagwarwa, Gawuna, Riga, da Gamar Fulani ta mika sakon godiya ga Gwamna Yusuf bisa cika alƙawarin sauyawa makarantar.

Mazauna unguwannin sun nuna farin ciki yadda aka kai makarantar kusa da su, musamman ma ganin cewa ta mata ce, inda su ka nuna cewa hakan zai kara habaka ilimin mata a yankin nasu.

~ Daily Nigerian

Sulhu Da Ƴan Bindiga Ya Gudana a FaskariAn gudanar da wani zaman tattaunawa da sulhu da ƴan bindiga a garin Faskari na J...
15/09/2025

Sulhu Da Ƴan Bindiga Ya Gudana a Faskari

An gudanar da wani zaman tattaunawa da sulhu da ƴan bindiga a garin Faskari na Jihar Katsina, inda aka samu halartar Ado Aleru tare da mabiyansa Fulani.

Wannan mataki na zuwa ne a ƙoƙarin rage tashin hankali da inganta tsaro a yankin, wanda ya daɗe yana fama da matsalar hare-hare da satar mutane.

Masu lura da al’amuran tsaro sun bayyana cewa nasarar wannan sulhu za ta dogara ne da yadda bangarorin biyu za su tsaya a kan yarjejeniyar da aka cimma.

Al’umma dai na cigaba da roƙon Allah Ya tabbatar da zaman lafiya mai ɗorewa a Katsina da ƙasar baki ɗaya.

“Na Je Ziyara Na saci Kaya” – An Cafke Saurayi A KatsinaWani saurayi ya gamu da cikas a soyayyarsa bayan da rundunar ’ya...
09/09/2025

“Na Je Ziyara Na saci Kaya” – An Cafke Saurayi A Katsina

Wani saurayi ya gamu da cikas a soyayyarsa bayan da rundunar ’yan sanda a jihar Katsina ta damke shi bisa zargin sata a gidan surikansa.

Matashin da aka bayyana da suna Abdullahi Umar, mai shekaru 31 daga Makarfi, jihar Kaduna, ya ce soyayya ce ta jawo shi cikin halin da ya tsinci kansa.

A cewarsa, ya hadu da budurwarsa ne ta Facebook, inda ta gayyace shi zuwa Katsina. Bayan ya isa, aka karɓe shi hannu bibbiyu har ya kwana biyu a gidan yayanta.

Sai dai ranar da zai tafi gida, ya zabi ya dauki laptop, takalma da kuma kayan sawa daga cikin gidan, abin da ya jawo aka cafke shi.

Kakakin rundunar ’yan sanda na Katsina, SP Gambo Isa, ya tabbatar da lamarin, inda ya ce za a gurfanar da shi a kotu bayan kammala bincike.

Miji na shirin kara aure, mata ta kashe ’ya’yanta biyuWani mummunan lamari ya auku a Kano inda wata mata ta hallaka ’ya’...
09/09/2025

Miji na shirin kara aure, mata ta kashe ’ya’yanta biyu

Wani mummunan lamari ya auku a Kano inda wata mata ta hallaka ’ya’yanta biyu da adda a safiyar yau, bayan samun labari cewa mijinta na shirin ɗaura aure da wata mata ta biyu.

Rahotanni sun nuna cewa lamarin ya faru ne a cikin gida, kuma makwabta sun bayyana mamaki da takaici a kan abin da ya faru.

Hukumomin tsaro sun ce an k**a matar, kuma bincike ya na gudana.

A halin yanzu, al’umma na ci gaba da tofa albarkacin baki, suna kira da a dinga yin hakuri da juna a rayuwar aure don gujewa irin wannan mummunan lamari.

KU JI TSORON ALLAH!Wata mahaukaciya ta gamu da mummunan zalunci daga hannun wani maras imani. Ana zuwa ana amfani da ita...
08/09/2025

KU JI TSORON ALLAH!

Wata mahaukaciya ta gamu da mummunan zalunci daga hannun wani maras imani. Ana zuwa ana amfani da ita har ta samu ciki, daga baya ta haihu da yaro namiji.

Wannan ba wai labari bane kawai – hujja ce ta irin muguntar da wasu ke aikatawa.
Fyade ga mahaukaciya ko yaro babban zunubi ne, kuma zalunci ne da Ubangiji zai hukunta shi.

Shin ba ku jin tsoron Allah?
Shin ba ku tsoron hukuncinSa a ranar karshe?

Ya Allah, ka fitar mata da hakkinta.
Ka hukunta duk wanda yake aikata irin wannan mugunta – ka tilasta shi ya tuba, ko ka ɗauke shi cikin wulakanci.

Ameen.

Abuja: Masu Gidaje 374 Sun Fuskanci Tara Mai TsokaHukumar Gudanar da Babban Birnin Tarayya (FCTA) ta ɗauki mataki kan ma...
08/09/2025

Abuja: Masu Gidaje 374 Sun Fuskanci Tara Mai Tsoka

Hukumar Gudanar da Babban Birnin Tarayya (FCTA) ta ɗauki mataki kan masu gidaje 374 da ke cikin wasu muhimman tituna na Abuja, bayan gano cewa sun sauya amfani da filayen gidajensu ba tare da izini ba.

FCTA ta bayyana cewa kowanne daga cikinsu zai biya Naira miliyan 5 a matsayin tara, tare da wa’adin kwanaki 30 daga 10 ga Satumba, 2025.

Bayan biyan wannan tara, za a ba su sabbin takardun mallaka – Statutory Right of Occupancy da Certificate of Occupancy.

An umarci masu gidajen da su garzaya ofishin Sashen Filaye na FCTA, No. 4, Peace Drive, Central Business District, Abuja, tare da takardunsu na asali da sahihan katin shaida.

Titunan da abin ya shafa sun haɗa da:

Gana Street, Usuma Street (Maitama), Yakubu Gowon Crescent (Asokoro), Aminu Kano da Adetokunbo Ademola Crescent (Wuse II), Ladoke Akintola Boulevard da Gimbiya Street (Garki II), Onitsha Street (Garki II), Ogbomosho Street, Lafia Close, Yola Street, Abriba Close, Danbatta Street, Ringim Close da Ilorin Street (Garki I).

Address

KADUNA
Kaduna

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Adamsy Gimbiya News24 posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share

Category