ClockwiseReports Hausa

  • Home
  • ClockwiseReports Hausa

ClockwiseReports Hausa Sabowar kafar yada labarai masu inganci

Fitar da maniyi akai-akai na rage haɗarin kamuwa da cutar sankarar mafitsara – Masana –
07/09/2025

Fitar da maniyi akai-akai na rage haɗarin kamuwa da cutar sankarar mafitsara – Masana –

Koodinetan Shirin Yaƙi da Cutar Sankara na Ƙasa, ƙarƙashin Ma’aikatar Lafiya da Walwalar Jama’a, Dakta Uche Nwokwu, ya bayyana cewa yawan fitar maniyyi na iya rage haɗarin kamuwa da cutar sankarar mafitsara ga maza. Nwokwu ya bayyana haka ne a yau Lahadi a Abuja, yayin wata hira da Kamfanin...

HOTONA: Jami'ar Usmanu Danfodiyo Sokoto (UDUS), ta ba Sheikh Aminu Ibrahim Daurawa digirin girmamawa.
06/09/2025

HOTONA: Jami'ar Usmanu Danfodiyo Sokoto (UDUS), ta ba Sheikh Aminu Ibrahim Daurawa digirin girmamawa.

Gwamnatin Tarayya ta yi gargaɗin cewa za a tafka mamakon ruwan saman da zai iya haifar da ambaliyar ruwa a jihohin Najer...
04/09/2025

Gwamnatin Tarayya ta yi gargaɗin cewa za a tafka mamakon ruwan saman da zai iya haifar da ambaliyar ruwa a jihohin Najeriya 14 daga ranar 4 zuwa 8 ga watan Satumba.

Cibiyar Gargaɗi Kan Ambaliya (FEWS) ta ma’aikatar ce ta sanar da hakan a cikin wata sanarwa ranar Alhamis.

Ga jerin jihohin da za a tafka ruwan da kuma yankunan.

Hukumar jin dadin Alhazai ta Jihar Kano ta sanar da kudin da alhazai za su fara biyan da kuma adadin kujerun da aka baiw...
04/09/2025

Hukumar jin dadin Alhazai ta Jihar Kano ta sanar da kudin da alhazai za su fara biyan da kuma adadin kujerun da aka baiwa Kano na Hajjin 2026

Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Kano ta bayyana kudin ajiya ga maniyyatan jihar da za su yi aikin Hajjin shekarar 2026.

Wata sanarwa da jami’in hulɗa da jama’a na hukumar, Sulaiman A. Dederi, ya fitar ta ce, wannan mataki ya yi daidai da umarnin Hukumar Hajji ta Ƙasa (NAHCON).

Ya bayyana cewa Babban Daraktan hukumar, Alhaji Lamin Rabi’u Danbappa, ne ya sanar da hakan a ranar Laraba yayin taron da aka gudanar tare da mambobin hukumar, manyan jami’ai, jami’an cibiyoyin hajjin kananan hukumomi da sauran ma’aikata a ofishinsa.

Dederi ya ce, bisa ga umarnin NAHCON, an sanya kudin ajiya na aikin Hajjin 2026 kan naira miliyan 8,500,000.

Ya kara da cewa hukumar za ta fara karɓar kudaden ajiya ta hanyar banki, ta wajen jami’an cibiyoyin hajjin kananan hukumomi.

Haka kuma ya bayyana cewa jihar Kano ta samu kujeru 5,684 domin aikin Hajjin 2026.

Ya ce za a fara karɓar kudin ajiya nan da nan, kuma za a ci gaba da karɓa har zuwa ranar 5 ga Oktoba, 2025, lokacin da za a sanar da kuɗin aikin Hajji na ƙarshe.

“Alhaji Lamin Rabi’u ya ja hankalin dukkan maniyyatan da su gaggauta biyan kudin ajiyarsu bisa jadawalin da masarautar Saudiyya ta bayar domin aikin Hajjin 2026. Ya kuma nanata cewa dole ne dukkan maniyyata su gabatar da hotuna guda takwas masu girman fasfo da ingantaccen fasfo na ƙasa da ƙasa a matsayin wani ɓangare na tsarin rajista.

“A nasa jawabin, Shugaban kwamitin gudanarwar hukumar, Alhaji Yusif Lawan, ya yi addu’a ga Allah Madaukakin Sarki da Ya ba wa dukkan maniyyata ikon biyan kudin aikin Hajji ba tare da wahala ba.

HOTUNA: Yadda aka yi bikin taya Sarki Muhammad Sanusi II murna bayan ya kammala digiri na uku a birnin Landan.Gwamnan Ka...
04/09/2025

HOTUNA: Yadda aka yi bikin taya Sarki Muhammad Sanusi II murna bayan ya kammala digiri na uku a birnin Landan.

Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf yana cikin waɗanda s**a raka Sarkin.

Yadda Shugaba Tinubu ya karbi bakuncin gwamnonin arewa maso gabas a fadar mulkinsa ta Villa
03/09/2025

Yadda Shugaba Tinubu ya karbi bakuncin gwamnonin arewa maso gabas a fadar mulkinsa ta Villa

Zan iya yanke wa kaina jam‘iyyar siyasar da ta fi dacewa da ni ba tare da neman shawara wurin kowa ba - Abdulmumin Jibri...
03/09/2025

Zan iya yanke wa kaina jam‘iyyar siyasar da ta fi dacewa da ni ba tare da neman shawara wurin kowa ba - Abdulmumin Jibrin

Dan majalisar wakilan da ke cikin jiga-jigan siyasar Kwankwasiyya a yayin hirarsa da gidan talabijin na Channels, ya ce, akwai kyakkyawar fahimta da girmamawa tsakaninsa da Shugaba Tinubu.

Gwamnatin Nijeriya ta ayyana Juma'a 5 ga watan Satumba a matsayin ranar hutun Maulidi
03/09/2025

Gwamnatin Nijeriya ta ayyana Juma'a 5 ga watan Satumba a matsayin ranar hutun Maulidi

Na goyi bayan tikitin Muslim-Muslim ne a 2023 don manufar siyasa ba addini ba - Elrufa'iTsohon gwamnan jihar Kaduna, Mal...
01/09/2025

Na goyi bayan tikitin Muslim-Muslim ne a 2023 don manufar siyasa ba addini ba - Elrufa'i

Tsohon gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasir El-Rufai, ya bayyana cewa goyon bayansa ga tikitin Musulmi da Musulmi a zaben shugaban kasa na 2023 ba don addini ba ne, illa siyasa ce kawai domin samun nasara.

El-Rufai ya bayyana haka ne a gidan talabijin na Channels ta cikin shirin Sunday Politics, inda ya ce matakin na jam’iyyar APC wani tsari ne na siyasa da aka yi tunani akai domin samun nasara a zabe, ba wai wani abu da ya shafi addini ba.
A cewarsa dama tsarin na siyasa ne, kuma dabarar lashe zabe ce, ba wani batu na addini ba,idan kana neman cin zabe kana duba dukkan dabarun da za su baka nasara.

Ya ce, irin wannan tunani shi ma ya yi lokacin da ya tsaya takarar gwamna a Kaduna a kan tikitin Musulmi da Musulmi, kuma hakan bai tauye wa Kiristoci hakkin su ba,kuma duk shugaban da yake son samun nasara ba zai takaita kansa ga addini ko kabila daya ba dole ne ya nemi mutane ko ta ina ne.

Shugabar ma’aikata na FCT, Adayilo ta rasuShugabar Majagaba na Ma'aikatan na Babban Birnin Tarayya, (FCT) Misis Grace Ad...
01/09/2025

Shugabar ma’aikata na FCT, Adayilo ta rasu

Shugabar Majagaba na Ma'aikatan na Babban Birnin Tarayya, (FCT) Misis Grace Adayilo, ta mutu.

Marigayi Adayilo ta rasu ne da sanyin safiyar Litinin, 1 ga Satumba, 2025.

Mataimaki na musamman kan harkokin yada labarai ga HoS, Anthony Odey, ya tabbatar wa manema labarai rahoton.

Tsohon Sufeta Janar na ƴan sandan Nijeriya Solomon Arase, ya rasu a Abuja
31/08/2025

Tsohon Sufeta Janar na ƴan sandan Nijeriya Solomon Arase, ya rasu a Abuja

An ba ma'aikatan VOA sama da 500 takardar sallama daga aikiGwamnatin Trump ta dauki matakin korar sauran ma'aikatan kafa...
31/08/2025

An ba ma'aikatan VOA sama da 500 takardar sallama daga aiki

Gwamnatin Trump ta dauki matakin korar sauran ma'aikatan kafar yada labarai ta gwamnatin kasar Muryar Amurka wato kafar VOA.

An aika wa ma'aikata fiye da 500 takardar sallama daga aiki a kafar da yaɗa labarai.

Shugabar riko ta kafar yada labaran, Kari Lake, ta sanar da wannan mataki na rage ma'aikatan a shafinta a kafar sada zumuntarta.

Ta ce matakin zai taimaka wadanda aka zaba damar tafiyar da gwamnati da rage kudin harajin da ake kashewa, duk da a kwai yiwuwar za a kalubalanci wannan mataki a kotu.

A lokacin yakin duniya na biyu ne aka samar da kafar yada labaran ta VOA domin dakile farfagandar da ake yada wa akan 'yan N**i.

Address


Opening Hours

Monday 07:00 - 19:00
Tuesday 07:00 - 19:00
Wednesday 07:00 - 19:00
Thursday 07:00 - 19:00
Friday 07:00 - 19:00
Saturday 07:00 - 19:00
Sunday 07:00 - 19:00

Telephone

+2349030769760

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when ClockwiseReports Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

  • Want your business to be the top-listed Media Company?

Share