ClockwiseReports Hausa

ClockwiseReports Hausa Sabowar kafar yada labarai masu inganci

Ɗaya daga chikin yaran Shugaba Buhari Fatima ta fashe da kuka yayin da ake bata hakuri a gidan sa dake daura.
15/07/2025

Ɗaya daga chikin yaran Shugaba Buhari Fatima ta fashe da kuka yayin da ake bata hakuri a gidan sa dake daura.

05/07/2025

Tinubu ya isa Brazil don halartar taron BRICS –

Shugaba Bola Tinubu a daren Juma'a ya isa birnin Rio de Janeiro na Brazil, domin halartar taron BRICS karo na 17. Wannan shi ne karon farko da Najeriya ta kara kulla kwance da BRICS. A cewar wata sanarwa da mai magana da yawun shugaban kasar My Bayo Onanuga ya fitar, jirgin saman shugaban kasar da y...

2027: Kwankwaso ba shi da wata jam’iyya da zai yi takara da Tinubu – NNPPJam’iyyar NNPP ta ce dan takararta na shugaban ...
05/07/2025

2027: Kwankwaso ba shi da wata jam’iyya da zai yi takara da Tinubu – NNPP
Jam’iyyar NNPP ta ce dan takararta na shugaban kasa a zaben 2023, Sen. Rabiu Kwankwaso, ba shi da damar yin takara da shugaba Bola Tinubu da ko wani dan takarar shugaban kasa a halin yanzu a 2027.

Shugaban NNPP na kasa, Dr Agbo Major ne ya bayyana haka cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Asabar.

Kamfanin Dillancin Labaran Najeriya NAN ya ruwaito cewa Major yana magana ne a kan maganar da Buba Galadima ya yi na cewa Kwankwaso zai tsaya takarar shugaban kasa a jam'iyyar NNPP.

Agbo ya bayyana cewa, tuni jam’iyyar NNPP ta kore da Kwankwaso da Galadima, saboda k**a su da yiwa jam’iyyar zagon kasa.

05/07/2025

2027: Kwankwaso ba shi da wata jam’iyya da zai yi takara da Tinubu – NNPP –

Jam’iyyar NNPP ta ce dan takararta na shugaban kasa a zaben 2023, Sen. Rabiu Kwankwaso, ba shi da damar yin takara da shugaba Bola Tinubu da ko wani dan takarar shugaban kasa a halin yanzu a 2027. Shugaban NNPP na kasa, Dr Agbo Major ne ya bayyana haka cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Asabar...

Mataimakin shugaban ƙasar Najeriya, Kashim Shettima ya isa gidan marigayi Alhaji Aminu Alhassan Dantata da ke unguwar Sa...
03/07/2025

Mataimakin shugaban ƙasar Najeriya, Kashim Shettima ya isa gidan marigayi Alhaji Aminu Alhassan Dantata da ke unguwar Sarari a birnin Kano don ta'aziyyar rasuwar sa.

Gwamnan jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf ne ya tarbi Shettima a filin jirgin sama na Malam Aminu Kano, sannan ya raka shi zuwa gidan gaisuwar.

An kwantar da Buhari a ICU a Landan - Rahoto Tsohon Shugaban Kasa Muhammadu Buhari na fama da rashin lafiya, kuma rahota...
02/07/2025

An kwantar da Buhari a ICU a Landan - Rahoto

Tsohon Shugaban Kasa Muhammadu Buhari na fama da rashin lafiya, kuma rahotanni sun ce kwanan nan aka sallame shi daga dakin kula da masu matsananciyar rashin lafiya (ICU) a wani asibiti da ke Landan a kasar Birtaniya.

Jaridar TheCable ta rawaito daga Empowered Newswire, wani makusancin tsohon shugaban ya bayyana cewa Buhari ya kamu da rashin lafiya ne a Landan yayin da ya je don duba lafiyarsa.

Rahoton ya ce an kwantar da Buhari a dakin ICU, amma daga bisani aka sallame shi makon da ya gabata.

Ko da ya ke ba a bayyana irin cutar da ke damunsa ba, rahotanni sun nuna cewa yana samun sauki a Landan, kuma ana sa ran zai dawo Najeriya da zarar ya warke gaba ɗaya.

Empowered Newswire ta kara da cewa, bisa bayanan da s**a samu daga wasu majiyoyi masu tushe, Mamman Daura – kawun Buhari kuma amintaccensa – shima yana samun sauki daga rashin lafiya a kasar Birtaniya.

Buhari bai halarci bikin cika shekaru 50 da kafuwar Kungiyar raya Tattalin Arzikin Kasashen Yammacin Afrika (ECOWAS) da aka gudanar a Legas ranar 28 ga Mayu ba.

A wata wasika da ya aika wa Shugaba Bola Tinubu, Buhari ya bayyana cewa rashin halartar sa taron ya samo asali ne daga tafiyarsa ta duba lafiya a Birtaniya.

Farfesa Haruna Musa Dambatta ya zama  sabon shugaban jami'ar BUKJami'ar Bayero ta Kano, ta zabi Farfesa Haruna Musa a ma...
01/07/2025

Farfesa Haruna Musa Dambatta ya zama sabon shugaban jami'ar BUK

Jami'ar Bayero ta Kano, ta zabi Farfesa Haruna Musa a matsayin sabon shugaban jami'ar.

Musa ya zama shugaban ne bayan jami'ar ta gudanar da zaɓe tsakanin ƴan takarar kujerar a yau Talata a harabar jami'ar.

Ga jerin yadda sak**akon zaɓen ya kasance:

1. Farfesa Haruna Musa = 853
2. Farfesa Mahmoud Umar Sani = 367
3. Farfesa Muhammad Sani Gumel = 364
4. Farfesa Adamu Idris Tanko = 161
5. Farfesa Bashir Muhammad Fagge = 18

An gudanar da Jana’izar Marigayi Alhaji Aminu Dantata a  Masallacin Annabi dake Madina sannan za a binne shi a Makabarta...
01/07/2025

An gudanar da Jana’izar Marigayi Alhaji Aminu Dantata a Masallacin Annabi dake Madina sannan za a binne shi a Makabartar Baqiah

Tawagar mataimakin shugaban majalisar dattawa, Barau I. Jibrin Maliya sun sauka a Madina domin halartar jana'izar Dattij...
01/07/2025

Tawagar mataimakin shugaban majalisar dattawa, Barau I. Jibrin Maliya sun sauka a Madina domin halartar jana'izar Dattijo Alhaji Aminu Dantata.

Tagawagar gwamnatin Kano ta sauka a Madina
30/06/2025

Tagawagar gwamnatin Kano ta sauka a Madina

Nan da watanni 2 gwamnan Kano da wasu gwamnonin 3 za su koma APC - ArodiogbuMataimakin shugaban jam’iyyar APC na ƙasa (y...
30/06/2025

Nan da watanni 2 gwamnan Kano da wasu gwamnonin 3 za su koma APC - Arodiogbu

Mataimakin shugaban jam’iyyar APC na ƙasa (yankin kudu maso gabas), Ijeoma Arodiogbu, ya bayyana cewa gwamnonin jihohin Bayelsa, Rivers, Plateau da Kano za su sauya sheka zuwa jam’iyyar mai mulki cikin watanni biyu masu zuwa.

A wata hira da jaridar Punch, Arodiogbu ya ce shirin sauya shekar ba zato ba ne ko jita-jita, illa dai wani abu da zai faru nan ba da jimawa ba.

Ya kara da cewa jam’iyyar APC ba ta rufe kofa ga yiwuwar Gwamna Peter Mbah na Enugu da takwaransa Alex Otti na Abia su ma su koma APC ba.

“Ina magana ne akan gwamnonin Bayelsa, Rivers, Plateau, Kano, ko dai Abia ko Enugu. Cikin watanni biyu masu zuwa, za ku ga sun shiga jam’iyyarmu a hukumance,” in ji shi.

“A bayyane yake cewa Bayelsa na cikin lissafin nan — shi yasa na ambace ta. Game da Adeleke (Gwamnan Osun), ba zan iya bayar da tabbaci ba, amma na san yana ta yin wasu yunkuri.”

Arodiogbu ya ce ‘yan siyasar adawa da ke kokarin hada kawancen jam’iyyun adawa domin fuskantar zaben 2027, burinsu kawai shi ne su fito a kafafen yada labarai, ba don mulki ko ci gaban kasa ba.

Hukumar NCAA ta dakatar jirgin Rano Air saboda gazawar injiA ranar Litinin din da ta gabata ne Hukumar Kula da Sufurin J...
30/06/2025

Hukumar NCAA ta dakatar jirgin Rano Air saboda gazawar inji

A ranar Litinin din da ta gabata ne Hukumar Kula da Sufurin Jiragen Sama ta Najeriya, NCAA, ta dakatar da wani jirgin saman Rano mai lamba 5N-BZY, wanda ya samu matsala a injinsa mai lamba 1.

Sai dai lamarin ya haifar da cikas ga zirga-zirgar fasinja, musamman ma matafiya da ke shirin tashi daga Sakkwato zuwa wasu wurare.

Hukumar ta NCAA ta bayyana cewa an gano hayaki a cikin dakin jirgin da jirgin da abin ya shafa, lamarin da ya sa aka fara aiwatar da hanyoyin gaggawar da s**a dace.

Address

Kaduna

Opening Hours

Monday 07:00 - 19:00
Tuesday 07:00 - 19:00
Wednesday 07:00 - 19:00
Thursday 07:00 - 19:00
Friday 07:00 - 19:00
Saturday 07:00 - 19:00
Sunday 07:00 - 19:00

Telephone

+2349030769760

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when ClockwiseReports Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share