ClockwiseReports Hausa

ClockwiseReports Hausa Sabowar kafar yada labarai masu inganci

Iran ta tabbatar da mutuwar jagoran mulkin kasar Ayatollah Ali Khameni," a cewar kafar yada labaran kasar.
01/03/2026

Iran ta tabbatar da mutuwar jagoran mulkin kasar Ayatollah Ali Khameni," a cewar kafar yada labaran kasar.

Fadar White House ta fitar da hotuna na farko daga cikin dakin taro na musamman (situation room) a Mar-a-Lago, inda aka ...
28/02/2026

Fadar White House ta fitar da hotuna na farko daga cikin dakin taro na musamman (situation room) a Mar-a-Lago, inda aka ga Donald Trump yana jagorantar sa ido kan Operation Epic Fury.

Hotunan na nuna Trump yana karɓar rahotanni kai tsaye tare da manyan jami’an tsaro yayin gudanar da wannan aiki.

Wannan sanarwa ta fito ne daga White House, a matsayin bayanin hukuma kan abin da ke faruwa.

Walida Abdulhadi Ibrahim da yarta tare da kwamishinar ta jihar Jigawa bayan karɓo ta daga hannun hukumar DSS.Matashiyar ...
26/02/2026

Walida Abdulhadi Ibrahim da yarta tare da kwamishinar ta jihar Jigawa bayan karɓo ta daga hannun hukumar DSS.

Matashiyar a yanzu na samun kulawa daga gwamnatin jihar Jigawa.

Motar Dangote ta yi ajalin Jami’in LASTMA da wasu mutum biyu a LegasGwamnatin Jihar Legas ta bayyana alhini kan rasuwar ...
25/02/2026

Motar Dangote ta yi ajalin Jami’in LASTMA da wasu mutum biyu a Legas

Gwamnatin Jihar Legas ta bayyana alhini kan rasuwar wani jami’in Hukumar Kula da Zirga-zirgar Ababen Hawa ta Jihar Legas (LASTMA) da wasu mutum biyu a wani mummunan hatsari da ya faru a shataletalen Badagry, hanyar zuwa Seme, ranar Litinin.

Hukumar LASTMA ta ce wata babbar mota kirar SHACMAN mai ɗauke da kaya ta kamfanin Dangote Group ce ta haddasa hatsarin bayan da ta samu matsalar birki yayin da take gudu da sauri, lamarin da ya sa direban ya rasa iko da motar.

Motar ta buge jami’in LASTMA da ke bakin aiki da wani mai tafiya a ƙafa a shataletalen, sannan ta ci gaba da tafiya ta sake buge wani mutum a nisan kusan mita 200.

Dukkanin mutanen uku sun mutu sak**akon munanan raunuka.

Direban ya tsere daga wurin amma daga bisani jami’an LASTMA s**a k**a shi tare da miƙa shi ga ’yansanda. An kwace motar domin gudanar da bincike.

Babban Manajan LASTMA, Olalekan Bakare-Oki, ya ce rasuwar jami’in abin takaici ne, yana mai jaddada buƙatar tsaurara matakan tsaro ga masu jigilar kaya domin rage hatsura a titunan Legas.

Gwamnatin Kano ta fara aikin ƙawata titunan Kano domin zuwan watan RamadanGwamnatin jihar Kano ta fara aiki ka'in da na'...
21/02/2026

Gwamnatin Kano ta fara aikin ƙawata titunan Kano domin zuwan watan Ramadan

Gwamnatin jihar Kano ta fara aiki ka'in da na'in na kawata wasu muhimman wurare a jihar Kano domin murnar zuwan watan Ramadan.

Kwamishinan ma’aikatar, muhalli da sauyin yanayi Dahir M. Hashim, ya ce an kaddamar da shirin ne domin kawata muhimman wurare a cikin birnin da kayayyakin ado masu nuna al’adun Musulunci da kuma muhimmancin watan azumi.

Ya bayyana cewa Kano ta dade tana zama cibiyar tarihi da al’adun musulunci a Najeriya, yana mai cewa wannan shiri wani mataki ne na kara jaddada martabar jihar tare da kiyaye yanayin ibada da tsarkin da ke tattare da wannan wata mai alfarma.

Hashim ya kara da cewa kayayyakin adon da aka girka a wurare daban-daban suna nufin karfafa dabi’u na imani, kame kai da hadin kai, wadanda watan Ramadan ke wakilta.

Ya bayyana aikin a matsayin wani muhimmin mataki na kara inganta yanayin addini da al’adu a fadin birnin Kano a wannan lokaci na Ramadan.

Wata kotu a Kano ta yanke wa jarumar Kannywood, Samha Inuwa, hukuncin daurin watanni shidaMai shari'a S.M. Shuaibu na ba...
13/02/2026

Wata kotu a Kano ta yanke wa jarumar Kannywood, Samha Inuwa, hukuncin daurin watanni shida

Mai shari'a S.M. Shuaibu na babbar kotun tarayya da ke zamanta a Kano, a ranar Juma’a, 13 ga Fabrairu, 2026, ya sami Sa’adatu Mohammed Inuwa (wadda aka fi sani da Samha) da laifi tare da yanke mata hukuncin daurin watanni shida bisa laifin wulakantawa da lalata takardar Naira.

An gurfanar da jarumar ne a gaban kotu kan tuhuma guda ɗaya da ta shafi lalata kuɗin Najeriya, wanda ya saɓa da tanade-tanaden Dokar Babban Bankin Najeriya (CBN) ta shekarar 2007.

Tuhumar da ake mata ta ce: “Ke Sa’adatu Mohammed Inuwa, a wani lokaci a shekarar 2022, a cikin hurumin wannan kotu mai daraja, kin lalata takardar Naira N1000 (Naira dubu ɗaya) wadda Babban Bankin Najeriya ya fitar ta hanyar face majina da hanci, wanda hakan ya saɓa da sashe na 21(1) na Dokar CBN ta 2007.”

Ms Inuwa ta amsa laifin da ake tuhumarta da shi bayan an karanta mata tuhumar. Dangane da amsa laifin da ta yi, lauyan masu gabatar da ƙara, Musa Isah, ya gabatar da hujjojin shari’ar tare da roƙon kotu ta yanke mata hukunci da ya dace.

Jarumar ta roƙi kotu da ta tausaya mata, tana mai cewa wannan shi ne karo na farko da ta aikata laifi kuma ta nuna nadama kan abin da ta yi.

Daga nan ne Alƙali Shuaibu ya yanke mata hukuncin daurin watanni shida, tare da zaɓin biyan tara ta Naira dubu dari biyu (N200,000) kacal.

Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf ya kai ziyarar ta'aziyya ga Sardaunan Kano Malam Ibrahim Shekarau bisa rasuwar yayansa Mal...
12/02/2026

Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf ya kai ziyarar ta'aziyya ga Sardaunan Kano Malam Ibrahim Shekarau bisa rasuwar yayansa Malam Dahiru Shekarau.

Jami’an tsaro sun kwace fasfon El-Rufai bayan yunkurin k**a shi ya ci tura – Muyiwa An yi yunkurin k**a tsohon gwamnan J...
12/02/2026

Jami’an tsaro sun kwace fasfon El-Rufai bayan yunkurin k**a shi ya ci tura – Muyiwa

An yi yunkurin k**a tsohon gwamnan Jihar Kaduna, Malam Nasir El-Rufai, a filin jirgin sama na Nnamdi Azikiwe da ke Abuja a ranar Alhamis.

Mai ba shi shawara kan harkokin yada labarai, Muyiwa Adekeye, ne ya bayyana hakan ta cikin jerin sakonni da bidiyo da ya wallafa a shafukan sada zumunta.

Ya ce El-Rufai na dawowa ne daga birnin Cairo na kasar Masar lokacin da jami’an tsaro s**a tare shi.

Adekeye ya ce jami’an sun nufi tsohon gwamnan ne da zarar ya sauka daga jirginsa, inda s**a nemi su tafi da shi domin tsare shi.

A cewarsa, tsohon gwamnan ya ki bin su, yana mai jaddada cewa ba zai amince da bukatar ba sai an gabatar masa da gayyata ta hukuma.

Sakon ya ce: “Jami’an tsaro a yau sun yi yunkurin k**a Malam Nasir El-Rufai yayin da ya iso daga Cairo. Malam El-Rufai ya ki bin su ba tare da gayyata ta hukuma ba.”

Adekeye ya kuma yi zargin cewa jami’an tsaron sun kwace fasfon tsohon gwamnan yayin da lamarin ke faruwa.

“Duk da haka, sun kwace fasfonsa daga hannun wani mataimaki,” in ji shi.

Ƴan majalisar Amurka sun nemi a hana Kwankwaso bizar shiga ƙasar Wasu ‘yan majalisar dokokin Amurka guda biyar daga jam’...
11/02/2026

Ƴan majalisar Amurka sun nemi a hana Kwankwaso bizar shiga ƙasar

Wasu ‘yan majalisar dokokin Amurka guda biyar daga jam’iyyar Republican sun gabatar da kudiri a majalisar wakilai ta ƙasar domin tilasta wa sakataren harkokin wajen Amurka gabatar da cikakken rahoto kan matakan da ƙasar ke ɗauka wajen magance zargin tsananta wa addini da kisan gilla da ake cewa na faruwa a Najeriya.

Idan kudirin ya zama doka, ana sa ran ma’aikatun harkokin waje da baitulmali na Amurka za su kakaba takunkumi, ciki har da hana biza da kwace kadarori, kan “mutane ko ƙungiyoyin da ke da hannu a take ‘yancin addini” a Najeriya.

Wadanda aka ambata a cikin kudirin domin yi musu takunkumi sun haɗa da tsohon gwamnan Kano kuma jagoran jam’iyyar NNPP, Rabiu Musa Kwankwaso; ƙungiyar Miyetti Allah Cattle Breeders Association of Nigeria (MACBAN); Miyetti Allah Kautal H**e; da kuma waɗanda aka bayyana a matsayin “makiyayan Fulani masu ɗauke da mak**ai a Najeriya.”

Kudirin na zuwa ne a daidai lokacin da ake ci gaba da muhawara kan batun tsaro da rikice-rikicen addini a Najeriya. Har zuwa yanzu, babu wata sanarwa daga waɗanda aka ambata kan wannan mataki da aka gabatar a majalisar dokokin Amurka.

DA DUMI-DUMI: Majalisar dattawa ta amince da aika sak**akon zaɓe ta hanyar amfani da na'ura da kuma takarda.Majiya: NTA
10/02/2026

DA DUMI-DUMI:

Majalisar dattawa ta amince da aika sak**akon zaɓe ta hanyar amfani da na'ura da kuma takarda.

Majiya: NTA

Wasu hotuna da ke nuna Sarkin Kano Muhammadu Sanusi ko ya fara halartar darussa a tsangayar ilimin Shari'a a jami'ar Nor...
20/01/2026

Wasu hotuna da ke nuna Sarkin Kano Muhammadu Sanusi ko ya fara halartar darussa a tsangayar ilimin Shari'a a jami'ar Northwest ta jihar Kano wacce ta bashi gurbin karatu a kwanan nan.

DA DUMI-DUMI : Ɗan majalisar jiha mai wakiltar karamar hukumar birnin Kano Sarki Aliyu Daneji ya rasu.Rasuwar ta sa na z...
24/12/2025

DA DUMI-DUMI :
Ɗan majalisar jiha mai wakiltar karamar hukumar birnin Kano Sarki Aliyu Daneji ya rasu.

Rasuwar ta sa na zuwa ne mintina kadan bayan an sanar da rasuwar dan majalisar jiha mai wakiltar karamar hukumar Ungoggo, Hon. Aminu Sa'adu

Sanusi Bature Dawakin Tofa mai magana da yawun Gwamnan Kano ne ya tabbatar da rasuwar ta sa a shafinsa na Facebook

Address

Kaduna

Opening Hours

Monday 07:00 - 19:00
Tuesday 07:00 - 19:00
Wednesday 07:00 - 19:00
Thursday 07:00 - 19:00
Friday 07:00 - 19:00
Saturday 07:00 - 19:00
Sunday 07:00 - 19:00

Telephone

+2349030769760

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when ClockwiseReports Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share