ClockwiseReports Hausa

ClockwiseReports Hausa Sabowar kafar yada labarai masu inganci

Saudi Arabia ta sanar da kammala manyan shirye-shirye domin gudanar da aikin Hajj na bana, inda aka tura ma’aikata 22,00...
18/05/2026

Saudi Arabia ta sanar da kammala manyan shirye-shirye domin gudanar da aikin Hajj na bana, inda aka tura ma’aikata 22,000 tare da samar da wuraren zubar da shara 88,000.

Haka kuma, an tanadi amfani da fasahohin zamani da sabbin tsarin gudanarwa domin inganta tsaro, tsafta da kuma inganta ayyukan hidima ga alhazai a dukkan wuraren ibada masu tsarki.

HOTUNA: Malam Ibrahim Shekarau ya shirya liyafar cin abinci ga masu neman takarar kujerar Sanatan Kano ta Tsakiya a Jam'...
18/05/2026

HOTUNA: Malam Ibrahim Shekarau ya shirya liyafar cin abinci ga masu neman takarar kujerar Sanatan Kano ta Tsakiya a Jam'iyyar APC bayan sun janye masa.

Kai tsaye daga fadar gwamnatin Kano, yayin da ake shirye-shiryen da sabon mataimakin gwamnan Kano Murtala Sule Garo.
05/05/2026

Kai tsaye daga fadar gwamnatin Kano, yayin da ake shirye-shiryen da sabon mataimakin gwamnan Kano Murtala Sule Garo.

Gwamnan Jihar Bauchi, Bala Mohammed, ya sanar da ficewarsa daga jam’iyyar Peoples Democratic Party zuwa Allied Peoples M...
02/05/2026

Gwamnan Jihar Bauchi, Bala Mohammed, ya sanar da ficewarsa daga jam’iyyar Peoples Democratic Party zuwa Allied Peoples Movement (APM), bayan makonni ana rade-radin makomarsa ta siyasa.

Gwamnan ya bayyana sauya shekar ne a ranar Asabar a gidan gwamnati da ke Bauchi, inda ya ce rikice-rikicen cikin gida da ke addabar PDP ne s**a tilasta masa neman wata sabuwar jam’iyya domin tabbatar da makomar magoya bayansa gabanin zaben 2027.

Tambuwal Ya Caccaki Rabiu Musa Kwankwaso: “Ya ce Ba Don Talakawa Yake Siyasa Ba”Sanata Rabiu Musa Kwankwaso na fuskantar...
02/05/2026

Tambuwal Ya Caccaki Rabiu Musa Kwankwaso: “Ya ce Ba Don Talakawa Yake Siyasa Ba”

Sanata Rabiu Musa Kwankwaso na fuskantar s**a daga Aminu Waziri Tambuwal, wanda ya zarge shi da rashin mayar da hankali kan muradun al’umma a harkokin siyasa.

Tambuwal ya bayyana cewa, da ace Kwankwaso na yi wa jama’a aiki ne da gaske, da ya tsaya tsayin daka wajen yin adawa domin kafa gwamnati mai inganci da za ta biya bukatun al’umma.

Sai dai ya ce akasin haka ne, yana zargin tsohon gwamnan Kano da fifita burin sa na son shugabanci kan bukatun jama’a.

Har ila yau, Tambuwal ya danganta yiwuwar ficewar Kwankwaso daga jam’iyyar ADC da rashin cimma burinsa na shugabanci a cikin jam’iyyar.

Wannan zargi na zuwa ne a daidai lokacin da ake ta rade-radin sauya sheƙar siyasa a tsakanin manyan ƴan siyasar ƙasar.

Obi da Kwankwaso za su fice daga ADC ranar Litinin - Buba GaladimaJigo a jam’iyyar ADC, Buba Galadima, ya bayyana cewa t...
02/05/2026

Obi da Kwankwaso za su fice daga ADC ranar Litinin - Buba Galadima

Jigo a jam’iyyar ADC, Buba Galadima, ya bayyana cewa tsohon gwamnan Anambra, Peter Obi, da tsohon gwamnan Kano, Rabiu Musa Kwankwaso, za su sanar da ficewarsu daga jam’iyyar ADC tare da komawa wata sabuwar jam’iyya a ranar Litinin.

Galadima ya bayyana hakan ne a wani taron masu ruwa da tsaki na ƙungiyar Obi-Kwankwaso da aka gudanar a Abuja, inda ya ce ana shirin kafa sabuwar haɗaka gabanin zaɓen shekarar 2027.

Jaridar Punch ta rawaito cewa shugabannin biyu na kammala shirin komawa sabuwar jam’iyya mai suna NDC, wadda ake danganta ta da tsohon gwamnan Bayelsa, Seriake Dickson.

Hotuna: Yadda hawan sallah ya gudana a masarautar Gaya dake jihar Kano.
21/03/2026

Hotuna: Yadda hawan sallah ya gudana a masarautar Gaya dake jihar Kano.

Address

Kaduna

Opening Hours

Monday 07:00 - 19:00
Tuesday 07:00 - 19:00
Wednesday 07:00 - 19:00
Thursday 07:00 - 19:00
Friday 07:00 - 19:00
Saturday 07:00 - 19:00
Sunday 07:00 - 19:00

Telephone

+2349030769760

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when ClockwiseReports Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Shortcuts

Share