Idon Matambayi

Idon Matambayi Labarai da rahotanin a Hausa, kuma daga Arewancin Naijeriya da sauran kasarce da ana magana da Hausa

Mazauna birnin Khartoum a Sudan na ci gaba da tserewa daga ƙasar bayan da aka cimma yarjejeniyar tsagaita wuta tsakanin ...
26/04/2023

Mazauna birnin Khartoum a Sudan na ci gaba da tserewa daga ƙasar bayan da aka cimma yarjejeniyar tsagaita wuta tsakanin ɓangarorin da ke yaƙi da juna a ƙasar. Yaƙin da ake yi a Sudan ya jefa jama’a cikin halin tsaka mai wuya – babu abinci kuma babu ruwan sha sannan farashin kayayyaki ya tashi sosai. BBC ta samu zantawa da wasu Hausawan Sudan da suke zaune a birnin na Khartoum – cibiyar rikicin....

Mazauna birnin Khartoum a Sudan na ci gaba da tserewa daga ƙasar bayan da aka cimma yarjejeniyar tsagaita wuta tsakanin ɓangarorin da ke yaƙi da juna a ƙasa

An kara ceto biyu daga cikin ‘yan matan Chibok 98 da s**a rage a hannun ‘yan Boko Haram da s**a yi garkuwa da su a sheka...
25/04/2023

An kara ceto biyu daga cikin ‘yan matan Chibok 98 da s**a rage a hannun ‘yan Boko Haram da s**a yi garkuwa da su a shekarar 2014. A cewar RFI, Yan matan sun kubuta ne a wani samamen dakarun sojin Najeriya s**a kai a maboyan ‘yan ta’addan cikin dajin Sambisa da ke jihar Borno. Kubutar ta su ta zo ne bayan wani farmaki da dakarun rundina ta 21 ta Operation Hadin Kai s**a gaddamar a mabambanta maboyan 'yan ta'adda a sassan dajin Sambisa....

An kara ceto biyu daga cikin ‘yan matan Chibok 98 da s**a rage a hannun ‘yan Boko Haram da s**a yi garkuwa da su a shekarar 2014. A cewar RFI, Yan matan

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya tafi taro na musamman na majalisar shugabannin kasashen yankin tekun Guinea (GGC), kar...
25/04/2023

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya tafi taro na musamman na majalisar shugabannin kasashen yankin tekun Guinea (GGC), karo na 3, wanda shugaban kasar Ghana Nana Akuffo-Ado ya shirya. Shugaban Buhari zai gabatar da jawabai a babban taron tattaunawa kan dabarun karfafa zaman lafiya da tsaro a yakin da ake aikata laifukan da s**a shafi teku. A matsayinsa na tsohon Shugaban Majalisar, Shugaba Buhari ya jajirce wajen kokarin hadin gwiwa da kasashen yankin, Kungiyar Tattalin Arzikin Kasashen Afirka ta Tsakiya, ECCAS, Kungiyar Tattalin Arzikin Yammacin Afrika, ECOWAS, Hukumar Gulf of Guinea, GGC da abokan aikinsu don magancewa da hana satar fasaha....

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya tafi taro na musamman na majalisar shugabannin kasashen yankin tekun Guinea (GGC), karo na 3, wanda shugaban kasar Ghana Nana

Gwamnatin Jihar Kaduna ta ce rahoton sace matafiya a kan hanyar Abuja zuwa Kaduna ba gaskiya ba ne. kwamishinan tsaro da...
08/04/2023

Gwamnatin Jihar Kaduna ta ce rahoton sace matafiya a kan hanyar Abuja zuwa Kaduna ba gaskiya ba ne. kwamishinan tsaro da harkokin cikin gida, Samuel Aruwan ya ce gwamnatin jihar ta nuna rashin jin dadinta game da labarin. A cewar shi, labarin karya ne, kuma gwamnatin jihar tana aiki da jami’an tsaro don ganin ta gurfanar da wadanda s**a asassa labarin ganin yadda ake samun ci gaba a jihar....

Gwamnatin Jihar Kaduna ta ce rahoton sace matafiya a kan hanyar Abuja zuwa Kaduna ba gaskiya ba ne. kwamishinan tsaro da harkokin cikin gida, Samuel Aruwan y

Wata baban kotu a Ibadan, taci tarar makaranta kasa da kasa na jami'ar Ibadan (ISI), da wasu mutane hudu, naira dubu dar...
06/04/2023

Wata baban kotu a Ibadan, taci tarar makaranta kasa da kasa na jami'ar Ibadan (ISI), da wasu mutane hudu, naira dubu dari biyu da arba'in (N240,000) don bata lokaci a saurarar karar da wasu Musulmai mata daliban makarantar s**a shigar don hana su yin anfani da hijabi. In ba'a manta ba, daliban makarantar Musulmai su goma sha Daya da ya hada da; Faridah Akerele, Aaliyah Dopesi, Akhifah Dokpesi, Raheemah Akinlusi, Imam Akinoso, Hamdallah Olosunde, Aliyyah Adebayo, Moriddiyah Yekinni, Ikhlas Badiru, Mahmuda Babarinde, Fareedah Moshood da kungiyar masu rajin Kare hakin Musulmai (MURIC) sun kai karar makarantar domin hana daliban yin amfani da hijabi a makarantar....

Wata baban kotu a Ibadan, taci tarar makaranta kasa da kasa na jami'ar Ibadan (ISI), da wasu mutane hudu, naira dubu dari biyu da arba'in (N240,000) don bata lo

Jami'an Tsaron Farin Kaya (NSCDC) sun k**a wasu mutane uku da jabun kudin Amurka da sabbin takardun naira 1000 da jumila...
06/04/2023

Jami'an Tsaron Farin Kaya (NSCDC) sun k**a wasu mutane uku da jabun kudin Amurka da sabbin takardun naira 1000 da jumilarsu ya kai naira miliyan biyu. Kakakin rundunar ta NSCDC, SC Ikor Oche ya sanar da hakan yayin gabatar da su ga manema labarai ranar Laraba a Gusau, baban Birnin jahar Zamfara. Ya ce wadanda aka k**an, Kamalu Sani mai shekara 28 da Suleiman Yusuf dan shekara 29, dukkaninsu 'yan Karamar Hukumar Tsafe ne da ke jihar....

Jami'an Tsaron Farin Kaya (NSCDC) sun k**a wasu mutane uku da jabun kudin Amurka da sabbin takardun naira 1000 da jumilarsu ya kai naira miliyan biyu. Kakaki

Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari ya umarci Mataimakin Shugaban cibiyar NASENI, Farfesa Mohammed Sani Haruna, da ya gaggaut...
05/04/2023

Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari ya umarci Mataimakin Shugaban cibiyar NASENI, Farfesa Mohammed Sani Haruna, da ya gaggauta barin ofishinsa. Sanarwar da ta fito ta hannu Daraktan Yaɗa Labarai na Ofishin Sakataren Gwamnatin Tarayya, Mr Willie Bassey, ta ce Buhari ya bai wa Sani Haruna umarnin ya mika ragamar aiki ga jami’i mafi girman mukami a cibiyar. “Wannan ya biyo bayan janye tsawaita wa’adin zama a ofis da Buharin ya yi a ranar 2 ga Afrilun 2023 zuwa 2 ga Afrilun 2025 duba da Haruna Sani ya kammala wa’adinsa na shekara biyar rike da cibiyar....

Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari ya umarci Mataimakin Shugaban cibiyar NASENI, Farfesa Mohammed Sani Haruna, da ya gaggauta barin ofishinsa. Sanarwar da ta fi

Gwamnatin Jihar Kaduna ta saukaka dokar hana fita ba dare ba rana da ta sanya a yankin Sabon Garin Nasarawa- Turkaniya d...
04/04/2023

Gwamnatin Jihar Kaduna ta saukaka dokar hana fita ba dare ba rana da ta sanya a yankin Sabon Garin Nasarawa- Turkaniya dake Karamar Hukumar Chikun, na jihar, wanda al'ummomin yankin a yanzu za su iya fita daga karfe 7:00 na safe zuwa karfe 7:00 na yamma. Cikin wani sanarwa da Kwamishinan Tsaro na cikin gidan Jihar, Samuel Aruwan ya fitar ya ce an saukaka dokar ne bisa dalilan samun bayyanai daga hukumomin tsaro wanda zata fara aiki a ranar Laraba 5th ga watan da muke ciki....

Gwamnatin Jihar Kaduna ta saukaka dokar hana fita ba dare ba rana da ta sanya a yankin Sabon Garin Nasarawa- Turkaniya dake Karamar Hukumar Chikun, na jihar, wa

Wata babbar kotu a Legas, karkashin Ibironke Harrison a ranar Litinin, ta yi watsi da karar da ASP Drambi Vandi ya shiga...
03/04/2023

Wata babbar kotu a Legas, karkashin Ibironke Harrison a ranar Litinin, ta yi watsi da karar da ASP Drambi Vandi ya shigar wanda ake zargin ya harbe wata lauyan Legas Omobolanle Raheem a ranar 25 ga Disamba 2022. Mista Vandi ya shigar da karar ne a ranar 28 ga watan Fabrairu inda ya roki kotu da ta yi watsi da tuhumar da ake masa....

Wata babbar kotu a Legas, karkashin Ibironke Harrison a ranar Litinin, ta yi watsi da karar da ASP Drambi Vandi ya shigar wanda ake zargin ya harbe wata lauyan

Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Ovie Omo-Agege. Hoto: Manhaja A Jihar Delta, Jam’iyyar APC ta kori Mataimakin Shu...
03/04/2023

Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Ovie Omo-Agege. Hoto: Manhaja A Jihar Delta, Jam’iyyar APC ta kori Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Ovie Omo-Agege, daga zama mamban jam’iyyar kan zargin yi wa jam’iyya zagon kasa. Wannan na kunshi ne a cikin wani wasika da APC reshen Delta ta fitar a ranar Litinin, Mai dauke da sa hannu Shugaban Jam’iyyar na jihar, Ulebor Isaac, a madadin Kwamitin Shugabannin APC na jihar da Sakatarenta, Inana Michael, da sauran mutum 23....

Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Ovie Omo-Agege. Hoto: Manhaja A Jihar Delta, Jam’iyyar APC ta kori Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Ovie Omo-

Fitacciyar Jarumar masana’antar fim ta Nollywood, Mercy Aigbe, ta bayyana cewa ta musulunta. Daily Post Hausa ta wallafa...
03/04/2023

Fitacciyar Jarumar masana’antar fim ta Nollywood, Mercy Aigbe, ta bayyana cewa ta musulunta. Daily Post Hausa ta wallafa cewa, Aigbe ta bayyana hakan ne a wani taron lacca/ addu’o’i na musamman na Ramadan da ita da mijinta, Kazeem Adeoti su ka shirya a ranar Asabar. A cewar Jaridar, Jarumar, wacce ta lashe kyautar warzuwar jarumai Nollywood ta kuma bayyana cewa sabon sunanta yanzu shine Meenah....

Fitacciyar Jarumar masana’antar fim ta Nollywood, Mercy Aigbe, ta bayyana cewa ta musulunta. Daily Post Hausa ta wallafa cewa, Aigbe ta bayyana hakan ne a

Mabarata Mata zaune akan t**i Hukumar Babban Birnin Tarayya Abuja (FCTA), a ranar Lahadi ta mayar da wasu mabarata akall...
03/04/2023

Mabarata Mata zaune akan t**i Hukumar Babban Birnin Tarayya Abuja (FCTA), a ranar Lahadi ta mayar da wasu mabarata akalla 217 zuwa jihohinsu na asali. Kwashe mabaratan ya biyo bayan umarnin da Karamar Minista a Ma’aikatar Babban Birnin, Ramatu Aliyu da Babban Sakataren Ma’aikatar s**a bayar don tsantace birnin daga mabarata. Daraktan Sashen Kula da walwalar Jama’a na hukumar, Alhaji Sani Amar Rabe, ne ya bayyana wa Kamfanin daillancin Labarai na Najeriya (NAN)....

Mabarata Mata zaune akan t**i Hukumar Babban Birnin Tarayya Abuja (FCTA), a ranar Lahadi ta mayar da wasu mabarata akalla 217 zuwa jihohinsu na asali. Kwa

Sojoji sun sami nasarar fatattakar ‘yan bindiga biyar a karamar hukumar Chikum dake a jihar kaduna. A cikin wata sanarwa...
01/04/2023

Sojoji sun sami nasarar fatattakar ‘yan bindiga biyar a karamar hukumar Chikum dake a jihar kaduna. A cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun mukaddashin mai Magana da yawun rundunar ta daya Lt-Col Musa Yahaya ya fitar a jihar Kaduna. Ya ce, dakarun sojojin Nijeriya dake runduna ta daya, sun kuma yi nasarar kwato bindigu kirar Ak-7 guda 6 da kuma gidan Alburusai na bindigar AK 47 guda shida da kuma wani Alburushi masu tsayin 7.62mm guda 24....

Sojoji sun sami nasarar fatattakar ‘yan bindiga biyar a karamar hukumar Chikum dake a jihar kaduna. A cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun mukaddashin

Kwamitin zartaswa na jam’iyyar PDP a ranar Alhamis ya janye dakatarwar da ya yi wa Tsohon Gwamnati Jihar Katsina, Ibrahi...
30/03/2023

Kwamitin zartaswa na jam’iyyar PDP a ranar Alhamis ya janye dakatarwar da ya yi wa Tsohon Gwamnati Jihar Katsina, Ibrahim Schema da Ayodele Fayoshe na jihar Ekiti. Sakataren yada labarai na jam’iyyar na kasa, Debo Ologunagba ne, ya bayyana hakan a wani mataki na sasanta rikicin da ke ruruwa a jam'iyar. Ya ce sauran sun hada da tsohon Shugaban Majalisar Dattawa, Anyim Pius Anyim daga Jihar Ebonyi, Farfesa Dennis Ityavyar daga Jihar Binuwai da kuma Dokta Aslam Aliyu daga Jihar Zamfara....

Kwamitin zartaswa na jam’iyyar PDP a ranar Alhamis ya janye dakatarwar da ya yi wa Tsohon Gwamnati Jihar Katsina, Ibrahim Schema da Ayodele Fayoshe na jihar E

Address

Kaduna

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Idon Matambayi posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Idon Matambayi:

Share