HAUSA Times

HAUSA Times publishing/distributing and broadcasting news

Shugabannin sun yi wannan kira ne a daidai lokacin da Trump ke karɓar bakuncin Firaministan Isra’ila Netanyahu kan lamar...
08/04/2025

Shugabannin sun yi wannan kira ne a daidai lokacin da Trump ke karɓar bakuncin Firaministan Isra’ila Netanyahu kan lamarin

Karin bayani:

Shugabannin ƙasashen Masar da Faransa da kuma Jordan sun bukaci shugaban Amurka Donald Trump a wata ganawa da s**a yi ta wayar Tarho da ya yi ƙoƙari wajen kawo ƙarshen yaƙin Gaza.

Yanda aka gudanar da Jana'izar marigayi Sheikh Dr Idris Abdulaziz Dutsen Tanshi, a filin Idi na Games Village a cikin ga...
04/04/2025

Yanda aka gudanar da Jana'izar marigayi Sheikh Dr Idris Abdulaziz Dutsen Tanshi, a filin Idi na Games Village a cikin garin Bauchi.

Allah ya jikan Malam da Rahama, Allah ya gafarta masa kura kuransa amin

Binciken Ɗan Bello Kan Badakalar Izala: Har Yanzu Kungiyar da Shugabanta Basu Fitar da Bahasi Kan Zargin baBiyo bayan wa...
03/04/2025

Binciken Ɗan Bello Kan Badakalar Izala: Har Yanzu Kungiyar da Shugabanta Basu Fitar da Bahasi Kan Zargin ba

Biyo bayan wani faifan bidiyo na yan mintuna kadan da Shahararren Dan jaridar nan mazaunin Amurka, Dan Bello ya fitar wanda hakan ya jawo cece-kuce a fadin Najeriya biyo bayan zargin da ya yi tare da kawo hujjojin shugaban kungiyar Izala ta kasa, Sheikh Bala Lau ya karbi wasu kudade yayi mirsisi dasu.

Binciken da Dan Bello ya gudanar ya bayyana yadda BVN din shugaban kungiyar Izala, ya samar da asusun Bankuna masu tarin yawa da BVN daya wanda kuma duka yake amfani dasu ta hanyoyi daban daban.

Sai dai kuma bayan sake bidiyon ne lamarin ya zamanto ya tada ƙura, inda mutane da daman gaske s**a baza ma domin tofa albarkacin bakinsu, wasu Malamai kuma s**a aika ta tofin la'anta zuwa ga Dan Bello kan wannan bincike da yayi.

Sai dai shugaban kungiyar na Izala har yanzu bai ce komai ba kan wannan zargi da aka jinjina masa, wanda wasu da dama sun shiga ruɗani da zullumi akan hakan.

Sai dai daga karshe wash daga cikin daliban kungiyar sun sa dukkan shafin dan Bello a faifayi, inda suke kira ga dukkan cikakken da kungiyar ta su da ya kai Ƙarar wannan shafin domin a rufe ta.

📸 Sahara Reporters Hausa

Tsohon shugaban ƙasar Najeriya, Olusegun Obasanjo, zai zuba jarin da ya kai zunzurtun ƙudi har dala miliyan 700 a ƙasar ...
03/04/2025

Tsohon shugaban ƙasar Najeriya, Olusegun Obasanjo, zai zuba jarin da ya kai zunzurtun ƙudi har dala miliyan 700 a ƙasar Kamaru domin ƙarfafa kasuwaci tsakanin Najeriya da Kamaru.
Ƙarin bayani -

Tsohon shugaban ƙasar Najeriya, Olusegun Obasanjo, zai zuba jarin da ya kai zunzurtun ƙudi har dala miliyan 700 a ƙasar Kamaru domin ƙarfafa kasuwaci tsakanin Najeriya da Kamaru.

Gwamnatin ƙasar Hungary ta ce ta yanke shawarar ficewa daga mambar kotun hukunta manyan laifuka ta duniya ICC, bayan isa...
03/04/2025

Gwamnatin ƙasar Hungary ta ce ta yanke shawarar ficewa daga mambar kotun hukunta manyan laifuka ta duniya ICC, bayan isar Benjamin Netanyahu ƙasar domin ziyarar aiki.

Matakin na Hungary na zuwa ne kasancewar Netanyahu ya samu sammaci bisa zargin aikata laifukan yaƙi a Gaza.

Ƙarin bayani:

Gwamnatin ƙasar Hungary ta ce ta yanke shawarar ficewa daga mambar kotun hukunta manyan laifuka ta duniya ICC, bayan isar Benjamin Netanyahu ƙasar domin ziyarar aiki.Matakin na Hungary na zuwa ne ƙasancewar…

Wannan shine sunayen SANATOCIN da s**a sanya hannu domin a dakatar da Sanata NATASHA.
08/03/2025

Wannan shine sunayen SANATOCIN da s**a sanya hannu domin a dakatar da Sanata NATASHA.

24/02/2025

Pi is a network of tens of millions of humans mining Pi cryptocurrency to use and build the Web3 app ecosystem.

Hukumar Alhazai ta Najeriya, wato NAHCON, ta ce ta ci karfin shirye-shiryen aikin Hajjin bana, domin ta tantace adadin m...
23/02/2025

Hukumar Alhazai ta Najeriya, wato NAHCON, ta ce ta ci karfin shirye-shiryen aikin Hajjin bana, domin ta tantace adadin maniyatan da ake sa ran za su tafi Saudiyya, da jiragen da za su yi jigilarsu da dai sauransu.

Ta ce ta daddale yarjejeniya tsakaninta da kamfanin da zai yi wa alhazan kasar hidima a kasa mai tsarki, bayan da ta gayyato jami'ansa zuwa Najeriya, inda aka kawar da duk wata kura da ake hasashen ta taso a tsakaninsu.

Farfesa Abdullahi Saleh Usman, shugaban hukumar alhazan Najeriyar,ya shaidawa BBC cewa sun yi duk wani abinda ya k**ata.

''Mun riga mun gama tantance jiragen sama da masu bada sabis a Saudiyya, da na Madina da na Makah da na Masha'ir

Duk dai abinda ya k**ata mu yi dangane da shirye shiryenmu, za mu iya cewa mun gama''. in ji shi

Game da kurar da taso da ake ganin za ta iya kawo cikas kuwa hukumar ta ce duk da cewa kurar ta tayar mu su da hankali amma komai ya lafa saboda sun cimma matsaya da kamfanin Saudiyyar.

'' Ta tayar muna da hankali domin ba mu san tushenta ba , ba mu san an yi wannan abu ba , wannan ne dalilin da yasa muka gayyoto kamfanin da aka ce sun rubuto takada akan cewa za su kai hukumar kara akan wai na soke mu su kwangilar da aka basu''

Ta ce shugaban kamfanin na Saudiyya da mukarabansa sun zo kasar kuma su ma sun yi mamakin jin wannan labari

Wasu jaridu sun ruwaito cewa hukumar ta NAHCON ta soke kwangilar da aka bai kamfanin na aiki a Masha'ir watau Minna , da Musdaliffa da kuma Arafat. Sai dai hukumar ta ce rashin fahimta ce ta janyo sabanin da aka samu tsakaninsu.

''Mu nan Najeriya an bamu kujeru na mutum dubu 95, toh mun lura cewa gaskiya ba zamu iya kawo mutane dubu 95 ba''

''Su kuma suna jiran lalai mu kawo mu su dubu casain da biyar, to sai su ke ganin ko wasu kamfanonin mu ke kokarin mu dauki wani bangare na aikin mu ba wa, mu ka ce mu su a'a'' in ji shi.

Shugaban hukumar na NAHCON ya ce sun nemi wakilan kamfanin a kan su zo Najeriya domin su karyata labarin da ke cewa sun kai hukumar kotu.

Hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa a Najeriya EFCC ta ta ce ta miƙa wa 'yan ƙasar waje kuɗinsu dala 127,892 (ko kuma n...
22/02/2025

Hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa a Najeriya EFCC ta ta ce ta miƙa wa 'yan ƙasar waje kuɗinsu dala 127,892 (ko kuma naira miliyan 70.60) da ta ƙwato daga hannun 'yan damfara.

An miƙa kuɗaɗen ne a hukumance yau Juma'a yayin taron manema labarai ga wakilan ƙasashen Amurka, da Sifaniya, da Switzerland waɗanda aka damfara daga Najeriya.

Charles Smith, wanda jami'in hukumar tsaro ta FBI ne a Amurka, ya karɓi dala 26,581 (naira N40,602,841.46) a madadin 'yan Amurka da aka damfara.

Bugu da ƙri, EFCC ta miƙa motoci biyu na alfarma, da wani gida da ke Unguwar Maigero a jihar Kaduna domin mayar wa mutanen.

Jakadan Switzerland ma a Najeriya, Andreas Baum, ya karɓi dala 100,011.43 don mayar wa 'yan ƙasarsa da aka damfara a Najeriya.

Sai kuma muƙaddashin jakadan Sifaniya a Najeriya, Maria Velasco, da ya karɓi dala 1,300.

Liverpool za ta saida dan wasan gaba na Colombia mai taka ma ta leda, Luis Diaz, 28, a kakar nan domin samun isassun kud...
22/02/2025

Liverpool za ta saida dan wasan gaba na Colombia mai taka ma ta leda, Luis Diaz, 28, a kakar nan domin samun isassun kudin da za ta sayi mai cin kwallo a kungiyar. (Football Insider)

Da alama an kure hakurin kungiyar hakurin Manchester City, inda ta dauki matakin sauya 'yan wasan da ba sa amfana ma ta komai sakomakon raunin da s**a ji ko gajiyawa. Wannan matakin zai sanya makomar 'yan wasa irin dan wasan tsakiyar Belgium Kevin de Bruyne, 33, da dan wasan Ingila John Stones, 30. (Guardian)

Arsenal ta sake nuna sha'awar dauko dan wasan Juventus Dusan Vlahovic, 25, inda kuluf din na Sabiya zai saida dan wasan kan farashi mai rahusa na fam miliyan 33. (CaughtOffside)

Manchester United, Liverpool da Chelsea na son yin ram dan wasan Faransa Castello Lukeba, da akai wa farashin fam miliyan 74.5 (Daily Briefing by Christian Falk )

Fitaccen attajirin nan Alhaji Aliko Dangote ya  yabawa tsohon shugaban mulkin sojin Nigeria Janar Ibrahim Badamasi Baban...
21/02/2025

Fitaccen attajirin nan Alhaji Aliko Dangote ya yabawa tsohon shugaban mulkin sojin Nigeria Janar Ibrahim Badamasi Babangida sak**akon yadda ya ce shine shugaban da ya fi ba da gudunmuwa wajen bunkasa tattalin arzikin Nigeria.

A cewar Dangote IBB shine ya fara bai wa 'yan kasa lasisi na kafa bankuna masu zaman kansu wanda shi kansa yana daga cikin mutane 30 da s**a amfana

"Ba ya ga wannan na tuna lokacin da kuma ka kira wasu 'yan Nigeria 5 ka ce su kawo tukuicin Naira miliyan dai-dai kowannensu a bashi rijiyar man fetur guda" Inji Dangote

Aliko ya bayyana hakan ne lokacin da ya ke jawabi a wajen taron kaddamar da littafin rayuwar tsohon shugaban kasar a Abuja.

Birnin Da Aka Gina Gidaje A Cikin DuwatsuSetenil de las Bodega dake kasar, birni ne da ke a kudancin ƙasar Andalus (Spai...
19/02/2025

Birnin Da Aka Gina Gidaje A Cikin Duwatsu

Setenil de las Bodega dake kasar, birni ne da ke a kudancin ƙasar Andalus (Spain) da aka gina a cikin tsaunin da ke kewaye da garin. Garin ya kasance sansanin Larabawa a zamanin da.

Setenil de las Bodegas gari ne, da ke Pueblo kuma gunduma a lardin Cádiz, a ƙasar Sifaniya, wadda ya shahara saboda gidajen da aka gina a kan dutsen da ke sama da Río Guadalporcún.

Dangane da ƙidayar jama'a ta shekarar Dubu Biyu da Biyar (2005), birnin ya na da yawan mazauna dubu uku da goma sha shida (3,016).

Muhammad Cisse

Address

ISA KAITA Road KADUNA
Kaduna

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when HAUSA Times posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to HAUSA Times:

Share