11/08/2026
Northwest University Kano ta musanta wani rahoton da ke yawo a kafafen sada zumunta cewa Mai Martaba Sarkin Kano Muhammadu Sanusi II ya halarci wata lacca domin ya “clear carry-over” a jami’ar.
Jami’ar ta bayyana cewa rahoton ba gaskiya ba ne, tare da kira ga jama’a da su yi watsi da wannan labari na ƙarya.
Hukumar jami’ar ta kuma buƙaci jama’a da su riƙa tantance sahihancin bayanai kafin su yaɗa su a kafafen sada zumunta, musamman batutuwan da s**a shafi jami’a da manyan mutane.
Northwest University Kano ta ce babu gaskiya a cikin wannan ikirari da ake yaɗawa.