21/06/2026
Labari Mai Ɗumi: Oyebanji na APC ya lashe zaɓen gwamnan Ekiti na 2026 da ƙuri’u 319,224, ya kayar da Oluyede na PDP da Bejide na ADC.
Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC) ta ayyana ɗan takarar jam’iyyar APC, Biodun Oyebanji, a matsayin wanda ya lashe zaɓen gwamnan Jihar Ekiti na shekarar 2026.
Oyebanji ya samu gagarumar nasara bayan ya tattara ƙuri’u 319,224, inda ya kayar da babban abokin hamayyar sa, ɗan takarar PDP, Dakta Wole Oluyede.
An gudanar da zaɓen ne a dukkan ƙananan hukumomi 16 na jihar, sai dai an samu zarge-zargen kura-kurai da sayen ƙuri’u da yawa, lamarin da masu sa ido kan zaɓen s**a yi Allah-wadai da shi.
Bisa ga sakamakon hukuma da INEC ta sanar, Oluyede ya samu ƙuri’u 40,543, yayin da ɗan takarar jam’iyyar ADC, Dare Bejide, ya samu ƙuri’u 12,872, inda ya zo na uku a jerin masu takara.
Babbar jami’ar tattara sakamakon zaɓen kuma shugabar gudanar da zaɓen, Farfesa Adenike Oladiji, ce ta sanar da sakamakon a safiyar Lahadi, inda ta bayyana Oyebanji a matsayin wanda aka zaɓa bisa cika dukkan sharuddan kundin tsarin mulki na samun nasara a zabe