02/08/2026
AREWAFLOW MEDIA
RAHOTON SIYASA / TA’AZIYYA
Kwankwaso Ya Mika Ta’aziyya Kan Rasuwar Kosan Waka
Daga: Amina Yusuf ✍️
AREWAFLOW MEDIA
Tsohon gwamnan Jihar Kano kuma jagoran siyasa, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso, ya bayyana alhininsa kan rasuwar fitaccen mawakin siyasa Muhammadu Buhari, wanda aka fi sani da Kosan Waka.
A cikin wani sako da ya wallafa, Rabi’u Musa Kwankwaso ya bayyana cewa ya samu labarin rasuwar Kosan Waka cikin jimami, tare da mika sakon ta’aziyya ga iyalan marigayin da abokansa.
A cewar Kwankwaso, Kosan Waka ya taka muhimmiyar rawa wajen yada manufofin tafiyar siyasarsu, inda ya ce gudunmawar mawakin ba za a manta da ita ba.
Haka kuma, Kwankwaso ya yi addu’ar Allah Ya gafarta wa marigayin tare da rokon Allah Madaukakin Sarki Ya sanya shi cikin Aljannar Firdausi.
Labarin rasuwar Kosan Waka ya jawo alhini daga bangarori daban-daban, musamman daga masu bibiyar harkokin siyasa da wakokin siyasa a Arewacin Najeriya.
ArewaFlow Media ta samu wannan rahoto ne daga bayanin da Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso ya fitar, yayin da ake ci gaba da mika sakonnin ta’aziyya ga iyalan marigayin.