AREWA A YAU

AREWA A YAU Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from AREWA A YAU, News & Media Website, Layin Sarki Close Badarawa Kaduna, Kaduna.

Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan ƊayaGwamnatin Jihar Zamfara ta bayyana...
03/06/2026

Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya

Gwamnatin Jihar Zamfara ta bayyana shirinta na tallafa wa mata, ’yan mata, masu nakasa da sauran marasa galihu sama da miliyan daya a faɗin jihar, a wani mataki da ta ce zai ƙarfafa rayuwar al’umma tare da bunƙasa tattalin arziki.

An bayyana hakan ne a yayin wani taron kwana uku da aka gudanar a Sakkwato kan yadda za a aiwatar da Manufofin Ƙarfafa Tattalin Arzikin Mata na Ƙasa, wato Women’s Economic Empowerment Policy, a Jihar Zamfara cikin shekaru biyar masu zuwa.

Da take jawabi a wajen taron, Kwamishiniyar Harkokin Mata da Ci Gaban Al’umma ta Jihar Zamfara, Dakta Aisha M.Z. Anka, ta ce shirin ya nuna ƙudurin gwamnatin jihar na tabbatar da cewa mata da sauran rukunin jama’a masu rauni sun samu damar inganta rayuwarsu.

Dakta Anka, wadda Babban Sakataren Ma’aikatar Harkokin Mata da Ci Gaban Al’umma, Alhaji Garba Aliyu Gayari, ya wakilta, ta bayyana cewa bunƙasa ilimin mata, kare haƙƙoƙinsu da kuma tabbatar da shigarsu cikin harkokin kuɗi zai taimaka wajen ƙarfafa iyalai da kuma samar da ci gaba mai ɗorewa a al’umma.

Ta ce gwamnatin Gwamna Dauda Lawal ta nuna aniyarta ta bunƙasa rayuwar mata ta hanyar manufofi da shirye-shiryen da ke ƙarfafa shigarsu cikin ilimi, noma, kiwon lafiya da shugabanci na siyasa.

A cewarta, ba za a iya samun ci gaban tattalin arziki mai ma’ana ba tare da bai wa mata da ’yan mata damar cin gajiyar shirye-shiryen ci gaba ba.

“Mun na buƙatar ƙarin haɗin gwiwa daga Gwamnatin Tarayya, Bankin Duniya (World Bank) da sauran abokan hulɗar ci gaba domin tallafa wa matan Zamfara ta fuskar zamantakewa, siyasa da tattalin arziki domin samun ci gaba mai ɗorewa,” inji ta.

Ta kuma buƙaci mahalarta taron da s**a haɗa da wakilan hukumomin gwamnati, cibiyoyin gwamnati, ƙungiyoyin fararen hula, sarakunan gargajiya da shugabannin addini da su bayar da gudunmawa mai amfani wajen daidaita manufofin da yanayin rayuwa, al’adu da dabi’un al’ummar Zamfara.

Tun da farko, wata ƙwararriyar mai ba da shawara da Shirin Kare Muhalli na Mata (WEP) ya ɗauka aiki, Misis Damaris Uja, ta ce an shirya taron ne domin ƙarfafa mata da matasa wajen samun damar amfani da haƙƙoƙinsu ta hanyar shirye-shiryen ci gaban muhalli, zamantakewa, siyasa da tattalin arziki.

Ta bayyana gurɓacewar muhalli, cin zarafin mata da rashin samun damar shiga harkokin kuɗi a matsayin manyan matsalolin da ke addabar mata da ’yan mata a sassa da dama na ƙasar nan.

A nasa jawabin yayin zaman nazari da tantance manufofin, jagorar taron, Farfesa Magdalyne Dura, ta ce aiwatar da manufofin wata alhakin gama-gari ce da ke buƙatar haɗin kan dukkan masu ruwa da tsaki.

Ta ce nasarar wannan tsari za ta dogara ne kan yadda masu ruwa da tsaki s**a fahimci yanayin tattalin arziki da zamantakewar jihar tare da bayar da gudunmawa wajen samar da manufofin da za su dace da muradun al’ummar Zamfara.

Farfesa Dura ta kuma yi kira ga mahalarta taron da su tabbatar an tsara manufofin cikin tsarin da ya dace da al’adun gargajiya da kuma koyarwar addinin Musulunci da ake bi a jihar.

A ƙarshe, mahalarta taron sun gabatar da shawarwari daban-daban domin samar da cikakkiyar manufa ta ƙarfafa tattalin arzikin mata, wadda za ta magance buƙatun mata, ’yan mata, masu nakasa da sauran marasa galihu a Jihar Zamfara.

Babban Jarabawar Da Allah Yayi Wa Mata , Shine Tarayya Da Maza , Kai Jama'ah Namiji Buhun Qaya, Namiji Qanin Ajali.✍️Pri...
03/06/2026

Babban Jarabawar Da Allah Yayi Wa Mata , Shine Tarayya Da Maza ,

Kai Jama'ah Namiji Buhun Qaya, Namiji Qanin Ajali.

✍️Princess Jiddah

Don Allah MĄZĂ Ku d!nga wanka da matanku Na Aure Hakan sunnah ce!
03/06/2026

Don Allah MĄZĂ Ku d!nga wanka da matanku Na Aure Hakan sunnah ce!

Innalillahi Wa'inna Ilaihirraji'un... Yau kuma da wannan Bidiyon na bacin rai muka tashi.Yan Mata ne guda biyu aka sace ...
03/06/2026

Innalillahi Wa'inna Ilaihirraji'un... Yau kuma da wannan Bidiyon na bacin rai muka tashi.

Yan Mata ne guda biyu aka sace a hanyar su ta zuwa Gusau Zamfara State, Ana dukan su ana ci musu mutunci abun gwanin ban tausayi da Takaici.

Yanzu haka za'a cigaba da Rayuwar nan k**ar ta dabbobi ko Lokacin Jahiliyyah period babu wata Mafita?... Allah Ya basu Mafita ya tsare mu bakidaya

✍️Ɗan Bello

Assalamu alaikum, Yanzu kanin Mahaifin yaran nan ya kirani a waya Yana kuka, 😭Wasu Bata gari s**a chaka ma yaron nan kar...
03/06/2026

Assalamu alaikum,
Yanzu kanin Mahaifin yaran nan ya kirani a waya Yana kuka, 😭
Wasu Bata gari s**a chaka ma yaron nan karfe a wiya tun shekaran jiya yake Asibitin 44 dake kaduna

Yayin da s**a nema naira 2.5m kudin aiki (operations) Kuma baida hali,
Dan Allah duk Wanda ke da hali ko hanyar da wani zai biya musu, a taimaka Dan Allah, masu kudin mu ko Yan siyasan ku
Acece rayuwan bawan Allah nan 🙏

Ga number da za'a kira Dan Karin bayani a tabbatar.
Baban yaron.

📞 08144177106

8144177106 opay Abubakar Bashir

UmarDG
08060373641

Innalillahi Wa Inna Ilaihi Raji'un 😭😭😭 Yanzu Muke Samun Labarin Rasuwar Musa Suleiman Pantami 😭Tuni Aka Yi Jana'izarsa K...
03/06/2026

Innalillahi Wa Inna Ilaihi Raji'un 😭😭😭

Yanzu Muke Samun Labarin Rasuwar Musa Suleiman Pantami 😭

Tuni Aka Yi Jana'izarsa Kamar Yadda Addinin Musulunci Ya Tanada

Allah Muke Roko Ya Jikansa Ya Gafarta Mishi Allahumma Ameen 🤲

Innalillahi wa innah ilaihi Raju un yanzu muke samun labarin wani bawan Allah a unguwar mu ya rasu tun ranar sallah mata...
03/06/2026

Innalillahi wa innah ilaihi Raju un yanzu muke samun labarin wani bawan Allah a unguwar mu ya rasu tun ranar sallah matarsa da ya'yansa sun tafi sallah ganin gida a zaria suke wan nan abun ya taba zuciyarmu sosai

Kwanansa (6) da rasuwa shi kadai acikin gida babu wanda yasani sai yau ake jin ware yayi yawa a unguwar anbuga gidansa shiru kuma k**ar alamar warin daga ciki yake fitowa cikin daren nan ansamo tsani an tsallaka aka tarar dashi harya fara rubewa 😭

Bawan Allah mutumin kirki Allah yajikansa da rahama Allah yasa mutuwa hutuce agaresa da sauran muslmai lallai makwabta wallahi dole mu gyara Alakarmu ace mutum kwana 6 kuma ba a ganinsa babu labari ba a binceka ba kuma zuwa yayi bayada yan uwa a kusa

✍️Abu Muhammad

ABINDA BABBA YA HANGO.. Ina kara fahimtar dalilin da yasa Sheikh Sani Yahaya Jingir yace Atiku da Kwankwaso su hakura da...
03/06/2026

ABINDA BABBA YA HANGO..

Ina kara fahimtar dalilin da yasa Sheikh Sani Yahaya Jingir yace Atiku da Kwankwaso su hakura da takara su goyi bayan Tinubu da Shettima (Muslim ticket) a zaben 2023 da ya gabata

A yanzu ma su Peter Obi siyasar addini suke mana, amma sun boye, sun jawo Kwankwaso jikinsu

Jiya na kara fahimtar abinda Sheikh Sani Yahaya Jingir ya fada bayan tsohon Sakataren Gwamnatin Nigeria Babacir David ya fice daga jam'iyyar ADC ya fadi maganganu na sharri a kan Atiku

Wato basu dauki darasi akan siyasar addini da aka bugata a zaben 2023 ba, mabiya addinin nasaran da suke tare da Atiku suna ta watsewa a gareshi suna komawa gurin Peter Obin Biafra da suke kan addini daya

Duk alamu ya nuna za'a sake buga siyasar addini a 2027, idan ta k**a muyi Tinubu don hana Obi zuwa fadar shugaban Kasa zamuyi, duk abinda zai faru ya jima bai faru ba

Amma Peter Obi ba zai taba zama ko da mataimakin Shugaban Kasa ba ma b***e shugaban Kasa, gara Tinubu yayi ta mulki har duniya ta tashi akan wani Peter Obi

Allah Ka kara albarka a rayuwar Sheikh Sani Yahaya Jingir

✍️Datti Assalafi

INNALILLAHI WA'INNAH ILAIHI RAJI'UN: Allah Ya Yi Wa Alhaji Auwal Inwala Rasuwa jiya Talata Sak**akon Hatsarin Mota Da Ya...
03/06/2026

INNALILLAHI WA'INNAH ILAIHI RAJI'UN: Allah Ya Yi Wa Alhaji Auwal Inwala Rasuwa jiya Talata Sak**akon Hatsarin Mota Da Ya Rutsa Da Shi

Za A Gudanar Da Jana'izar Sa Da Misalin Ƙarfe 9:00 Na Safiyar yau Laraba A Gidan Su Da Ke Gangaran Gangariya, Cikin Garin Funtua Jihar Katsina.

Allah Ya Jiƙan Sa Da Rahama!

Daga Jamilu Dabawa, Katsina

Address

Layin Sarki Close Badarawa Kaduna
Kaduna

Telephone

+2348029500185

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when AREWA A YAU posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share