AREWA A YAU

AREWA A YAU Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from AREWA A YAU, News & Media Website, Layin Sarki Close Badarawa Kaduna, Kaduna.

Lokacin ina aiki akwai wani babban ma'aikacin Gwamnati daya kawo karar wata abokiyar shashancinsa da ta dauki videon sa ...
04/09/2026

Lokacin ina aiki akwai wani babban ma'aikacin Gwamnati daya kawo karar wata abokiyar shashancinsa da ta dauki videon sa tumbur.

Ya kawo kara ne akan ta nemi ya bata kudi masu yawa ko ta yada ma duniya videon.

Da aka kamota aka kawota bata yi musu ba, sai na karbi number mahaifinta na kirashi na nemi yazo, sai yace "ku mata duk abunda doka ta tanada don nima tafi karfina ta fandare mini".

Me karar bayaso abun ya fadada, haka na take kafa saida aka kaita kotu, kotu ta turata gidan gyaran hali na Suleja.

Da ta sha wahala a gidan gyaran hali ko sati bata yiba ta kira mahaifinta tana kuka tana neman gafara.

Har office uban yazo yana godiya.

Ranar da aka dawo da ita kotu idonta ya rena fata tana kuka, se nasa aka janye FIR din, dama nayi haka ne don ta gane a cikin duniya akwai wata duniyar.

Haka na ja mata kunne na sa to goge vidion nace duk lokacin da videon ya bayyana seta koma gidan gyaran hali.

Cikin ikon Allah hakan yasa wannan yarinyar ta shiriya.

Ire-iren wadannan case din sunada yawa, wasu sun biya kudi, wasu na gaban Jami'an tsaro.

Allah ya shirya.

✍️ Malam Muhammad K Garba

Yadda Aka Rufe Karagar Mai Martaba Sarkin Gumel Menan, Jim Kaɗan Bayan Bayyana RasuwarsaAl'umma na cigaba da nuna alhini...
04/09/2026

Yadda Aka Rufe Karagar Mai Martaba Sarkin Gumel Menan, Jim Kaɗan Bayan Bayyana Rasuwarsa

Al'umma na cigaba da nuna alhini kan wannan babban rashi.

Allah Ya kyautata makwanci.

Daga Abubakar Shehu Dokoki

Gwamna Dauda Lawal Ya Karɓi Lambar Yabo Ta Gwarzon Gwamna A Bikin Cikar Jaridar DAILY TIMES Shekara 100Gwamnan Jihar Zam...
03/09/2026

Gwamna Dauda Lawal Ya Karɓi Lambar Yabo Ta Gwarzon Gwamna A Bikin Cikar Jaridar DAILY TIMES Shekara 100

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya karɓi lambar yabo ta Gwarzon Gwamna na Yankin Arewa maso Yamma da jaridar DAILY TIMES ta ba shi, a yayin bikin cika shekaru 100 da kafuwar jaridar da aka gudanar a Abuja.

Gwamnan ya karɓi lambar yabon ne a yau, Alhamis, a wajen bikin DTN@100 Times Heroes Awards, wanda jaridar DAILY TIMES, wadda ake yi wa kallon mafi daɗewar jaridar Nijeriya, ta shirya domin murnar cika shekaru 100 da kafuwarta.

An karrama Gwamna Lawal ne bisa la’akari da irin jagorancinsa, hidimar da yake yi wa jama’a da kuma gudunmawar da yake bayarwa wajen ci gaban ƙasa.

Lambar yabon na daga cikin shirye-shiryen bikin cika shekaru 100 na jaridar, wadda aka fara wallafawa a shekarar 1926, kuma ta kasance tana bibiyar sauye-sauyen siyasa, tattalin arziki, zamantakewa da al’adun Nijeriya tsawon ƙarni guda.

Shugaban Majalisar Kyaututtukan Jaruman DTN@100, Bolaji Okusaga, ya bayyana cewa an zaɓi Gwamna Lawal ne bayan ya samu mafi yawan ƙuri’u da sunayen waɗanda aka gabatar a matsayin ’yan takara a yankin Arewa maso Yamma.

Okusaga ya ce, bayan gudanar da cikakken tsarin gabatar da sunayen ’yan takara da kuma kaɗa ƙuri’ar jama’a, Gwamna Lawal ne ya samu mafi yawan ƙuri’u a wannan rukuni.

Ya ƙara da cewa, Majalisar Kyaututtukan Jaruman Times da sauran masu ruwa da tsaki sun tabbatar da zaɓensa, bisa la’akari da jagorancinsa, hidimar jama’a da gudunmawar da yake bayarwa wajen ci gaban Nijeriya.

Da yake karɓar kyautar, Gwamna Lawal ya nuna godiyarsa ga Kwamitin Daraktoci, Hukumar Gudanarwa da Kwamitin Shirya Bikin Cika Shekaru 100 na Daily Times Nigeria, da kuma Majalisar Kyaututtukan Jaruman Times da dukkan ’yan Nujeriya da s**a mara wa takararsa baya.

Gwamnan ya ce karramawar ta ƙara tabbatar da jajircewarsa wajen inganta shugabanci nagari da samar da ingantaccen aikin gwamnati ga al’ummar Jihar Zamfara.

Daga cikin sauran fitattun ’yan Nijeriya da aka karrama a wajen taron akwai Sakataren Gwamnatin Tarayya (SGF), Sanata George Akume, da tsohon Shugaban Bankin Raya Afirka (AfDB), Dakta Akinwumi Adesina.

Jaridar ta sanar da cewa za a saka sunayen mutanen da cibiyoyin da s**a samu kyaututtukan DTN@100 Times Heroes Awards cikin jerin fitattun mutane da cibiyoyin da s**a taka muhimmiyar rawa wajen ci gaban Nijeriya a cikin wani babban littafi mai shafuka 700 mai suna Nigerian Grand Book.

A cewar jaridar, littafin zai kasance kundin tunawa da ƙasa baki ɗaya, tare da zama madogara ta tarihi da za ta adana tarihin mutane, cibiyoyi da nasarorin da s**a taimaka wajen tsara tafiyar ci gaban Nijeriya.

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ne ya rubuta gabatarwar littafin Nigerian Grand Book.

Sulaiman Bala Idris
Mai magana da yawun Gwamnan Jihar Zamfara
3 ga Satumba, 2026.

ALLAH SARKI: An Ce Sanadiyyar Bashi Aka Kai Shi Gidan Yari, Inda Bayan an Fito Da Shi Ya Tarar Da Matarsa Ta Haihu, Sann...
03/09/2026

ALLAH SARKI: An Ce Sanadiyyar Bashi Aka Kai Shi Gidan Yari, Inda Bayan an Fito Da Shi Ya Tarar Da Matarsa Ta Haihu, Sannan Kuma Mahifiyarsa Ta Rasu, Wanda Hakan Ya Sa Shi Fashewa Da Kuka

Cikin ban tausayi an nuno mutumin na kyka ita matar tasa tana kuka.

Innalillahi wa inna ilaihi Raji'un 🥹 Shekaran Jiya na kirashi yazo har gida na bashi wankin huluna na, jiya ya kirani na...
03/09/2026

Innalillahi wa inna ilaihi Raji'un 🥹

Shekaran Jiya na kirashi yazo har gida na bashi wankin huluna na, jiya ya kirani na karbi hulunan nace masa bana kusa ya bayar a kofar gida a jiye mini.

Yau da safe muka tashi da labarin rasuwar Hussaini Karamiye ba tare da rashin lafiya ko wani iriba, matashi ne mai mutunta kowa ga yawan ibada da naiman nakai baya fada da Kowa.

Muna addu'a ALLAH ya Jaddada rahama a gareshi ya sadashi da Manzon ALLAH SAW.✅👏

Usman Ibrahim Kobie

BABBAR MAGANA‎: "Idan mijinki ya ce kar ki zaɓi APC ki kashe auren ki fito ni zan biya sadaki na aure ki", In Ji shugaba...
03/09/2026

BABBAR MAGANA‎: "Idan mijinki ya ce kar ki zaɓi APC ki kashe auren ki fito ni zan biya sadaki na aure ki", In Ji shugaban jam'iyyar APC na Jihar Yobe, Alhaji Ibrahim Gadaka.

Me za ku ce ?

Yau Alhamis ne aka yi sadakar bakwai na rasuwar mahaifiyata.. ina barar adduarkuاللَّهُمَّ اغْفِرْ لَهَا وَارْحَمْهَا، و...
03/09/2026

Yau Alhamis ne aka yi sadakar bakwai na rasuwar mahaifiyata.. ina barar adduarku
اللَّهُمَّ اغْفِرْ لَهَا وَارْحَمْهَا، وَعَافِهَا، وَاعْفُ عَنْهَا، وَأَكْرِمْ نُزُلَهَا، وَوَسِّعْ مُدْخَلَهَا، وَاغْسِلْهَا بِالْمَاءِ وَالثَّلْجِ وَالْبَرَدِ، وَنَقِّهَا مِنَ الْخَطَايَا كَمَا نَقَّيْتَ الثَّوْبَ الأَبْيَضَ مِنَ الدَّنَسِ

✍️Ahmed Habeeb

Tsohon gwamnan jihar Kano marigayi Alhaji Abubakar Rimi a lokacin da ya ke rantsar da marigayi sarkin Gumel Marigayi Alh...
03/09/2026

Tsohon gwamnan jihar Kano marigayi Alhaji Abubakar Rimi a lokacin da ya ke rantsar da marigayi sarkin Gumel Marigayi Alhaji Ahmed Sani a kan karagar mulki a ranar 16 ga Disamba, 1980.

Innalillahi Wa Inna Ilaihi Raji'un 😭😭😭 Yanzu Muke Samun Labarin Rasuwar Amina Bello Bawa 😭Tuni aka yi Jana'izarta kamar ...
03/09/2026

Innalillahi Wa Inna Ilaihi Raji'un 😭😭😭

Yanzu Muke Samun Labarin Rasuwar Amina Bello Bawa 😭

Tuni aka yi Jana'izarta kamar yadda addinin Musulunci ya tanada

Allah Muke Roko Ya Jikanta Ya Gafarta Mata Allahumma Ameen 🤲

Address

Layin Sarki Close Badarawa Kaduna
Kaduna

Telephone

+2348029500185

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when AREWA A YAU posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Shortcuts

Share