ZM Hausa TV

ZM Hausa TV Wannan page an buɗe shi ne domin labarun duniya cikin bidiyo da rubutu, da sauran abubuwan da s**a shafi al'umma a faɗin duniya gaba ɗaya.

ga masu buƙatar tallata kasuwancin su ko wani abu su tuntuɓemu a Whatsapp ta wannan number 07060641312

12/04/2026

Wannan ma wata ɗaliba kenan daga cikin masu sauka,amma fa ita sai da ta kai ƙarshe daɗi ya cikata ta fashe da kuka.🥰😂✅

12/04/2026

Wasu bayin Allah kenan,a yayin gabatar da aikin lada na gyaran makabarta.

12/04/2026

Wata ɗaliba kenan, a ranar saukar su tana karatu tana kuka.

12/04/2026

Mai buƙata yayi magana.

12/04/2026
Tsohon gwamnan jihar Kano Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso yayin da ya duƙa domin gaida Hajiya Mariya Ɗantata, mahaifiyar at...
12/04/2026

Tsohon gwamnan jihar Kano Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso yayin da ya duƙa domin gaida Hajiya Mariya Ɗantata, mahaifiyar attajirin Afrika Aliko Ɗangote a wata ziyara da ya kai mata.

ZM Hausa TV

An Karrama Gwamna Fintiri Da Sarautar Gargajiya Ta "Garkuwar Michika" A Bikin Al'adu Na Michika Na Shekarar 2026Gwamnan ...
12/04/2026

An Karrama Gwamna Fintiri Da Sarautar Gargajiya Ta "Garkuwar Michika" A Bikin Al'adu Na Michika Na Shekarar 2026

Gwamnan Jihar Adamawa, Ahmadu Umaru Fintiri, ya samu karrama wa ta sarautar gargajiya mai taken “Lakaa Ka Michika” (Garkuwar Michika) a yayin bikin al’adu na Michika na shekarar 2026 da aka gudanar a ranar Asabar, kamar yadda Arewa Media ta ruwaito.

Gwamnan ya samu wannan karramawa ne a wajen bikin al’adu na shekara-shekara tare da bikin cikar shekara guda da naɗin Mbege Ka Michika, Bulus Luka Gadiga, wanda aka gudanar a filin makarantar Government Secondary School da ke Michika.

A jawabinsa, Gwamna Fintiri ya jaddada muhimmancin al’adu wajen kare asali da tarihin al’umma, yana mai cewa ƙirƙirar masarautar Michika na nuna ƙoƙarin gwamnatinsa na ƙarfafa cibiyoyin gargajiya domin wanzar da zaman lafiya da haɗin kai.

Ya bayyana cewa sabbin sarakunan da aka kafa a jihar sun nuna halaye nagari ba tare da samun wata matsala ba, tare da kira ga al’umma da su ci gaba da ba su goyon baya domin inganta zaman lafiya da fahimtar juna.

Gwamnan ya kuma tabbatar da ƙudirin gwamnatinsa na inganta tsaro da haɗa yankin Michika da lantarki na ƙasa domin bunƙasa tattalin arziki da ci gaban al’umma.

Shugaban taron, Buba Marwa, ya bayyana al’adu a matsayin ginshiƙin kowace al’umma, yana mai jaddada buƙatar kiyaye su. Ya kuma yi kira ga al’umma da su ƙara haɗin kai domin samun ci gaba mai ɗorewa.

Marwa ya yaba wa gwamnan bisa ayyukan ci gaba da aka aiwatar a yankin, musamman a fannin hanyoyi da samar da lantarki, yana mai cewa waɗannan nasarori za su bar tarihi mai kyau a jihar.

Shi ma da yake jawabi, Mbege Ka Michika, Bulus Luka Gadiga, ya gode wa gwamnan bisa ƙirƙirar masarautar Michika tare da yin alƙawarin cikakken goyon bayan masarautar wajen ci gaba. Ya kuma yaba da ayyukan more rayuwa da aka gudanar a yankin, yana mai cewa za su taimaka wajen ƙarfafa zaman lafiya da haɗin kai.

Sarkin ya kuma sanar da ba Gwamna Fintiri sarautar “Lakeka Michika” (Takobin Zaman Lafiya), wadda ya ce na nuna jajircewarsa wajen tabbatar da zaman lafiya da tsaro.

A nasa jawabin, Shugaban Ƙaramar Hukumar Michika, Dan Biyu P. Tumba, ya bayyana gwamnan a matsayin ginshiƙin fata ga al’ummar jihar.

Bikin ya samu halartar manyan baƙi da masu sarauta daga ciki da wajen Jihar Adamawa, inda aka ƙawata shi da wasannin al’adu masu ƙayatarwa.

ZM Hausa TV

Burin ƴaƴa mata suyi karatu su zama likitoci da malaman Asibiti.Yayin da Najeriya ke fama da ƙarin tabarbarewar tsaro da...
12/04/2026

Burin ƴaƴa mata suyi karatu su zama likitoci da malaman Asibiti.

Yayin da Najeriya ke fama da ƙarin tabarbarewar tsaro da ta zama tarnaƙi ga ilimin ƴaƴa mata, masu ruwa da tsaki na kiran a ƙara himma wajen ganin miliyoyin ƴanmata a Arewacin ƙasar sun kammala aƙalla sakandare.

Da yawan ƴanmata ne ba su iya kammala karatunsu na firamare da sakandare. Baya ga ɗimbin waɗanda ba sa zuwa makarantar ma baki-ɗaya saboda dalilan talauci da al'ada da sauransu.

To sai dai, wata gidauniya bunƙasa ilimin ƴaƴa mata a garin Zaria mai suna Center for Girls' Child Education ta ce ta tashi tsaye wajen taimaka wa mata wajen kawar da ƙalubalen da ke hana su samun ilimin.

Ɗaya daga cikin waɗanda suke cin moriyar wannan shirin, Khadija Sa'id Ismail ta ce burinta shi ne ta ga tana aikin asibiti.

"Na samu kaina ne a wannan karatu na musamman daga lokacin da muka shiga aji biyu na sakandare. S**a zo s**a ce za su taimaka mana da horo na musamman saboda mu cika abin da muke buri a rayuwa saboda yawancinmu ba za mu iya ba," in ji ta.

Zm hausa

Innalillahi Wa'inna Ilaihi Rajiun!!!Ana cigiyar iyalan wannan bawan Allah da su duba shi asibitin kwararru na State Spec...
12/04/2026

Innalillahi Wa'inna Ilaihi Rajiun!!!

Ana cigiyar iyalan wannan bawan Allah da su duba shi asibitin kwararru na State Specialist wato General Hospital dake birnin Maiduguri a jihar Borno, don Allah kuyi mana sharing a samu dangin sa.

ZM Hausa TV

MASJIDUL SABAG: A wannan wajen ne Manzo (S) ke horas da Dawakinsa, don zuwa jihadin ɗaukaka kalmar Allah.Allah ya ya ƙar...
12/04/2026

MASJIDUL SABAG: A wannan wajen ne Manzo (S) ke horas da Dawakinsa, don zuwa jihadin ɗaukaka kalmar Allah.

Allah ya ya ƙaramana daraja domin darajar fiyyyen Halitta.

ZM Hausa TV

Address

Zabin Zaria
Kaduna

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when ZM Hausa TV posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to ZM Hausa TV:

Share