12/04/2026
An Karrama Gwamna Fintiri Da Sarautar Gargajiya Ta "Garkuwar Michika" A Bikin Al'adu Na Michika Na Shekarar 2026
Gwamnan Jihar Adamawa, Ahmadu Umaru Fintiri, ya samu karrama wa ta sarautar gargajiya mai taken “Lakaa Ka Michika” (Garkuwar Michika) a yayin bikin al’adu na Michika na shekarar 2026 da aka gudanar a ranar Asabar, kamar yadda Arewa Media ta ruwaito.
Gwamnan ya samu wannan karramawa ne a wajen bikin al’adu na shekara-shekara tare da bikin cikar shekara guda da naɗin Mbege Ka Michika, Bulus Luka Gadiga, wanda aka gudanar a filin makarantar Government Secondary School da ke Michika.
A jawabinsa, Gwamna Fintiri ya jaddada muhimmancin al’adu wajen kare asali da tarihin al’umma, yana mai cewa ƙirƙirar masarautar Michika na nuna ƙoƙarin gwamnatinsa na ƙarfafa cibiyoyin gargajiya domin wanzar da zaman lafiya da haɗin kai.
Ya bayyana cewa sabbin sarakunan da aka kafa a jihar sun nuna halaye nagari ba tare da samun wata matsala ba, tare da kira ga al’umma da su ci gaba da ba su goyon baya domin inganta zaman lafiya da fahimtar juna.
Gwamnan ya kuma tabbatar da ƙudirin gwamnatinsa na inganta tsaro da haɗa yankin Michika da lantarki na ƙasa domin bunƙasa tattalin arziki da ci gaban al’umma.
Shugaban taron, Buba Marwa, ya bayyana al’adu a matsayin ginshiƙin kowace al’umma, yana mai jaddada buƙatar kiyaye su. Ya kuma yi kira ga al’umma da su ƙara haɗin kai domin samun ci gaba mai ɗorewa.
Marwa ya yaba wa gwamnan bisa ayyukan ci gaba da aka aiwatar a yankin, musamman a fannin hanyoyi da samar da lantarki, yana mai cewa waɗannan nasarori za su bar tarihi mai kyau a jihar.
Shi ma da yake jawabi, Mbege Ka Michika, Bulus Luka Gadiga, ya gode wa gwamnan bisa ƙirƙirar masarautar Michika tare da yin alƙawarin cikakken goyon bayan masarautar wajen ci gaba. Ya kuma yaba da ayyukan more rayuwa da aka gudanar a yankin, yana mai cewa za su taimaka wajen ƙarfafa zaman lafiya da haɗin kai.
Sarkin ya kuma sanar da ba Gwamna Fintiri sarautar “Lakeka Michika” (Takobin Zaman Lafiya), wadda ya ce na nuna jajircewarsa wajen tabbatar da zaman lafiya da tsaro.
A nasa jawabin, Shugaban Ƙaramar Hukumar Michika, Dan Biyu P. Tumba, ya bayyana gwamnan a matsayin ginshiƙin fata ga al’ummar jihar.
Bikin ya samu halartar manyan baƙi da masu sarauta daga ciki da wajen Jihar Adamawa, inda aka ƙawata shi da wasannin al’adu masu ƙayatarwa.
ZM Hausa TV