GOBE TA ALLAH CE

GOBE TA ALLAH CE The group was established for sending news that are currently happening in our geographical areas,

10/05/2024

Tarihin KAFEN DAUDU...

Tsakuri.

Wato shi Daudu sunan wani hadimin Sarki ne, wanda ya kasance yana zama a Kofar fada. Kuma daidai inda wannan kafe da ake kira da KAFEN DAUDU yake inda har ya kai saboda girmamawa anyi masa rumfar zama a wannan wuri(Kafe).

Wannan shine abinda muka fara tsakurowa daga tarihin wannan wurin mai dogon zamani da ake kira KAFEN DAUDU, kamar yadda kuke yawan tambayar mu akan tarihin wannan wuri kuma In Sha Allah zamuyi iya ƙoƙarin mu domin kawo maku cikakken tarihin wannan wuri.

Sannan muna maraba da duk wani mai shirin bamu gudunmawa wurin yaɗawa tare da tabbatuwar tarihi.

Ku cigaba da bibiyar mu...

Mungode!

Copied By _ H. Gidan Gari ✍️✍️

09/04/2024

Ramadaniyyat: 1445 [30]‎

✍️Dr Muhammad Sani Umar Rijiyar Lemo Hapizahullah

Rabbaniyyun: Ilimi da Malanta:‎

‎12.0. Kyautta mu'amla da mutane:‎

Ci gaba….‎

‎12.4. Cikin waɗanda s**a cutar da Ibnu Taimiyya akwai alƙali Ibn ‎Makhluf. Wannan alƙali yi iya bakin ƙoƙarinsa ya ga an zubar da jinin ‎Ibnu Taimiyya a kan wasu mas'alolin da suke saɓani da shi amma bai yi ‎nasara ba. Shi kuwa Ibnu Taimiyya ta ɓangarensa ga abin da yake faɗa, ‎ya ce: "Wallahi ina daga cikin waɗanda s**a fi kowa ba da gudunmawa ‎wajen kashe duk wata wutar fitina da ta sharri, da kuma tabbatar da ‎alheri a wannan gari Masar da sauran garuruwa. Duk abin da Ibnu ‎Makhluf zai aikata min, ni ta ɓangarena duk wani alheri da zan iya yi ‎masa, to zan yi masa, kuma har abada ba zan taimaka wa maƙiyinsa a ‎kansa ba.. Wannan ita ce niyyata da ƙudurina, tare da cewa ina sane da ‎duk abubuwan da s**a faru. Domin kuwa na san Shaiɗan yana tunzura ‎tsakanin muminai, to don haka ba zan zama mai taimaka wa Shaiɗan a ‎kan 'yan'uwana muminai ba..". [Duba, Ibnu Taimiyya, Majmu'ul ‎Fatawa, juz. 3, sh. 271].‎

‎12.5. Bayan fitowar Sheikhul Islam Ibnu Taimiyya daga gidan yari, ya ‎nuna wani hali na dattako lokacin da Sarki Nasir ya dawo kan kujerar ‎mulkinsa. Sarki ya so ya yi ramuwar gayya a kan malamai da alƙalai ‎waɗanda s**a ci amanarsa, s**a goyi bayan abokin hamayyarsa, watau ‎Al-Jashankir. Kuma su dai waɗannan malaman su ne waɗanda s**a riƙa ‎yanke wa Ibnu Taimiyya hukuncin ɗauri a jarabawarsa ta farko, a inda ‎ya yi zaman kurkuku na tsawon wata goma sha takwas a sanadiyyarsu. ‎Don haka sai Sarki Nasir ya nemi fatawa a wajen Ibnu Taimiyya cewa, ‎wane hukunci ya kamata ya yi musu game da cin amanarsa da s**a yi? ‎Sai Ibnu Taimiyya ya buɗi baki ya ce masa: “Jininsu ya haramta a ‎kanka. Haramun ne ka cutar da su”. Sai Sarki ya ce: “Mutanen nan fa ‎sun cutar da kai, sun yi ƙoƙarin kashe ka a lokuta da dama”. Sai Ibnu ‎Taimiyya ya amsa masa da cewa: “Duk wanda ya cuce ni, to ni na yafe ‎masa. Wanda kuwa ya cutar

YA ZAKAYI BAKINCIKI?Ya zakayi BAKINCIKI alhalin Allah ya maka ni'ima da musulunci waninka ko yana sujuda ga wanin Allah....
14/03/2024

YA ZAKAYI BAKINCIKI?

Ya zakayi BAKINCIKI alhalin Allah ya maka ni'ima da musulunci waninka ko yana sujuda ga wanin Allah.

Ya zakayi BAKINCIKI alhalin Allah ya suturta aibunka wani ko an bayyana nasa.

Ya zakayi BAKINCIKI alhalin Allah ya sanyaka mai rufin asiri waninka ko yana rokon mutane.

Ya zakayi BAKINCIKI alhalin Allah yabaka ji da gani da kafa da hannu wasu ko basu samu ba.

Duba wadanda ke kewaye dakai dakyau don kaga ni'imomi nawane Allah yasoka dashi alhalin ya hana wasunka?

Godiya ga Allah akan ni'imominsa da basa kididdiguwa.

Na daka cikin rashin adalci na yan Adam shine mutum yayi maka abin alheri amma ka kasa bayyanawa duniya ta gani. Amma da...
14/03/2024

Na daka cikin rashin adalci na yan Adam shine mutum yayi maka abin alheri amma ka kasa bayyanawa duniya ta gani. Amma da zaran wani Kuskure ko aqasin hakan ya faru dashi to kaji ihun mutane ta kowane ban gare. Mu dai mun sani me girma iyan zazau yayi Abinda ba'a taba yi ba a siyasar zaria dama Kaduna state baki daya. Allah yaja zamanin me girma speaker na Nigeria jagaban mutanan Zazzau.

10/03/2024

Barka da zuwa watan ramadan mai albarka

27/02/2024

News # Oronsaye: Duka Ma'aikatu da Hukumomi 45 da Gwamnatin Tarayya Za Ta Iya Rusawa

- Bola Ahmed Tinubu ya bada umarni a dabbaka shawarwarin da kwamitin Steve Oronsaye ya ba gwamnatin Goodluck Jonathan

- Sabon shugaban Najeriyan ya dauki wannan mataki ne a wajen zaman majalisar FEC da aka yi domin rage kashe kudi a kasar

- An nemi hada NEMA da sauran hukumomin da ke kula da 'yan gudun hijira a Najeriya, akwai hukumomi 30 da za a iya soke su

Abuja - Tsohon shugaban ma'aikatan gwamnatin tarayya ya kawo shawarar a soke wasu ma'ikatu, ya kuma nemi a dunkule wasunsu.

Rubuta MBD don samun labaran Hausa, wasu Karin labaran na jiranku.

03/02/2024
https://youtube.com/shorts/wbCyNCfso78?si=iRPx1YDbxYS_ZyfC... Alhamdulilah wanann video... Cikin ikon Allah za mudinga k...
21/01/2024

https://youtube.com/shorts/wbCyNCfso78?si=iRPx1YDbxYS_ZyfC... Alhamdulilah wanann video... Cikin ikon Allah za mudinga kawo muku... Wato shirin muryar malamai acikin wannan channel mai albarka wato Gobe ta Allah ce tv dan Allah karku manta kuyimana subscribe da shearing Domin samun sababbin video namu da zarar mun saka...... 🙏🙏🙏🙏🙏☝️Gobe ta Allah ce 📺 tv

Address

Zabin Zaria
Kaduna

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when GOBE TA ALLAH CE posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share