Mairuwa News updated

  • Home
  • Mairuwa News updated

Mairuwa News updated Stay informed with credible and timely news reports.

Mairuwa News Updated is a reliable online news platform delivering breaking news, politics, security, business, sports, and entertainment updates from Nigeria and beyond.

30/07/2026

jarimi Adam Zango da sadiq sani sadiq na Raha

"Gwamnanmu mai wa'adi biyu, in shaa Allah." – Samir HangaMuhammad Samir Hanga, wanda a baya ya yi fice wajen s**ar Gwamn...
30/07/2026

"Gwamnanmu mai wa'adi biyu, in shaa Allah." – Samir Hanga

Muhammad Samir Hanga, wanda a baya ya yi fice wajen s**ar Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, da kuma mai magana da yawunsa, Sanusi Bature Dawakin-Tofa, ya bayyana tare da gwamnan bayan shafe wani lokaci ba a jin duriyarsa.

Samir Hanga ya wallafa hotonsa tare da Gwamna Abba Kabir Yusuf a shafinsa, tare da rubuta cewa:

"Alhamdulillah. Tare da Babanmu, Gwamnan Jihar Kano mai wa'adi biyu, in shaa Allah, bayan ganawa da shi a ofishinsa da ke Abuja."

Wannan wallafar ta jawo ce-ce-ku-ce da martani daga mabiyansa a shafukan sada zumunta, musamman ganin yadda a baya ya kasance cikin masu s**ar gwamnatin Kano.

Me kuke gani kan wannan sauyin? Ku bayyana ra'ayoyinku cikin girmamawa.

📸 HOTUNA: Sanata Rufa’i Hanga da Sanata Kabiru Gaya Sun Gana da Shugaba Tinubu a AbujaSanata mai wakiltar Kano ta Tsakiy...
27/07/2026

📸 HOTUNA: Sanata Rufa’i Hanga da Sanata Kabiru Gaya Sun Gana da Shugaba Tinubu a Abuja

Sanata mai wakiltar Kano ta Tsakiya, Rufa’i Sani Hanga, da Sanata mai wakiltar Kano ta Kudu, Kabiru Ibrahim Gaya, sun gana da Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, a Abuja.

Taron ya gudana ne a ƙarƙashin jagorancin Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau I. Jibrin, a ranar Lahadi, 26 ga Yuli, 2026.

📷 Ga wasu daga cikin hotunan ganawar.

🚨 Halima Shehu Ta Musanta Zargin Karkatar da Naira Biliyan 44Tsohuwar Shugabar Hukumar National Social Investment Progra...
27/07/2026

🚨 Halima Shehu Ta Musanta Zargin Karkatar da Naira Biliyan 44

Tsohuwar Shugabar Hukumar National Social Investment Programme Agency (NSIPA), Halima Shehu, ta musanta zargin karkatar da Naira biliyan 44, tana mai cewa babu wani bincike da ya nuna an tura kuɗi zuwa asusunta ko na wani daga cikin iyalanta.

A wata hira da ta yi da Arise TV, Halima ta ce tun kafin a dakatar da ita daga mukaminta a watan Disamban 2023, ta kai rahoton wasu zarge-zargen almundahanar kuɗi ga EFCC da ICPC.

Ta bayyana cewa bayan ta karɓi ragamar hukumar, ta gano wasu matsaloli a tsarin kula da kuɗaɗe, tare da zargin cewa ana fitar da kuɗaɗe ba tare da amincewarta ko sa hannunta ba.

Halima ta ce binciken EFCC bai gano ko sisin kwabo a asusunta, na iyalanta ko na abokanta ba, tana mai jaddada cewa kuɗaɗen da ake magana a kai an tura su ne ga hukumomin biyan kuɗi da gwamnati ta amince da su domin rabon tallafi.

Ta kuma yi kira ga Shugaba Bola Ahmed Tinubu da ya tabbatar an bayyana sakamakon binciken da ake yi kan harkokin NSIPA.

🗣️ Me kuke gani? Ya kamata a bayyana sakamakon binciken ga jama’a?

🚨 Gwamnatin Nijar Ta Dakatar da Kamfanoni da ’Yan Kasuwa 36 Kan Zargin Boye SimintiGwamnatin Jamhuriyar Nijar ta dakatar...
27/07/2026

🚨 Gwamnatin Nijar Ta Dakatar da Kamfanoni da ’Yan Kasuwa 36 Kan Zargin Boye Siminti

Gwamnatin Jamhuriyar Nijar ta dakatar da kamfanoni da ’yan kasuwa 36 daga gudanar da harkokin sayar da siminti a faɗin ƙasar na tsawon kwanaki 15.

Ma’aikatar Kasuwanci da Masana’antu ta ce an ɗauki matakin ne bayan zargin wasu daga cikin kamfanonin da ’yan kasuwar da ɓoye siminti domin sakin sa a kasuwa a kaɗan-kaɗan, lamarin da ake zargin ya haddasa ƙarancinsa da kuma tashin farashinsa.

Hukumomi sun bayyana cewa matakin na da nufin kare masu amfani da kayayyaki, tabbatar da wadatar siminti a kasuwa, da kuma dakile duk wani yunkuri na haifar da ƙarancin kayan gini ba bisa ƙa’ida ba.

🗣️ Me kuke ganin ya kamata gwamnati ta yi domin magance matsalar tashin farashin siminti?

Ma'aikatar Tsaro Ta Jaddada Aniyarta Na Bunƙasa Jami'ar Sojojin Najeriya Da Ke BiuMinistan Tsaro, Janar Christopher Musa...
26/07/2026

Ma'aikatar Tsaro Ta Jaddada Aniyarta Na Bunƙasa Jami'ar Sojojin Najeriya Da Ke Biu

Ministan Tsaro, Janar Christopher Musa (mai ritaya),ya sake jaddada ƙudirin Gwamnatin Tarayya na mayar da Jami'ar Sojojin Najeriya da ke Biu (NAUB)ta zama cibiyar koyarwa ta ƙwarai wajen horar da jami'an soja da fararen hula.

Hakan na ƙunshe ne cikin wata sanarwa da Mai Bai wa Ministan Tsaro Shawara kan Harkokin Yaɗa Labarai, Leah Katung-Babatunde, ta fitar.

A cewar sanarwar, Janar Musa ya bayyana hakan ne yayin da ya karɓi baƙuncin mambobin Majalisar Gudanarwar jami'ar a hedikwatar Ma'aikatar Tsaro da ke Abuja. Ya tabbatar musu da ci gaba da ba jami'ar cikakken goyon baya, yana mai cewa NAUB na taka muhimmiyar rawa wajen samar da ƙwararrun ma'aikata masu ilimin fasaha da ƙwarewar aiki domin fuskantar sabbin ƙalubalen tsaro.

Sanarwar ta ƙara da cewa Ma'aikatar Tsaro za ta yi aiki tare da Rundunar Sojojin Najeriya domin tabbatar da cikakken amfani da kaso 30 cikin 100 na guraben shiga jami'ar da aka ware wa jami'an soja, domin cike gibin ƙwarewa a fannin tsaron ƙasa.

A nasa jawabin, Shugaban Majalisar Gudanarwar Jami'ar, Laftanar Janar Tukur Yusuf Buratai (mai ritaya), ya yabawa Ministan Tsaro bisa jagorancinsa da hangen nesansa, yana mai cewa gudunmawar da yake bayarwa na ci gaba da ƙarfafa tsarin tsaron Najeriya.

25/07/2026

Gwamna Uba Sani Ya Kaddamar Da Rabon Motoci 500 Na Takin Noma Kyauta Ga Manoma 150,000 A Kaduna

Atiku Ya Caccaki Fadar Shugaban Ƙasa Kan Kwatanta Najeriya Da ChinaTsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Alhaji Atiku Abubaka...
25/07/2026

Atiku Ya Caccaki Fadar Shugaban Ƙasa Kan Kwatanta Najeriya Da China

Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Alhaji Atiku Abubakar, ya soki Fadar Shugaban Ƙasa kan amfani da tsarin shari’ar ƙasar China wajen kare Shugaba Bola Ahmed Tinubu, yana mai cewa hakan ya sake jawo hankalin jama’a kan tsofaffin zarge-zargen da s**a shafi shugaban.

A wata sanarwa da mai taimaka masa kan harkokin yaɗa labarai, Phrank Shaibu, ya fitar, Atiku ya ce Fadar Shugaban Ƙasa ta kauce wa mayar da martani kan muhimman batutuwan da ya gabatar, maimakon haka ta mayar da hankali wajen kai masa hare-haren siyasa.

Ya ce kwatanta batun da China ba zai amfani gwamnatin Tinubu ba, domin a cewarsa ƙasar na da tsauraran dokoki kan laifukan safarar miyagun ƙwayoyi da cin hanci da rashawa.

Atiku ya kuma jaddada cewa babu wata kotu a Najeriya ko wata ƙasa da ta taɓa samun sa da laifin cin hanci, safarar miyagun ƙwayoyi ko wani laifi.

Haka kuma, ya buƙaci gwamnatin tarayya da ta fi mayar da hankali wajen magance matsalolin tattalin arziki, yunwa da rashin tsaro, maimakon shiga cece-kuce na siyasa.

Wannan martani ya biyo bayan kalaman mai magana da yawun Shugaban Ƙasa, Bayo Onanuga, wanda ya zargi Atiku da cin hanci a lokacin da yake Mataimakin Shugaban Ƙasa. Sai dai Atiku ya musanta zarge-zargen, yana mai cewa babu wata kotu da ta taɓa same shi da wani laifi.

🏫 Hotuna: Yadda Gwamnatin Jihar Kwara Ke Sauya Fasalin Ilimi Tun Daga Shekarar 2019Gwamnatin Jihar Kwara ta ci gaba da z...
25/07/2026

🏫 Hotuna: Yadda Gwamnatin Jihar Kwara Ke Sauya Fasalin Ilimi Tun Daga Shekarar 2019

Gwamnatin Jihar Kwara ta ci gaba da zuba jari mai yawa a fannin ilimi domin samar da ingantaccen yanayin koyo ga ɗalibai a faɗin jihar.

📌 Daga cikin manyan nasarorin da aka samu akwai:

✅ Gyara da gina sabbin makarantun firamare 600.
✅ Gina sabbin ajujuwan karatu 1,254.
✅ Ɗaukar sabbin malamai 8,601 tsakanin shekarun 2019 zuwa 2024.
✅ Gina rijiyoyin burtsatse 122 domin samar da tsaftataccen ruwan sha.
✅ Gina bandakuna 125 a makarantu.
✅ Faɗaɗa shirin KwaraLEARN zuwa makarantu 870.
✅ Zuba sama da Naira biliyan 14 wajen bunƙasa ilimin matakin farko.

Wadannan matakai na daga cikin ƙoƙarin gwamnatin jihar na inganta ilimi, samar da ingantaccen yanayin koyarwa da koyo, tare da gina kyakkyawar makoma ga ɗaliban Jihar Kwara.

Gwamna Abba Kabir Yusuf Ya Samu Babbar Lambar Yabo Ta Duniya Kan Jagoranci A Fannin IlimiGwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba...
25/07/2026

Gwamna Abba Kabir Yusuf Ya Samu Babbar Lambar Yabo Ta Duniya Kan Jagoranci A Fannin Ilimi

Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya samu babbar lambar yabo ta International Literacy and Learning Leadership Award, bisa gudunmawar da ya bayar wajen inganta ilimi da kuma jajircewarsa wajen sauya fasalin tsarin ilimi a Jihar Kano.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sunusi Bature Dawakin Tofa, ya fitar a ranar Asabar.

Kamfanin Universal Learning Solutions (ULS) ne ya ba da lambar yabon a wani biki na musamman da aka gudanar a Stationers’ Hall da ke birnin London na ƙasar Birtaniya, a matsayin wani ɓangare na bikin cika shekara 20 da ƙaddamar da shirin Jolly Phonics a nahiyar Afirka.

Mai Martaba Sarkin Kano, Muhammadu Sanusi II, ne ya karɓi lambar yabon a madadin Gwamna Abba Kabir Yusuf, yayin da ya wakilce shi a wannan babban taron ƙasa da ƙasa da ya haɗa masana ilimi, abokan hulɗar ci gaba da masu tsara manufofi daga sassa daban-daban na Afirka da sauran ƙasashen duniya.

Address

Badarwa

2345

Telephone

+2348039214741

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Mairuwa News updated posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Shortcuts

  • Want your business to be the top-listed Media Company?

Share