16/08/2024
'ISRA’ILAWA A FALASƊINU KULLU-YAUMIN SAI SUN KASHE MUTUM'.
_Sheikh Ibraheem Zakzaky (H).
"Wannan inda Mutum yana bibiyan abin da ke faruwa, zai ga cewa tun k**awar watan Rajab, ko ma nace tun karshen JimadaThani, wanda ya yi daidai da farkon shekarar miladiyya din nan, kullu-yaumin Mutanen nan kisa suke yi, kullu-yaumin suna kashe Falasɗinawa ne, su je su kai musu hare-hare, Sojoji ne ɗauke da bindigogi da kwalkwali, da rigunan da ke kare kai daga harsashi, da manyan-manyan takalma, da miyagun shiga, idan ka gansu k**ar dodonni, su suke shiga su kutsa Unguwa-unguwa, Kullu-yaumin wai suna neman wai Ƴan ta’adda.
Duk wani saurayi ana iya k**a shi, harbi suke yi, kuma harbin nan da suke yi a ka suke yi, mafi yawan waɗanda s**a kashe a ka ne (an harbe su a kai), kuma mafi yawansu Matasa ne ƴan shekaru Goma sha zuwa shekaru Ashirin da wani abu, ko ‘yan shekaru Talatin da wani abu, mafi yawa ƴan ƙasa da Goma ne da kuma ƴan kasa da Talatin, mafi yawansu kuma suna harbinsu ne a ka, kullu-yaumin sai sun kashe Mutum, basu ma damu da abin da suke aikatawa ba..."
-CIKIN JAWABIN JAGORA SHAIKH IBRAHEEM ZAKZAKY (H) A RANAR QUDUS. 2023/1444.
’irar kaduna
08/Safar/1446
16/08/2024