Da’irar Kaduna

Da’irar Kaduna Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from Da’irar Kaduna, News & Media Website, Kaduna.

SANARWA! SANARWA!! SANARWA!!!Ƴan Uwa Musulmi Almajiran Sheikh Ibraheem Zakzaky (H) na garin Kaduna, suna gayyatar daukac...
30/10/2025

SANARWA! SANARWA!! SANARWA!!!

Ƴan Uwa Musulmi Almajiran Sheikh Ibraheem Zakzaky (H) na garin Kaduna, suna gayyatar daukacin al'ummah zuwa Zikiran tunawa da Shahidan Waki'ar Buhari na Shekara 2015 da Shahidan Harka Islamiyya ga badaya, kamar yadda s**a saba shiryawa duk bayan wata daya. Wannan karon taron Zikiran zai kasance akan Maudu'i kamar haka;
"MATASA DA GWAGWARMAYAR MUSULUNCI MAHANGAR SHAHEED AHMAD"

Wanda zai Gudana kamar Haka:-

Rana: Juma'a 31/October/2025

Wuri: Fudiyya Rimi

Lokaci: Karfe 3:00 na rana

Mai Jawabi:- Brother Abdullahi Sulaiman Bala

(Kar amanta da sanya baqaqen kaya Domin alamta juyayi)

SHAHIDAN MU GWARAZANMU

https://www.facebook.com/share/p/1BVoaCFJZ6/

Harisawan Matari Sub-Unit, sun gabatar da Aikin gayya.Ranar Laraba, 29/10/2025, Harisawan Matari Sub-Unit, dake Zaria Un...
30/10/2025

Harisawan Matari Sub-Unit, sun gabatar da Aikin gayya.

Ranar Laraba, 29/10/2025, Harisawan Matari Sub-Unit, dake Zaria Unit, Rasulul-Akram Zone. Sun gabatar da Aikin gayya Aikin gayya a Maƙabartar garin Matari, na rage ciyawar dake cikin ta.

— Hurras Media




Mu taimaki Sayyid Zakzaky karmugaji, domin shima bai gajima   Allah (T)
30/10/2025

Mu taimaki Sayyid Zakzaky karmugaji, domin shima bai gajima Allah (T)

IM Production dake shirin film na tarihin Sultan Attahiru sun ziyarci Jagora Sheikh Ibraheem Zakzaky (H), bayan sun kamm...
29/10/2025

IM Production dake shirin film na tarihin Sultan Attahiru sun ziyarci Jagora Sheikh Ibraheem Zakzaky (H), bayan sun kammala bada rahoton yadda aikin ke tafiya da cigaban da ake samu, Jagora (H) ya basu shawarwari da yi masu addu'ar fatan nasara.




28/10/2025

Za'a cigaba da zamun labarin Garin kaduna daga majiya masu inganci Wannan shine a lamar labaran da a ka tabbatar daga wa...
29/10/2025

Za'a cigaba da zamun labarin Garin kaduna daga majiya masu inganci

Wannan shine a lamar labaran da a ka tabbatar daga wannan da'irar ta Kaduna za'a daka wannan logon a jiki

Zamu da katar wa wannan shafin a cigaba da bibiyar da wadannan Shafukan

Zamu cigaba da kwafu muku labar daga shafukan kafin mu kulle wannan.

https://www.facebook.com/share/1GhJ6JAFQr/

https://t.me/kd_media_forum

https://www.youtube.com/

https://www.tiktok.com/?_t=ZS-90uVKq7eR1x&_r=1

https://x.com/kd_media_forum?t=mACxoNHaG05hLwP5A7cUsg&s=09

Follow the KD MEDIA FORUM 🌐 channel on WhatsApp: https://whatsapp.com/channel/0029VaeebOH2phHEplla0x3U

https://www.instagram.com/kd_media_forum

16/10/2025

JAWABIN JAGORA SAYYID IBRAHEEM ZAKZAKY (H) A LOKACIN DA DALIBAN HAUZAH ILMIYYA DA S**A ZIYARCI 02

16/10/2025

JAWABIN JAGORA SAYYID IBRAHEEM ZAKZAKY (H) A LOKACIN DA DALIBAN HAUZAH ILMIYYA DA S**A ZIYARCI 01

DALIBAN HAUZAH ILMIYYA SUN ZIYARCI JAGORA (H)Daga Ofishin Sayyid Ibraheem Zakzaky (H)‘Yan uwa daliban Hauzah Ilmiyyah, d...
15/10/2025

DALIBAN HAUZAH ILMIYYA SUN ZIYARCI JAGORA (H)

Daga Ofishin Sayyid Ibraheem Zakzaky (H)

‘Yan uwa daliban Hauzah Ilmiyyah, daga kasashen Iran, Iraq, Lebanon, Nijar da Mali sun gana da Jagora Shaikh Ibraheem Zakzaky (H) a gidansa da ke Abuja, a yammacin Talata, 20 ga Rabi’ul Thani, 1447 (14/10/2025).

Da yake jawabi ga maziyartan, Jagoran ya bayyana manufar ganawar, inda ya ce, don a tunatar da juna ne akan muhimmancin abinda s**a saka a gaba, ta yadda su kansu za su daura damara su dauki karatun da muhimmanci. “Ku san cewa kuna yin wannan (karatun) ne a matsayin sadaukarwa a madadin dukkanin al’umma.”

Jagora ya tunatar da su muhimmancin tsayuwa da karantar da mutane ilimi, ba kawai wa’azi irin yadda yanzu ake yayin masu wa’azi daban-daban a kasar nan suna yi a sigar hayaniya ba. Yace: “A zauna a yi karatu, a dauko littafi daga bango zuwa bango a karanta kowace kalma sanka-sanka a bi ta da bayani a wuce a sauke, sannan a dauko wani a sake sawa daga bango zuwa bango.”

Shaikh Zakzaky ya bayyana musu cewa, yana da kyau yin ma mutanen gari wa’azi. “Wa’azin da zai iya hada kan al’umma da fahimtar al’umma Musulmi a matsayin abu guda, wannan yana da kyau, ba wanda zai rarraba su ba.” Ya jaddada cewa: “ Amma karantarwa shi ne ‘ahammus shay’i.”

Jagoya ya ce, mutum ba zai karantar da ilimi ba, har sai in ya yi karatu, shi kuma karatun ana sadaukarwa ne a dauki lokaci a yi shi. Inda ya bukaci da su zama misalin kendir, wanda yake kona kansa don ya haska waje. “Abinda ya kamata ma’abota karatu su kasance kenan, su kona kansu don wasu su samu hasken ilimi.”

Ya kuma jaddada musu hadafin karatun a matsayin karatu don a karantar, inda ya ba da misali da yadda Malaman Zaure a kasar Hausa kan sadaukar su yi karatu mai zurfi don su karantar da sauran al’umma.

Jagora ya gargadi daliban ilimin akan tsayawa kyam akan tafarkin addini, ba tare da karkata ga azzalumai ba. Ya ce: “Abinda (wasu) suke ta kokarin su nuna mana shi ne, a zauna lafiya da hukuma. Mu ba mu ce ba za mu zauna lafiya da hukuma ba, amma a wane unwanin? A unwanin muna yaransu? Haihata! Haihata minnaz zilla! Haihata!”

Ya bayyana cewa, amma idan zama lafiya da su din a muna matsayin daidai da su ne, suna ganin mu ma ‘entity’ ne, suna bukatarmu, har suna neman abu a wajenmu, to Masha Allah, ka ga cigaba ne wannan. “Amma ka je a wulakance, kamar masu zuwa rarakan nan, har da cewa wai su ba a san da su ba, ba a yi da su, alhali suna da yawa suna da kaza, amma ba a wakiltansu…. To kaskanci ne wannan.”

Shaikh Zakzaky ya ce, abinda yanzu ake ta kitsa ma mutane kenan, su zauna lafiya da azzalumai. “Ban ki ba, idan mutum ya ga shi yanzu ba zai iya tsayawa kyam ya yi gwagwarmaya ba, ya koma waje daya ya ce koyarwa zan yi. Ba zan zarge shi ba.”

Ya ce: “Amma ya koyar din ne kawai, kada ya bude bakinsa ya ce masu gwagwarmaya laifi suke yi. Tunda shi ba zai iya ba, ya ja bakinsa ya tsuke, ya shiga lungu ya koyar. Ba zai iya wannan ba? To ya yi wannan din, amma kar ya zo ya ce, wadannan da suke wannan abin su bari.”

Ya kara da cewa: “Kowa ya yi nasa. Sadaukarwa ne, in ba za ka sadaukar ba, wani zai yi. An fahimta ai.”

Jagora ya ce, masu ganin cewa zama da mahukunta lafiya shi ne ‘aula’. Sai in ce, da haka nan ne, da Imam Husaini (AS) ya zauna lafiya da Yazidu, da ba a cire masa kai ba. Kuma na san ba za ka fi shi ganin maslahar al’ummar nan ba. Yace: “Yanzu irin wannan da’awar, su suna ganin kamar mu ne muke jefa kanmu a cikin wahala, mu muka ja ma kanmu.”

Don haka ya jaddada kira ga daliban ilimin akan lallai su san hadafin da ya kai su karatun. Wanda yace, hakan muhimmin abu ne. Ya yi musu nasiha akan su tsayu da karban karatu ne daga Malaman da suke karatu a wajajensu, amma su bar musu Fikirorinsu matukar ba ya dace da Fikirar da suke kai ne ba. “Da yake akwai masu Tunani daban daban a Hauzozi, a yi karatun kawai. Luga ne, ya iya Luga, ya koya maka Luga. Fiqihu ne ya iya, ya koyar. Usul ne ya iya, ya koyar. Amma ra’ayinka daban nasa daban, ya rike ra’ayinsa ka rike naka. Allahumma sai dai in ra’ayin naku iri daya ne, amma ba ka je ne a canza maka tunani ba. Yana da muhimmanci ka san diban karatun za ka yi don ka amfana, wani ya amfana da kai.” Ya jaddada.





14/10/2025

Taron tunawa da Shaheedan JASAZ yana cigaba da gudana.An fara taron ne da misalin ƙarfe 4:00PM na yama da bude taro da a...
14/10/2025

Taron tunawa da Shaheedan JASAZ yana cigaba da gudana.

An fara taron ne da misalin ƙarfe 4:00PM na yama da bude taro da addu'a da karatun Alkur'ani sai Malam Shamsudden Fudiyya ya gabatar da waƙe ga Shaheedan. Bayan nan, sai ziyarar Shuhada da Display na Firqatul Shaheed Humaid sai kuma Ƙasaitaccen Faretin girmamawa ga Shaheed Ahmad da sauran Shaheedan JASAZ wanda ɓangaren fareti s**a gabatar.

Sai discussion ya gudana akan 'Wake da alhakin kula da iyalan matasan Shaheedai bayan Shahadarsu' wanda shugaban Mu'assasatu Shuhada Amma Maryam Sani ta ƙarƙare bayanan.


‎Matasa Almajiran Shaikh Zakzaky sun gabatar da taron addu'o'i na musamman ga ruhin Shahid Ahmad Ibraheem Zakzaky Ɗa ga ...
13/10/2025

‎Matasa Almajiran Shaikh Zakzaky sun gabatar da taron addu'o'i na musamman ga ruhin Shahid Ahmad Ibraheem Zakzaky Ɗa ga Jagoran Harkar Musulunci a Najeriya Shaikh Ibraheem Zakzaky (H) a ci gaba da bukukuwan tunawa da ranar haihuwarsa.

‎Taron addu'o'in ya gudana ne a muhallin Makwancin Shahidai na Jannatu Darur Rahma da ke Dambo, a garin Zariya. Yau Litinin 13 ga watan Oktoba, 2025.

’irar Kaduna

Shahid Ahmad! Muna tunawa da kai a yau 13 ga watan Oktoba wadda ta yi daidai da ranar haihuwarka a shekara ta 1990. Yau ...
13/10/2025

Shahid Ahmad! Muna tunawa da kai a yau 13 ga watan Oktoba wadda ta yi daidai da ranar haihuwarka a shekara ta 1990. Yau shekara 35 (ƙidayar shamsiyya) ke nan cur da haihuwarka. Duk da cewa ka bar mu da gangan jikinka shekaru goma sha ɗaya da s**a gabata, mun san cewa, kai da ƴan'uwanka, kuna nan rayayyu a wajen Ubangijinku; kuna cin arzikin Sa.

Muna tunawa da ku kullum a zukatanmu da addu'o'inmu.

Muna roƙon Allah Ta'ala ya ba mu guzurin isowa inda ku ke.

Shahid Ahmad 13th October 1990 - 25th July 2014

Address

Kaduna

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Da’irar Kaduna posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share