Da’irar Kaduna

Da’irar Kaduna Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from Da’irar Kaduna, News & Media Website, Kaduna.

May Allah reward us and reward you with the testimony of our Lady of Women of the Worlds, peace be upon her       04/11/...
04/11/2025

May Allah reward us and reward you with the testimony of our Lady of Women of the Worlds, peace be upon her





04/11/2025

“KASHE KIRISTOCI BA JIHADI BANE!”__Jagora Shaikh Ibraheem Zakzaky (H)Ta yaya za ka kashe mutum don kawai ba addininku ɗa...
03/11/2025

“KASHE KIRISTOCI BA JIHADI BANE!”

__Jagora Shaikh Ibraheem Zakzaky (H)

Ta yaya za ka kashe mutum don kawai ba addininku ɗaya ba, ko don kuna da banbancin fahimta, sannan ka ɗauka wai jihadi kake yi? Duk wani mutumin da yake maka da’awa cewa; ɗan uwanka mutum, ko ma meye addininsa kashe shi ake yi, to ba addini yake koya maka ba, don addini ba kisan kai ba ne!

"Lokacin da Manzon Allah (S) ya zo bai samu mushirikan Larabawa suna bautar gumaka ba ne? To sai ya kashe su? Da ya kashe su da ina addinin yake? Kiransu ya yi har s**a musulunta s**a bi addinin! Manzon Allah (S) da kyawawan ɗabi’u ya yi nasara akan maqiya ba da yaqi ba! Dan haka Musulunci ba kisan kai ya koyar ba".

__Mujson Hadejiamedia Daga littafin ZANTUKAN HIKIMA Daga Fasahar Maganganun Shaikh Ibrahim Zakzaky (H) WallafarCibiyar Wallafa da Yada Ayyukan Shaikh Zakzaky (H) Shafi na 20

Dandalin Matasa Harakar Musulunci Na Garin Shinkafi Sun Gabatar Da Aikin Gayya Na Yashe Kwalbati (Gota).—Daga; Jabir Al'...
03/11/2025

Dandalin Matasa Harakar Musulunci Na Garin Shinkafi Sun Gabatar Da Aikin Gayya Na Yashe Kwalbati (Gota).

—Daga; Jabir Al'ansar.

A Ranar Asabar 30—10—2025 da ta gabata ne, Dandalin Matasa Harakar Musulunci ƙarƙashin jagorancin Sayyid Ibraheen Zakzaky (H), s**a gabatar da aikin gayya na yashe kwalbati a unguwar Ƴar Shantali titin gidan Abun Gajere da ke cikin ƙaramar hukumar Shinkafi Jihar Zamfara.

Gamayyar matasan da s**a haɗa da Maza da Mata sun shiga unguwar inda s**a gabatar da wannan aiki, a yayin aikin an yashe kwalbatin tare da kwashe ƙasa da sharar da s**a yi sanadin toshe kwalbatin, inda s**a kwashe s**a gyara hanyar ruwan.

Al'ummar unguwar sun nuna farin cikinsu da wannan aiki, matasan sun ɗauki tsawon lokaci suna gabatar da wannan aiki.

Alhamdulilla an fara aikin lafiya kuma an kammala lafiya.

Youth Forum Media Team
Imam Ali Arridha Sokoto Zone
03—11—2025

SHEKARU 11 DA WAƘI'AR BOM ƊIN ASHURA A POTISKUM Daga Ibraheem El-TafseerA ranar 11 ga watan Muharram na shekarar 1436, w...
03/11/2025

SHEKARU 11 DA WAƘI'AR BOM ƊIN ASHURA A POTISKUM

Daga Ibraheem El-Tafseer

A ranar 11 ga watan Muharram na shekarar 1436, wanda ya yi daidai da 3/11/2014, an fita Muzaharar Ashura a Potiskum, kamar yadda aka saba kowace shekara, an yi lafiya an kammala lafiya. An rufe Muzaharar ne a kusa da fadar Sarkin Fika dake Potiskum, to akwai 'yan Tamsiliya, sun taho Fudiyya, domin su cire kayan Tamsiliyar da ke jikinsu, yaran gari da yawa sun biyo su da kallo, sun zo daidai kofar gidan Marigayi Alhaji Jaji, sai kawai aka je fa musu Bom a tsakiyarsu.

Mafi yawansu yara ne ƙanana, sun hango wani da rawani a cikin 'yan Tamsiliyar, sun ɗauka wakilin 'yan'uwa Sayyid Mustafa Lawan Nasidi ne.

Tashin Bom ɗin ke da wuya, sai ga motar Sojoji ta iso wajen, suna isowa, s**a fara iface-iface, ga mutane kwance cikin jini, amma suna fadin cewa a watse a bar wajen, su kuma 'yan ISMA da Harisawa suna ƙoƙarin kwashe waɗanda s**a samu raunuka da waɗanda s**a yi shahada. Da s**a ga 'yan'uwa ba su bar wajen ba, sai s**a tafi s**a ƙaro yawa, har da tankar yaƙi (Igwa), tun daga nesa s**a fara harbin 'yan'uwa, harbi suke yi babu ƙaƙƙautawa, harbi suke kan mai uwa da wabi, shi ya sa a Shahidan har da mutanen gari da yawa.

Sun ƙaro yawa ne domin su kashe Sayyid Mustafa Lawan Nasidi tare da 'yan'uwan dake wajen gabaɗaya, su rushe Fudiyya, shi kenan sun shafe Shi'a a Potiskum, a cewar su.

Shi ne s**a turo tankar yaƙi (Igwa) ta nufo Fudiyya gadan-gadan tana harbi, sai wani ɗan'uwa, Shahid Muhammad Isah Adamu (ya yi shahada a Gyallesu) ya yi kwantan Ɓauna, ya haye saman tankar yaƙin, ya dinga dukan Direban tankar yaƙin da itace, sai da ya farfasa masa kai, ya masa jina-jina, shi ne Allah ya saka musu razani s**a yi kwana da Igwar, s**a gudu.

A wannan tayar da Bom da harbin da Sojoji s**a yi an samu Shahidai 30, 'yan'uwa kusan 50 ne s**a samu raunuka. Dubban jama'a ne s**a halarci jana'izar Shahidan, inda aka kaisu maƙabartar unguwar Jaji.

Jama'a da dama ne s**a zo ta'aziyya, ciki har da gwamnan jihar Yobe na wancan, Alhaji Ibrahim Gaidam da mai martaba Sarkin Fika.

-- Ibraheem El-Tafseer
03/11/2025

Yunƙurin haɗin Kan Malaman addinin Musulunci, Prof. Ibraheem Maqari da tawagarshi sun ziyarci Jagora Sheikh Ibraheem Zak...
02/11/2025

Yunƙurin haɗin Kan Malaman addinin Musulunci, Prof. Ibraheem Maqari da tawagarshi sun ziyarci Jagora Sheikh Ibraheem Zakzaky (H) yau Lahadi a gidansa dake Abuja.

Bayan gabatar da jawabai da shawarwari akan muhimmancin haɗin kai da kusantar juna tsakanin malaman addini, Jagora (H) ya ƙarfafi wannan ƙoƙari sannan yayi fatan alkhairi da samun nasara.




02/11/2025

02/11/2025

JAWABIN JAGORA (H) NA RUFE MU’UTAMAR DIN MEDIA FORUM A ABUJA JIYA ASABAR

JAGORA (H) YA RUFE MU’UTAMAR DIN MEDIA FORUM A ABUJADaga Ofishin Sayyid Ibraheem Zakzaky (H)Da yammacin Asabar 10 ga Jim...
01/11/2025

JAGORA (H) YA RUFE MU’UTAMAR DIN MEDIA FORUM A ABUJA

Daga Ofishin Sayyid Ibraheem Zakzaky (H)

Da yammacin Asabar 10 ga Jimadal Ula, 1447 (1/11/2025) Jagoran Harkar Musulunci, Shaikh Ibraheem Zakzaky (H) ya rufe Mu'utamar da Dandalin Yaɗa Labaran Harkar Musulunci (Media Forum) a gidansa da ke Abuja.

Mu'utamar ɗin wanda Media Forum ta shirya na yini daya a garin Abuja, ya tattaro mahalarta daga dukkan sassan kasar nan, tare da wakilai daga bangarori daban-daban na Media din Harka Islamiyya, inda aka gabatar da jawabai akan Maudu'ai daban-daban da s**a shafi aikin jarida da Nizami Harka Islamiyya.

A yayin jawabinsa, Jagora Shaikh Ibraheem Zakzaky ya fara da bayyana tarihin yadda al’amarin isar da sako ta hanyar ‘media’ ya faro a Harkar Musulunci da buga ‘yan takardu masu isar da sako, daga bisani aka yi yunkurin samar da Mujallar Turanci mai suna Al-Mizan a farkon shekarun 1980s, inda a farkon shekarun 1990s aka samar da jaridar Hausa ta Almizan mai falle biyu, daga baya ta rika fadada tare da tasiri mai girma dukkan sassan kasar nan.

Harwayau, Jagora ya bayyana yadda aka rika samar da Jaridun Turanci na Pointer, da Pointer Express, da kuma Mujallu irin su Mujallar Gwagwarmaya, Mujallar Mujahida da sauransu, wanda duk daga baya s**a kwanta. Inda ya dauki lokaci yana bayani akan zuwan Intanet, da yadda ya rika cigaba har zuwa ga samuwar ‘Social Media’, wanda ya kunshi rubutu, hoto, da hoto mai motsi, kuma ake amfani da shi wajen yada sakon kaitsaye a cikin lokaci, ba kamar yadda jaridun takarda suke da jinkiri ba.

Shaikh Zakzaky (H) ya ja hankalin masu bibiyan kafafen sadarwa akan su rika bashi lokacin da za su rika dubawa a kowane rana, domin kar ya rika cinye musu lokaci. Ya ce, “in ka lura da lokacin da kake ci a Social Media, za ka kuma tambayi kanka, awa nawa na yi a karatun Alkur’ani da Sallah da sauransu. Kamata ya yi kowane abu ka bashi lokacinsa, in ba haka ba sai ka bannata lokacinka, domin shi wannan abin na da cin rai.”

Ya kuma bayyana yadda Yammacin Duniya ke kokarin sarrafa kakafen, wanda dama mafi yawa mallakinsu ne. Yace, wanda ma ba nasu din ba ne, to s**an yi kokarin kutse a cikinsa don su samu cikakken daman iko da shi. Inda ya bayar da misali da yadda Tiktok ya rika fallasa ta’addancinsu, alhali suna iya ‘control’ din sauran kafafe irin su Facebook, wanda hakan yasa yanzu s**a yi kokarin sayen ‘share a Tiktok din, don su rika sa ido akan wadanda suke ‘posting’ abinda bai yi daidai da ra’ayinsu ba kamar yadda suke yi a sauran kafofin.

Jagora ya kuma jaddada muhimmancin kafafen na sadarwa, inda ya bayyana cewa sun fi kowane kafa isar da sako a yanzu, saboda su suna zuwa ga mutane ne nan take.

Ya nuna takaicinsa matuka, akan yadda ganin amfaninsa mai kyau, sai kuma makiya ke amfani mare kyau da shi wajen kirkiran farfaganda da karairayi, da kuma kirkiran rigingimu da hayaniyar da wasu da gangan suke tado maganar da za a yi ta musu da musayar raddodi, in an kammala akan wani abin saisu kara kunno wani daban. Ya ce: “Kamar wasu sun dauka idan suna surutai irin wannan ana ta zuzutasu, kamar yana daukaka sunansu ne. Suna son su yi kaurin suna ne.”

Yace: “Kar wannan masu neman su yi kaurin suna su dauke ma mutane hankali, ya kamata a yi banza da su ne, a yi kokari a gina abin kirki, wanda kuma shi ke wahala.

Jagora ya nuna takaicinsa akan yadda makiya addini ke ta kokarin sai sun baiwa ‘yan uwa Musulmi sunan kungiya, ya ce: “Tunda su sun ce su kungiya ne, wai ala dole mu ma kungiya ne. Kuma yanzu ma suna wani yayi, wai suna neman su yi kungiya, su ce wai har da mu a ciki. Nace haba! Ai linzami ya fi karfin bakin kaza! wani bai isa ya ce ya yi kungiya ya saka mu a ciki ba, mu mun wuce nan! Ba dai akan addinin nan ba.

“Mutane yanzu kowane na ta fito da wani abu, wai mu kungiya ce. Wa ya ce maka? Mu mun ce muna addini ne, mu muke ‘representing’ din addinin. Amma sai s**a ce wai har da kungiyar kaza, wai kungiyar Mazhaba. A kafafen watsa labaru, wai kungiyar Mazhabar Shi’a, ko ‘yan Shi’a, ko kaza. Wai ala dole, tunda su sun yi kungiya, to ku ma kungiya ne. To ku kuke da kungiya, mu muna addini ne, mu bamu da wata kungiya, mu abinda muke yi sunansa addini ne. Ku ku yi ta kungiyoyinku!” Inji Shaikh Zakzaky (H).

Ya kara da cewa: “Na’am, ku kungiya ne, amma mu ba kungiya ba ne, ba kuma za mu taba zama kungiya ba. Ba kuma za a taba saka mu a cikin kungiya ba. Mu addini muke yi. Addinin Musulunci. Tun farko bamu taba ce muku addinin Musuluncin kuma ya kasu kashi-kashi ba, ba mu taba ganinsa a kashi-kashi ba, mu mun san addinin Musulunci bai kasu kashi-kashi ba! Abu daya ne rak! Sakon da Manzon nan ya zo da shi daga wajen Allah. Illa-iyaka, zance ya kare.”

Harwayau, Jagora ya ja hankali akan kokarin gina Fikira Sahihiya na sanar da mutane mene ne addini a hakikarsa, da kuma yunkurin dawo da ikonsa ya tabbata daram a doron kasa, wanda yace makiya kan kasa fahimtarsa, su yi ta masa fassara daban-daban.

Ya bayyana yadda Alkur’ani ya kawo tarihin Annabawa da s**a zo s**a kirayi al’ummarsu daban-daban, yace sam ba a kan kungiya ko mulki ko sarauta suke ginawa da’awarsu ba. “Ana ce mutane su zo su bauta ma Allah a bisa ka’idar da aka saukar ne, abinda ake ce ma mutane kenan. Ba an ce musu su zo su shiga wata kungiya ne ba.”

Yace: “To mu ma mukan ce, tunda mun yi sa’a mu dama al’ummar Musulmi ne, abinda muke cewa, al’ummar ta dawo bisa addininta. Illa iyaka. Amma sai s**a ce ku kaza ne.”

Jagora ya ja hankali akan kar mu daka ta mutane wajen amsa sunan ‘yan kaza da suke saka ma mutane. Ya bukaci “a dora mutane ne akan Fikira Sahihiya na cewa, addini ake yunkurin tabbatarwa, addinin nan kuma sunansa Al-Islam, shi kuma Al-Islam din nan ‘shaamil’ ne, karkashinsa ne aka sami fahimta daban-daban. Fahimta daban-daban ba addinai ne daban-daban ba, fahimtar shi wannan addinin ne. Kuma ana batun in addinin ya kafu, to shi zai tafi ne bisa shi ka’idan addinin, ba son ran wani ba, ba fahimtar wani ba.”

Jagora ya jadda jan hankalin ‘yan uwa akan kar su bari a rika shagaltar da su da wasu abubuwan da ba shi ke gabansu ba. “Na san wasu janibobi da s**an fada tarko, in an zage su su yi zagi, ka ga an yi batsattsale a ciki. Kuma abinda wadancan suke so kenan. To kai kar ka yarda a kautar da kai daga abinda kake kai. Ka yi ta fadan abinda yake shi ne daidai. Mai zagi ya yi ta zage-zagensa, kai kuma ka yi ta yi, in ka daka tasa, za ka koma ne ka zama kana bashi amsa, kuma abinda yake so kenan. To mu kar mu daka tasu, ya zama kullum kokarin kwakkwafa mutane akan abinda yake shi ne daidai, da kuma tsayawa kyam, da yi domin Allah, yi don Allah, yi don Allah, insha Allah.”

Ya karkare jawabinsa da nasiha kamar yadda ya saba akan yin kpomai saboda Allah. Ya ce: “Ana yi ne saboda Allah. Yi don Allah, yi don Allah, yi don Allah, ba don ka yi suna ba. Kuma in ana tare ana aiki kar ka dauka kowa zai ba da hadin kai a yi lafiya lau a tafi, a’a dabi’an mutum ne, in aka tara mutane, sai an ji abubuwa, sai an ce, wannan shi ya yi kane-kane, ko kuwa wannan dan bani na iya, wancan in ba shi aka ce ba rigima za a yi. Wannan an dinga yi kenan, dama dan Adam ba a raba shi da wadannan abubuwan. Kai dai ka yi abinka kawai, in kana yi saboda Allah ne. In kana yi saboda mutane ne, sai ka bari in dominsu ne, amma in kana yi domin Allah ne sai ka yi.”

A karshe, Jagora ya rufe da addu’ar, Allah Ya ba mu ladan abubuwan da muke yi, kuma ya kai mu ga kyakkyawan natija.





01/11/2025

Tunatarwa:Daga Jagora Sayyid Ibraheem Zakzaky (H)“Abin da muke so daga gareka shi ne; in ka riƙe Mazhabar da ka gada, ko...
01/11/2025

Tunatarwa:

Daga Jagora Sayyid Ibraheem Zakzaky (H)

“Abin da muke so daga gareka shi ne; in ka riƙe Mazhabar da ka gada, ko kuma ka zaɓi wata (wanda) ba ka gada ba, to ka sani cewa akwai waɗansu daban, kuma suma ɓangare ne na addini, saboda haka sai kayi naka, in ka ga wani yana nasa ka zura masa ido, amma kar kace nasa ba addinin bane.

“Kuma wannan shi ne abin da ya shigo mana yanzu na ƙoƙarin a rarraba mutane, wai ace wannan addini (daban), wancan ma addini ne, wancan ma addini ne, wato kamar addinai muke dasu.

“Muna da addini guda ne (Musulunci) amma yana da makarantu, yana da Mazhabobi, kuma hakanan, zamu karɓeshi, mu kuma mun yarda cewa; lallai idan mutum yana Mazhaba ne zamu masa uzuri, kowace irin Mazhaba ce.

“Kuma mun yarda a tamu fahimtar kowace irin Mazhaba ka ke zamu iya bin ka Sallah, kuma Sallarmu tayi, kuma ba zamu sake (wata Sallar) ba hatta in kayi abin da mu in mun yi a wajenmu Sallar ta ɓaci, tunda kai a wurinka Sallah sahihi ka ke, muma a wurinmu yayi an yarda muyi”.

— Ɓangaren jawabin Jagora Shaikh Ibraheem Zakzaky (H) a yayin rufe Mu'utamar ɗin Sisters da Academic Forum a garin Katsina, a shekarar 2013.

— Cibiyar Wallafa Ayyukan Shaikh Zakzaky



1/11/2025

HARKAR MUSULUNCI TA NAJERIYA TA KARYATA ZARGIN KISAN KIRISTOCITa bakin Farfesa Abdullahi DanladiDaga: Resource Forum, Is...
01/11/2025

HARKAR MUSULUNCI TA NAJERIYA TA KARYATA ZARGIN KISAN KIRISTOCI

Ta bakin Farfesa Abdullahi Danladi

Daga: Resource Forum, Islamic Movement in Nigeria

Harkar Musulunci ta Najeriya, ƙarƙashin jagorancin Sheikh Ibraheem Zakzaky, ta daɗe tana tsayawa kan zaman lafiya, adalci, da haɗin kan ‘yan Najeriya ba tare da la’akari da addini, ƙabila ko jam’iyyar siyasa ba. Harkar na ganin cewa Musulunci da Kiristanci addinai ne guda biyu daga Allah waɗanda ke kira ga alheri, tausayi da gaskiya. A ganinta, Musulmi da Kiristoci suna da abubuwa da yawa da s**a haɗa su fiye da waɗanda s**a bambanta su, sai dai ‘yan siyasa masu son zuciya ne suke amfani da waɗannan bambance-bambancen don cimma burinsu.

A bisa tushen wannan akida, Harkar Musulunci ta yi imani cewa matsalar Najeriya ba ta addini ba ce, amma ta ɗabi’a da siyasa. Matsalar ta samo asali ne daga rashawa, son kai, da yaudara da manyan ‘yan siyasa ke yi wa talakawa. Duk da ana ta ƙoƙarin jefa Musulmi da Kiristoci cikin gaba, a gaskiya abokan gaban su na gaskiya su ne waɗanda ke sace dukiyar ƙasa suna ci gaba da zalunci. Sheikh Zakzaky ya sha faɗi cewa, “Talakan Kirista da talakan Musulmi ba su da matsala da juna; abokin gaban su na gaskiya shi ne tsarin zalunci da ke bautar da su duka.”

A bisa wannan fahimta ne Harkar Musulunci ta nuna damuwa da ƙaryar da tsohon shugaban Amurka, Donald J. Trump, ya yi, inda ya zargi gwamnatin Najeriya da goyon bayan “kisankai akan Kiristoci,” tare da barazanar sanya Najeriya cikin jerin “ƙasashen da ke da matsalar ‘yancin addini.” Trump da wasu ‘yan siyasa a Amurka sun yi ikirarin cewa “Musulmi masu tsattsauran ra’ayi” na kashe Kiristoci a Najeriya, har ma suna nufin a turo sojojin Amurka don “kare su.”

Harkar Musulunci ta Najeriya ta karyata waɗannan zarge-zarge gaba ɗaya, tana kiran su ƙarya, tunzura, da kuma haɗari. Ta bayyana su a matsayin wani ɓangare na farfaganda ta yammacin duniya da nufin tada fitina da neman hanyar tsoma baki cikin harkokin Afirka. Wannan irin zargi na karya yana watsi da ainihin matsalolin da s**a shafi siyasa da tattalin arzikin Najeriya, yana kuma rage ta zuwa labarin “yakin addinai” wanda bai dace ba.

A gaskiya, Musulmi da Kiristoci duka suna fama da matsalolin tsaro iri ɗaya — ta’addanci, fashi, da zaluncin gwamnati. Ana kashe mutane a arewacin ƙasar inda Musulmi s**a fi yawa, haka ma ana kai hari kan coci da unguwannin Kiristoci. Waɗannan ba yakin Musulunci da Kiristanci ba ne, amma sakamakon tsarin mulki mai cike da rashawa da rashin adalci.

Harkar Musulunci ta kuma bayyana rashin gaskiyar ‘yan siyasar Yammacin duniya waɗanda ke da hannu wajen ƙona ƙasashe da kashe Musulmi miliyoyi a Iraki, Afghanistan, da sauran wurare, amma yanzu suna ikirarin kare hakkin dan Adam a Afirka. A ganinta, wannan “tausayin” da suke nunawa Kiristoci ba gaskiya ba ne, illa kawai wata dabarar siyasa ce don raba kan ‘yan Najeriya da samun damar sarrafa albarkatun ƙasar.

Gwamnatin Najeriya ma ta mayar da martani ta bakin mai magana da yawunta, Kimiebi Imomotimi Ebienfa, inda ta musanta maganganun Trump, tana cewa “’Yan Najeriya na addinai daban-daban sun daɗe suna rayuwa tare cikin zaman lafiya.” Gwamnati ta kuma tabbatar da kudirinta na “ƙarfafa haɗin kai tsakanin addinai da kare rayuka da haƙƙin kowa.” Harkar Musulunci ta yaba da wannan matsayi, tana kuma kira ga gwamnati ta tabbatar da gaskiya da adalci domin samun zaman lafiya na gaskiya.

Harkar ta yi gargaɗi cewa ƙasashen waje sun dade suna amfani da addini don rusa ƙasashe da neman dalilin tsoma baki. Kiran Musulmi na Najeriya da sunan “radical Islamists” wani ɓangare ne na labarin ƙarya da Yammacin duniya ke yadawa don nuna addinin Musulunci a matsayin na tashin hankali. Wannan ra’ayi ba kawai yana karya Musulunci ba ne, har ma yana lalata zaman lafiya tsakanin Musulmi da Kiristoci.

Tun shekaru da dama, Harkar Musulunci ta yi aiki don bunƙasa tattaunawa da fahimtar juna tsakanin Musulmi da Kiristoci. Mambobinta suna ziyartar coci a lokutan Kirsimeti da Easter, haka ma shugabannin Kirista suna halartar taron Harkar a matsayin alamar zumunci. Harkar tana la’antar kowace irin hari da aka kai kan coci, kamar yadda take la’antar harin da ake kai wa masallatai. Manufarta ita ce cewa duk wanda ya kashe marar laifi, ba tare da la’akari da addininsa ba, kamar ya kashe dukkan bil’adama ne.

Harkar ta ci gaba da jaddada cewa zaman lafiya na gaskiya ba zai tabbata ba sai an samu adalci. Shugabannin Najeriya su daina amfani da siyasar yaudara da rarrabuwa, su maida hankali wajen yaki da rashawa, talauci, da rashin tsaro. Jama’a kuma su gane cewa rikicin addini kawai yana amfanar da masu satar dukiyar ƙasa. Idan talakawa sun rabu, azzalumai s**an fi samun ƙarfi; idan sun haɗu, zalunci zai rushe.

A ƙarshe, Harkar Musulunci ta kira Musulmi da Kiristoci su ƙi yarda da labaran ƙarya da ƙasashen waje da wasu ‘yan Najeriya ke yadawa don cin moriyarsu. Ya kamata mu haɗu a matsayin ‘yan ƙasa guda, mu dogara ga imaninmu da Allah da kuma burin samun ƙasa mai adalci da zaman lafiya.

Sakon Harkar ya bayyana a sarari: haɗin kan ‘yan Najeriya ya fi ƙarfi fiye da ƙaryar da ke neman raba su. Ainihin yakin ba tsakanin Musulmi da Kiristoci yake ba, amma tsakanin gaskiya da ƙarya, adalci da zalunci, amana da yaudara. Har sai mun haɗu don fuskantar wannan gaskiya, ba za mu tsira daga danniya ba.

Harkar Musulunci ta Najeriya ta tsayawa cikakke wajen zaman lafiya, adalci da haɗin kai, tana ƙin duk wani yunƙuri — na cikin gida ko na ƙasashen waje — da ke ƙoƙarin jefa ‘yan Najeriya cikin gaba ta sunan addini.

Sayyid Ibraheem Zakzaky Office

Fadin Sayyid Khamene'i (H) Ga Jagora Sayyid Zakzaky (H) Ina Jin Dadi Haduwa Da Ku Da Iyalanku Kai Misali Ne Na Gaskiya N...
01/11/2025

Fadin Sayyid Khamene'i (H) Ga Jagora Sayyid Zakzaky (H) Ina Jin Dadi Haduwa Da Ku Da Iyalanku Kai Misali Ne Na Gaskiya Na Mujahidi A Tafarkin Allah Muna Fatan Zaka Ci Gaba Da Wannan Gwagwarmaya

_Imam Khamene'i A Yayin Ganawarsa Da Jagora Sayyid Ibrahim Zakzaky (H) Da Iyalansa

A Ranar 14/10/2023

01/11/2025

Address

Kaduna

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Da’irar Kaduna posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share