Madogara TV/Radio

Madogara TV/Radio Kafar watsa labarai ce mai zaman kanta da aka samar domin yada labarai da rahotanni na gaskiya. Kafar watsa labarai mai hasko labarai masu amfanarwa.
(1)

Barayin Mashin Sun Jikkata Auwal Auta Kardi a AzareWani matashi mai suna Auwal Auta Kardi ya shiga mawuyacin hali bayan ...
08/10/2025

Barayin Mashin Sun Jikkata Auwal Auta Kardi a Azare

Wani matashi mai suna Auwal Auta Kardi ya shiga mawuyacin hali bayan da barayin mashin s**a kai masa hari jiya yayin da yake kan hanyarsa zuwa gidansa a kauyen Kardi, cikin garin Azare, Jihar Bauchi.

Rahotanni sun nuna cewa barayin sun kwace masa mashin, inda har s**a jikkata shi sosai s**a cire masa hannu guda kafin su tsere.

Yanzu haka yana kwance a Asibitin Tarayya na FUHSTH Azare a sashen gaggawa, inda yake karɓar kulawa.

Ana roƙon ’yan siyasa, ’yan kasuwa, da masu hannu da shuni da su taimaka masa wajen samun lafiya da jinya.

Ko a kwanakin bayama wadanan Batagarin sun jikkata wani a yayin da suke kokarin kwace masa abin hawan sa.

Kwacen waya kuwa Yazama Ruwan dare a garin na Azare.

Wanda Wannan lamari ya tayar da hankalin jama’a, yayin da al’umma ke kira ga hukumomi da su dauki matakin gaggawa kan karuwar ayyukan ta’addanci da fashi da makami a yankin Bauchi, musamman garin Azare, domin tabbatar da tsaro da zaman lafiya.

Idris Azare.

Tsohon Shugaban Kasa Ibrahim Badamasi Babangida zai gina asibiti a garin Kumurya da ke karamar hukumar Bunkure da ke Kan...
08/10/2025

Tsohon Shugaban Kasa Ibrahim Badamasi Babangida zai gina asibiti a garin Kumurya da ke karamar hukumar Bunkure da ke Kano, albarkacin kasancewarta mahaifar mahaifinsa.

📸: Ahmad Datti, Kano.

Sanata Dandutse na gab da kammala gina Sabon Dakin Karatu na Zamani a MalumfashiSanata Muntari Mohammed Dandutse, mai wa...
08/10/2025

Sanata Dandutse na gab da kammala gina Sabon Dakin Karatu na Zamani a Malumfashi

Sanata Muntari Mohammed Dandutse, mai wakiltar Katsina ta Kudu a majalisar dattawa, na gab da kammala gina sabon ɗakin karatu na zamani (Modern Library) a garin Malumfashi, jihar Katsina.

Wannan ɗakin karatu da aka tsare shi da tsarin zamani, ana kawata shi da kayan aiki na musamman, domin bai wa ɗalibai da matasa damar gudanar da nazari da bincike cikin sauƙi.

A cewar Sanata Dandutse, babban burin aikin shi ne samar da ingantaccen yanayi ga matasa domin karatu da kuma buɗe sabbin damar ci gaban ilimi a yankin da ma kasa baki ɗaya.

Masana harkokin ilimi sun bayyana cewa wannan aiki zai taimaka wajen ƙara sha’awar karatu da bincike, musamman a tsakanin matasa, tare da samar da muhalli da ya haɗa karatu da fasahar zamani.

Wani malami a Malumfashi ya shaida wa Dandutse Media Reporter cewa:

Akwai ɗimbin ɗalibai masu hazaka da ke bukatar irin wannan cibiya domin haɓaka karatunsu. Wannan aiki ya zo a daidai lokacin da ake bukatar sa, kuma zai yi tasiri sosai.”

Haka kuma, wasu matasa sun bayyana farin cikinsu da wannan dakin karatu, inda s**a ce zai ba su damar shiga tsarin karatu na zamani ba tare da dogaro da tsoffin hanyoyin neman bayanai kadai ba.

Ana sa ran cewa cibiyar za ta taka muhimmiyar rawa wajen raya ilimi da bunkasa tattalin arziki a yankin, musamman ta fuskar bincike, nazari, da kuma tallafawa matasa wajen samun ingantaccen ilimi.

Wannan aikin ya kasance cikin jerin manyan ayyukan raya ya ilimi da da raya kasa da Sanata Dandutse ya gudanar a shiyyar Katsina ta Kudu.

Sen. Dandutse Media Reporter

BADAƘALA DA KUDIN ALHAZAI: Hukumar EFCC ta Gayyaci Shugaban NAHCON, Sheikh Pakistan Bisa Zargin Wawure Naira Biliyan 50H...
08/10/2025

BADAƘALA DA KUDIN ALHAZAI: Hukumar EFCC ta Gayyaci Shugaban NAHCON, Sheikh Pakistan Bisa Zargin Wawure Naira Biliyan 50

Haɗaddiyar Hukumar Yaki da Cin Hanci da Rashawa ta (EFCC) ta gayyaci Shugaban Hukumar Alhazai ta Kasa (NAHCON), Sheikh Abdullahi Pakistan, domin ya bayyana kan zargin batar da kudade kimanin Naira biliyan 50 a hukumar.

Rahotanni sun bayyana cewa EFCC ta fara bincike kan yadda wasu makudan kudade da aka ware domin shirya aikin Hajji na bana s**a bace ba tare da cikakken bayani kan yadda aka kashe su ba.

Wata majiya daga cikin hukumar ta ce an gano wasu rashin daidaito a cikin kudaden da aka tara daga maniyyata da kuma yadda aka gudanar da ayyukan shirye-shiryen Hajji.

EFCC ta bukaci Sheikh Abdullahi Pakistan tare da wasu manyan jami’an hukumar NAHCON da ke da hannu a harkokin kudi su bayyana a ofishinta domin bayar da cikakken bayani kan lamarin.

Sai dai har yanzu, hukumar NAHCON ba ta fitar da wata sanarwa ba kan batun, ko kuma ta karyata zargin da ake yi mata.

COURT STOPS CONDUCT OF PARALLEL NATIONAL ELECTIVE CONGRESS OF NYCN*….. Orders Inspector General of Police, DSS to Enforc...
07/10/2025

COURT STOPS CONDUCT OF PARALLEL NATIONAL ELECTIVE CONGRESS OF NYCN

*….. Orders Inspector General of Police, DSS to Enforce Directives*

An FCT High Court in Abuja has issued an interim injunction restraining certain individuals from holding or proceeding with a purported parallel National Elective Congress of the National Youth Council of Nigeria, NYCN scheduled for today, pending the hearing and determination of a motion on notice in a suit before the Court.

It would be recall that the National Youth Council of Nigeria held its National Elective Congress from 19th to 22nd September, 2025 in Bayelsa State, where Sukubo Sara-Igbe Sukubo was legitimately re-elected as President of NYCN, alongside members of its National Executive Committee comprising both new and old members.

Justice J.E. Obanor of the FCT High Court issued the interim order upon hearing the motion Ex parte brought before it by Incorporated Trustees of the National Youth Council of Nigeria and Sukubo Sara-Igbe Sukubo on behalf of the National Executives of NYCN against the Respondents in the matter including Ademola Gbenga, Okechukwu Nnamene, Abel Abaji, Alex Allen Akin and Hassan Mamman.

The Court also ordered the Inspector General of Police and the Department of State Security Service, DSS who were joined as Respondents in the matter to enforce the order restraining the aforementioned individuals, their agents, privies or associates from holding or proceeding with a parallel National Elective Congress of NYCN today pending the determination of the motion on notice in the suit before the Court.

The Court adjourned the matter to 16th October, 2025 for hearing of the motion on notice.

Signed:

Media Unit,
Office of President of the National Youth Council of Nigeria (NYCN).
Monday 6th October, 2025.

ƘUDIRI: Shirin Fim Ɗin Hausa Mai Dogon Zango Na Farko Da Sama Mutum Miliyan Daya S**a Kalla Cikin Kwana Hudu. Ƙudiri sab...
07/10/2025

ƘUDIRI: Shirin Fim Ɗin Hausa Mai Dogon Zango Na Farko Da Sama Mutum Miliyan Daya S**a Kalla Cikin Kwana Hudu.

Ƙudiri sabon shirin fim ne mai nisan zango wanda ya sha bambam da waɗanda ake kallo. Shiri ne da aka zuba basira da lissafi wanda ke ƙunshe da zunzurutun fikira kamar irin finafinan da s**a yi suna a duniya na ƙasashen ƙetare.

Ƙwaƙwalwa ta taka muhimmiyar rawa a shirin, yayin da masu laifi s**a aikata kisan kai s**a toshe duk wata hujja da za a gano su, a lokacin su kuma ƙwararrun jami'an tsaro s**a zurfafa bincike cikin ƙwarewa. S

Ƙudiri, idan ka fara kallonsa ba za ka daina ba, idan ka kammala kallon na wannan makon za ka shafe mako guda cike da zumuɗi da ɗokin Alhamis ta zagayo domin ci gaba da kallon inda aka tsaya.

Sababbin fuska ne a cikin shirin amma saboda ƙayatuwarsa ya kafa tarihin da babu sabon shirin da ya taɓa kafawa. Inda ya sami mabiya sama da miliyan ɗaya cikin kwana huɗu kacal. Tabbas Ƙudiri sai ya danne duk wani shiri mai dogon zango da yake tashe a duniyar finafinan Hausa.

Domin shiri ne da ya zo da sabon salon da ba a taɓa ganin irinsa ba, ya zo da darusan rayuwa mabanbanta. Shiri ne da hatta jami'an tsaro sai sun ƙaru da ilmin cikinsa na bincike, basira, fikira da lissafi b***e kuma sauran jama'ar gari.

Da a ce ana shiri irin na Ƙudiri da Kannywood ta yi zarra a duniyar finafinai ta duniya, domin mafi yawancin shirye-shiryen Kannywood ana yinsu ne kan soyayya, shaye-shaye ko daba amma shi Ƙudiri na daban ne ya zo da wani salo da yake wahalar bayyanawa a baki dole sai mutum ya gani da kansa zai fahimta.

Ana sakin shirin a kowace ranar Alhamis, da karfe 8pm na dare a YouTube channel mai suna "Kannywood Exclusive TV"

Daga Imam Aliyu Indabawa

K**a Ummulkhair Iliyasu da tsare ta saboda kiran da take yi wajen gyara ayyukan gwamnati a Plateau State, musamman Jos N...
06/10/2025

K**a Ummulkhair Iliyasu da tsare ta saboda kiran da take yi wajen gyara ayyukan gwamnati a Plateau State, musamman Jos North, zalunci ne babba kuma cin zarafi ne a dimokuraɗiyya.

Na saurari bidiyoyinta a hankali, babu inda tayi zagi ko ta ɓata mutuncin wani.

Duk abin da take yi na neman wayar da kai da kokarin kawo gyara, akan doron doka suke.

Amma saboda wannan kira bai yi wa wasu ‘yan siyasa daɗi ba, aka maida shi dalilin tsare ta.

Muna kira da ƙarfi da babbar murya: a saki wannan baiwar Allah nan take.

ANYI KIRA GA ADALIN GWAMNA MALAM DIKKO RADDA DA YA GINA SABUWAR "KATSINA CENTRAL MARKET" DUBA DA YADDA KATSINA KE CIGABA...
06/10/2025

ANYI KIRA GA ADALIN GWAMNA MALAM DIKKO RADDA DA YA GINA SABUWAR "KATSINA CENTRAL MARKET" DUBA DA YADDA KATSINA KE CIGABA A KARKASHIN JAGORANCIN SHI.INJI HON AHMED MADUGU.

Anyi wannan kiran ne ayayin wani zama da akai da matasa yan kasuwa a cikin birnin katsina, Hon Ahmed madugu yace duba da irin ayyukan da Gwamna yakeyi na inganta garin katsina da fadada shi gina sabuwar Katsina central market ba karamin cigaba bane musamman ta bangaren tattalin arziki.
Misali.

* Zai samar ma jiha kudin shiga.
* Matasa da mutane zasu samu aikin yi domin rage Zaman banza da sace sace a cikin gari.

* Za'a fadada kasuwancin katsina da kuma ingan tashi.

* Garin katsina zai kara cigaba ta bangaren kasuwanci.
* Wasu daga ciki da wajen jihar,harma da kasashen ketare zasu saka hannun jarin su.
*
Dadai sauran makamancin irin wannan cigaban.

A bayanin shi ya danganta gwamnatin Malam Dikko Radda da babu irin ta wurin kawo cigaban al'umma tunda aka kafa dimukradiyya.

Hon Ahmed madugu ya kara dacewa ita kasuwar Fatima baika ya kamata duk wata kasuwa ta cikin gari su dawo nan.misali kamar kasuwar chake, kasuwar kofar keke da dai sauran su.

Haka kuma ita Fatima baika tayi kadan adai yadda katsina ke cigaba a yanzu sannan kuma an ginata tun lokacin abacha ne lokacin katsina na karamin gari.

Su kuma wayanda ke cikin Fatima baika ayi tsarin da kowa za'a maida mashi shagon shi a sabuwar kasuwar (replacement). Musamman ga fili nan tsakanin Fatima shema da sardauna estate. Idan aka dauketa tun daga t**in Fatima shema ta dangane har t**in strolling yadda zata samu fuska biyu ta t**i da kuma girma sosai.

A karshe Hon Ahmed Madugu ya kara da cewa a cigaba da yiwa katsina da gwamnatin katsina da maigirma gwamna Malam Dikko Radda addu'a Allah ya taimake ta Allah kuma ya taimake shi ya baki ikon cigaba da ayyukan alkairan da yake kawo mana Allah kuma ya kawo mana Zaman lafiya mai dorewa.

Dalilin da yasa ya kamata ayita.

*Cinkosan ababen hawa a Fatima baika.

*Fatima baika tayi karanta duba da yadda garin ke cigaba.

*Samar ma matasa dama al'umma aikin yi dan dogaro da kawunan su.

*Fatima baika ta tsofa dan tun lokacin abacha take.

*Cigaba da fadada katsina.
*Samun baki da manyan yan'kasuwa musamman yan Kasar Nijar dake ketarawa zuwa kano (nesa tazo kusa).

Mahaifiyar Attajirin Dan Kasuwa Alh Aliko Dangote, Wato Mariya  Sunusi Ɗantata, Kuma ƴar Wan Hamshaƙin Attajirin Wanda Y...
06/10/2025

Mahaifiyar Attajirin Dan Kasuwa Alh Aliko Dangote, Wato Mariya Sunusi Ɗantata, Kuma ƴar Wan Hamshaƙin Attajirin Wanda Ya Rasu Kwana Nan, Alh Aminu Alasan Ɗantata {Amin-Dogo}

Da yawa mutane ba su san wacece Mariya Sanusi Dantata ba, kawai dai suna kallon tacne a matsayin mahaifiyar shahararren Attajirin nan na Afrika Aliko Dangote.

Cikakken sunanta shine, Uwar Marayu da Marasa Gata, Domin idan zan yi maka ta babban mahaukaci zan iya rantse maka, duk fadin Afrika babu wanda ke ciyar da al'umma abinci tare da agazawa talakawa sama da ita, wallahil azim, ko Gwamnati ba za ta iya abinda wannan baiwar Allah take yi na ciyar da bayin Allah ba.

Saboda idan kazo gidan Mariya, sai ka tausayawa kudi, duk jihar Kano, duk Nijeriya, duk Afrika babu inda kudi suke kuka da ihu sama da gidan Mariya Sanusi Dantata, domin Mariya wani kamfani ta kafa na musamman domin ciyar da Bayin Allah tare da farantawa rayuwarsu.

Idan ka je kofar gidanta ka ga yadda ake ciyar da mutane kamar a wasan kwaikwayo, na san duk tsananin kiyayyar ka da Mariya Sanusi Dantata sai ka ce Ubangiji ya gafartawa Mariya.

Gidan Mariya ya zama wata inuwa wacce talakawa suke zuwa su huta, Mariya ta zama wata katanga wacce al'umma ke jingina da ita su sami saukin rayuwa. Abokina Sadik Abdullahi Koki
Tunda a unguwarku take ai zaka bada sheda akanta.

Malam ka zo jihar Kano kofar gidan Mariya a sannan za ka san wacece ita.

Akalla talakawa sama da dubu hamsin kullum suna cin abinci tun daga safe har zuwa dare a jikin Mariya domin da yawansu ba su da wata hanyar samun abinci sai a gidan Mariya.

Kullum ciyarwa ake yi gidan Mariya.

Abincin asibiti daban
Abincin gidan nakasassu daban.

Abincin Alumma na gari daban.

Banda wanda take rabawa mutane ba tare da an kirga ba.

Akalla Mariya tana da ma'aikan da take baiwa albashi sama da mutum dubu a karkashinta, wadanda ta ajiye saboda kawai kula da ciyar da Bayin Allah.

Daga Cikin ma'aikatanta akwai.

Masu saran itacen girki.
Masu nikan garin tuwo.
Masu dauko Itace.
Masu cefane daban.
Masu girki daban.
Masu rabon Abinci daban.
Masu markade daban.
Masu tuka mota

A yau Litinin, kotun hukunta manyan laifuka ta duniya ICC, ta samu wani jagoran mayaƙan sa kai na Sudan, wato Ali Muhamm...
06/10/2025

A yau Litinin, kotun hukunta manyan laifuka ta duniya ICC, ta samu wani jagoran mayaƙan sa kai na Sudan, wato Ali Muhammad Ali Abd-Al-Rahman, da aikata laifukan yaƙi da cin zarafin bil adama a lokacin da s**a rika ƙaddamar da munanan hare-hare a yankin Darfur.

Ƙarin bayani: https://rfi.my/C4ck

Dubban mutane ne s**a taru a Addis Ababa, babban birnin Ethiopia a ƙarshen makon da ya gabata domin yin bikin nuna godiy...
06/10/2025

Dubban mutane ne s**a taru a Addis Ababa, babban birnin Ethiopia a ƙarshen makon da ya gabata domin yin bikin nuna godiya ga ubangiji wanda 'yan ƙabilar Oromo suke gudanarwa duk shekara.

Bikin wanda ake kira Irreecha ana yinsa ne domin nuna godiya ga ubangijin ƙabilar Oromo mai suna Waaqa.

Wasu daga cikin mahalarta bikin suna yin al'adar da ake kira Waaqqeffannaa, wadda ta kasance bauta ga Waaqa.

Oromo ita ce ƙabilar da ta fi yawa a Ethiopia inda take da adadin da ya kai ɗaya cikin uku na mutum kusan miliyan 130 da ke ƙasar.

Suna yin amfani da bikin domin neman haɗin kai da zaman lafiya da kwanciyar hankali a ƙasar.

Ya Zama Wajibi Gwamnati Ta Kare Kamfanonin Dangote Saboda Cigaban Lasa -Mataimakin Shugaban Kasa Kashim Shettima Mataima...
06/10/2025

Ya Zama Wajibi Gwamnati Ta Kare Kamfanonin Dangote Saboda Cigaban Lasa -Mataimakin Shugaban Kasa Kashim Shettima

Mataimakin shugaban ƙasa, Kashim Shettima, ya ce Nijeriya ta fi ƙarfin ƙungiyar PENGASSAN, tare da jaddada cewa ya zama wajibi gwamnatin tarayya ta kare kamfanonin da ke ƙarƙashin rukunin Dangote Group, saboda rawar da suke takawa wajen bunƙasa tattalin arzikin ƙasar.

Shettima ya bayyana hakan ne yayin wata tattaunawa da manema labarai, inda ya bayyana shugaban kamfanonin rukunin Dangote, Aliko Dangote, a matsayin “fitila ga Nijeriya” a ɓangaren kasuwanci da tattalin arziki.

“Yadda muke mu’amala da shi, haka ’yan ƙasashen waje za su ɗauke mu,” in ji Shettima.

Ya ce da Aliko Dangote ya so, da ya zuba jarinsa na dala biliyan 10 a kamfanonin fasaha irin su Microsoft, Amazon ko Google, kuma da watakila ya riga ya tara ribar tsakanin dala biliyan 70 zuwa 80 a yanzu.

Sai dai, a cewar Shettima, Dangote ya zabi ya zuba jarinsa a Najeriya domin haɓaka tattalin arzikin ƙasar, don haka gwamnati da ’yan Najeriya gaba ɗaya su ba shi cikakken goyon baya.

“Wajibi ne mu kare muradunsa da kamfanoninsa, saboda ci gaban ƙasarmu gaba ɗaya,” in ji mataimakin shugaban ƙasar.

Address

Gwargwaje Birnin Gwari Road Opposite Old KAEDCO Office, Zaria
Kaduna
800102

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Madogara TV/Radio posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Madogara TV/Radio:

Share