Kidaya

Kidaya Kidaya Is Online Newspaper that features truthful and reliable information in Nigeria and beyond. We

YANZU-YANZU :  Tunibu ya sauka Kano Domin ta' aziyyar Marigayi Alhaji Aminu Dantata.
18/07/2025

YANZU-YANZU : Tunibu ya sauka Kano Domin ta' aziyyar Marigayi Alhaji Aminu Dantata.

Sheikh Professor Isa Ali Pantami ya ziyarci karamar hukumar Nguru, kan hanyarsa ta halartar babban taro a jami'ar Tarayy...
13/07/2025

Sheikh Professor Isa Ali Pantami ya ziyarci karamar hukumar Nguru, kan hanyarsa ta halartar babban taro a jami'ar Tarayya dake Gashua.

Sheikh Prof Isa Ali Pantami, ya fara ziyartar gidan mu'assas na cibiyar yada addinin Musulunci dake Nguru (Zaid bin Thabit) Engr Ibrahim Yakubu Nguru daga nan ya shiga ziyarce-ziyarce a cikin garin na Nguru wurin iyaye da dattawan gari.

Yadda Aka Gudanar da Bikin Makon Ƙungiyar Ɗaliban Aikin Jarida (MACOSA Week) A Jami’ar Tarayya Kashere, Jihar GombeA jiy...
01/07/2025

Yadda Aka Gudanar da Bikin Makon Ƙungiyar Ɗaliban Aikin Jarida (MACOSA Week) A Jami’ar Tarayya Kashere, Jihar Gombe

A jiya Litinin, Ƙungiyar Ɗaliban Sashen Kimiyyar Yada Labarai ta Jami’ar Tarayya Kashere (MACOSA) ta kammala bikin makonta cikin wani gagarumin taron ilimi na musamman (symposium) da aka shirya domin faɗaɗa tunanin ɗalibai da mahalarta kan ci gaban fasaha da tasirinta a fannin aikin jarida.

Babban bako kuma mai jawabi na musamman (Keynote Speaker) a taron shi ne mai girma Shugaban Jami’ar Tarayya Kashere, Farfesa Umaru A. Pate mashahurin masanin kimiyyar yada labarai da ilimin sadarwa, wanda ya yi fice a Najeriya da ma duniya baki ɗaya.

Taken Taron:

Juyin Juya Halin Fasahar AI a Fannin Jarida: Muhimman Hanyoyin Kiyaye Ka’idoji da Mafi Kyawun Ayyuka.”

A cikin jawabinsa, Farfesa Pate ya yi bayani mai zurfi kan yadda fasahar wucin gadi (Artificial Intelligence - AI) ke sauya fasalin aikin jarida, daga matakin rubuce-rubuce zuwa tantancewa da rarraba labarai. Ya bayyana yadda AI ke kawo sauƙi da sauri wajen gudanar da aiki, amma a lokaci guda yana haifar da manyan ƙalubale dangane da sahihanci, amincewa, da kiyaye ka’idojin aikin jarida.

Ya jaddada bukatar ɗalibai da malamai su fahimci wannan sauyi a matsayin wata dama ta ci gaba, amma mai buƙatar ilimi, ƙwarewa da kiyaye ƙa’idodi. Har ila yau, ya nuna muhimmancin koyarwa da tsara manufofi masu inganci wajen amfani da fasahar AI, domin kare martaba da darajar aikin jarida.

Taron ya kasance mai cike da nishadi, ilmantarwa da tattaunawa mai zurfi tsakanin kwararru, malamai da ɗalibai, inda aka bayyana ra’ayoyi mabanbanta kan makomar aikin jarida a wannan zamani na dijital.

✍️ Muhammad Chigari Kumo

Arewa Media Writers Na Kira Ga Gwamnatin Tarayya Da Jihohin Filato Da Benue Kan Kisan Matasan ArewaDaga Arewa Media Writ...
25/06/2025

Arewa Media Writers Na Kira Ga Gwamnatin Tarayya Da Jihohin Filato Da Benue Kan Kisan Matasan Arewa

Daga Arewa Media Writers

Ƙungiyar marubutan Arewa a kafafen sada zumunta, Arewa Media Writers, ƙarƙashin jagorancin Comr Haidar H. Hasheem, ta bayyana damuwa da alhini game da kisan gillar da aka yi wa matasan Arewa a jihohin Filato da Benue a cikin makon nan, tare da kira ga gwamnati da hukumomin tsaro da su gaggauta ɗaukar mataki.

A cewar ƙungiyar, a jihar Benue, an kashe Barhama Suleiman da Jamilu Ahmad, matasa 'yan asalin jihar Kano, bayan da wasu da ake zargin ‘yan ta’adda ne s**a tare motarsu s**a hallaka su. An gudanar da jana'izarsu a babban masallacin ƙasa da ke Abuja, inda manyan jami'ai ciki har da Nuhu Ribadu da Gwamna Abba Kabir Yusuf s**a halarta.

Haka kuma, a jihar Filato, matafiya daga Zaria, yawancinsu ’yan asalin Basawa, sun rasa rayukansu yayin da suke kan hanyarsu ta zuwa bikin aure. Akalla mutum 12 ne s**a mutu a harin da aka kai a karamar hukumar Mangu.

Ƙungiyar ta bayyana cewa kisan gillar ba sabon abu ba ne, domin an dade ana kai wa 'yan Arewa hari a waɗannan yankuna, amma ba a ganin hukunci ko mataki daga hukumomi. Wannan shiru da sakaci na gwamnati yana ƙara nuna gazawar tsarin tsaro da rashin adalci ga ’yan Arewa.

Shin rayukan ‘yan Arewa ba su da ƙima? Ko kuwa gwamnati na da hannu a ciki ?

Arewa Media Writers ta yi kira ga Gwamnatin Tarayya da jihohin da abin ya shafa da su:

1. Gaggauta bincike da gurfanar da masu hannu a gaban kuliya.

2. Bayyana matsayi a fili kan kisan gillar da ake wa ‘yan Arewa.

3. Hukumomin tsaro (’Yan Sanda, DSS) su gudanar da bincike tare da bayyana sak**akon.

4. Majalisar dokoki ta kaddamar da bincike kai tsaye kan yawaitar kashe-kashen ’yan Arewa.

Ƙungiyar ta ƙara da cewa, irin wannan rashin adalci na barazana ga zaman lafiya da hadin kan Najeriya, don haka dole ne a tabbatar da cewa jinin ɗan Arewa yana da daraja k**ar na kowa.

Idan gwamnati ba za ta kare rayukan ‘yan Arewa ba, mu da harshenmu da alkalumanmu za mu ci gaba da tashi tsaye har sai an yi mana adalci.







Rubutawa, Muhammad Kwairi Waziri, National Director Media And Publicity II Arewa Media Writers.

Duk Wanda ya sayi Datar 1GB ta MTN mai 30DAYS a cikin Application din ABBA PANTAMI DATA LTD, to sai tayi kwanaki 30 sann...
22/06/2025

Duk Wanda ya sayi Datar 1GB ta MTN mai 30DAYS a cikin Application din ABBA PANTAMI DATA LTD, to sai tayi kwanaki 30 sannan za tayi Expired

Ministan Abuja Nysome Wike Ya Sanya Wa Ɗakin Taro Na Kasa Da Kasa Da Ya Sabunta, Sunan Shugaban Kasa Bola Tinubu
10/06/2025

Ministan Abuja Nysome Wike Ya Sanya Wa Ɗakin Taro Na Kasa Da Kasa Da Ya Sabunta, Sunan Shugaban Kasa Bola Tinubu

Kwamishinan Ayyuka Na Musamman A Jihar Akwaibom, Ini Ememobong Ya Yi Murabus Daga Muƙaminsa, Saboda Ba Zai Sauya Sheƙa Z...
06/06/2025

Kwamishinan Ayyuka Na Musamman A Jihar Akwaibom, Ini Ememobong Ya Yi Murabus Daga Muƙaminsa, Saboda Ba Zai Sauya Sheƙa Zuwa Jam'iyyar APC Ba, Bayan Gwamnan Jihar Ya Sanar Da Ficewarsa Daga PDP Zuwa APC

Shekaru Biyu A Gwamnatin Da Ta Dawo Da Martabar Jihar  KanoA lokacin da Gwamna Abba Kabir Yusuf ya hau karagar mulki a r...
04/06/2025

Shekaru Biyu A Gwamnatin Da Ta Dawo Da Martabar Jihar Kano

A lokacin da Gwamna Abba Kabir Yusuf ya hau karagar mulki a ranar 29 ga Mayu, 2023 al’ummar Kano sun fara ganin sauyi na gaske. Sauyin da ya tabbatar da aiki, tsare-tsare, da kula da lafiyar al’umma da tattalin arziki wannan ba mulki ba ne na alkawari kawai, wannan mulki ne mai cike da aiki da cika alkawari.

A cikin shekaru biyu kacal, Gwamna Abba Kabir Yusuf ya tabbatar da cewa mulki nagari ba a magana ba ne, aiki ne da kishin al'umma

A bangaren noma da ban ruwa, sama da hectare dubu an samar da su domin noman rani, tare da gine-ginen dam-dam a kananan hukumomi fiye da goma sha biyu.

A fannin lafiya, an cire dubban masu rijista na bogi, an dauki matakan inganta kulawa da marasa lafiya, tare da shigar da dubban talakawa cikin tsarin lafiya kyauta.

Gwamnatin Abba ta kawo karshen matsalar rashin magunguna a asibitoci, ta kafa cibiyoyi na musamman da samar da injinan iskar oxygene masu amfani da hasken rana.

An ba da kulawa ta musamman ga yara da mata masu fama da cututtuka ta hanyar shirin ABBACARE, tare da tallafawa masu sikila da marasa galihu.

Tsarin rajista da kididdiga na zamani (EMR) ya kara inganta tsarin lafiya da sarrafa bayanai a asibitoci fiye da goma.

Gaskiya ce, Gwamna Abba Kabir Yusuf yana aiki tukuru, yana gina jihar Kano bisa gaskiya, adalci da amana. Wannan gwamnatin ba ta yi alkawarin da ba ta cika ba cikin shekara biyu da fara mulkin jihar Kano!

ABAISWORKING
📅 29th May, 2025
Wanda ya shuka nagarta, shi zai girbi tagomashi

AJAM Ta Yaba Wa Gwamnatin Tarayya Kan Nasarorin Da Ta Cimma Wajen Dawo da Zaman Lafiya a ArewaGamayyar Kungiyar Ayyukan ...
01/06/2025

AJAM Ta Yaba Wa Gwamnatin Tarayya Kan Nasarorin Da Ta Cimma Wajen Dawo da Zaman Lafiya a Arewa

Gamayyar Kungiyar Ayyukan Arewa (AJAM) ta jinjina wa Gwamnatin Tarayya bisa manyan nasarori da ta samu wajen dawo da zaman lafiya da tsaro a yankin Arewa, wanda da can ya kasance cike da matsalolin ta’addanci da miyagun laifuka.

Kungiyar ta bayyana musamman rawar da Ma'aikatar Tsaro ke takawa wajen aiwatar da manyan ayyukan tsaro masu amfani da fasahar zamani a yankunan Arewa maso Yamma da Arewa maso Tsakiya.

A cikin wata sanarwa da mai jagorantar kungiyar, Lauretta Bako ta fitar a ranar Alhamis, AJAM ta bayyana cewa an samu gagarumin ci gaba a fannin tsaro a yankin, wanda hakan ya biyo bayan dabarun rundunonin tsaro da gwamnatin ke aiwatarwa.

"A yau muna rayuwa a wani sabon yanayi na tsaro fiye da da, inda aka kore Boko Haram zuwa matsugunan duhu, yayin da shugabannin masu garkuwa da mutane da ‘yan bindiga s**a hallaka ko s**a tsere."

"Nasarorin da aka samu wajen kawar da ‘yan bindiga, ‘yan ta’adda da kuma sarkakiyar hanyoyin aikata laifi, tare da farfado da tattalin arzikin yankuna, ya nuna ingancin wannan tsari."

A cewar AJAM, daya daga cikin ginshikan wannan nasara shine Operation FANSAR YAMMA, wanda ya samu nasarori da dama, ciki har da hallaka sanannen shugaban ‘yan bindiga, Kachalla Dogo Isah, tare da wasu ‘yan ta’adda 44 a jihar Zamfara.

Sanarwar ta kara da cewa, “Kashe fitattun masu aikata laifi ciki har da masu sayar da mak**ai da shugabannin ‘yan bindiga ya tarwatsa manyan hanyoyin aikata laifi, tare da isar da sako ga sauran masu laifi cewa gwamnati ba za ta yarda da rashin tsaro ba.”

Tasirin wadannan matakan tsaro ya wuce kidayar alkaluma kawai; yana da tasiri kai tsaye ga rayuwar yau da kullum ta ‘yan kasa. Hanyoyi k**ar hanyar Kaduna-Abuja, wanda da can aka fi jin tsoro, yanzu sun fi aminci ga matafiya, hakan kuma yana taimakawa wajen kasuwanci da zirga-zirga.

Kasuwanni a wurare irin su Giwa, Birnin Gwari da Jibia suna samun sabuwar rayuwa, inda shugabannin al’umma da jama’a ke tabbatar da ingancin tsaro. Farfadowar harkokin kasuwanci na da nasaba kai tsaye da nasarorin da sojoji s**a samu tare da samar da yanayi mai kyau ga kasuwanci.

Gina Brigade na National Mission Force a Samaru Kataf shima ya taka rawa wajen warware matsalolin tsaro a Kudu ta Kudancin Kaduna, wanda ya haifar da ingantattun yanayin zamantakewa da tattalin arziki. A cikin watanni ukun farko na shekarar 2025 kadai, an hallaka ‘yan ta’adda 122 kuma an k**a fiye da 1,000 daga cikin masu laifi.

A matsayinmu na Arewa Joint Action Movement, muna tare da kokarin da Ma’aikatar Tsaro ke yi wajen kare al’ummominmu da dawo da fata a zukatan jama’a. Muna fahimtar cewa har yanzu akwai kalubale, amma nasarorin da aka samu sun haskaka mana hanya. Zamu ci gaba da goyon bayan manufofi da matakan da za su kawo zaman lafiya, tsaro da cigaba mai dorewa a Arewarmu.

YAN SIYASA DA YARANSU KASHI NA 1Yan Siyasa Yaran dakuke Tare Dasu Basuda Wata Bukata Agunku Dayawuce Kutemakesu Afanni D...
04/05/2025

YAN SIYASA DA YARANSU KASHI NA 1

Yan Siyasa Yaran dakuke Tare Dasu Basuda Wata Bukata Agunku Dayawuce Kutemakesu Afanni Daban Daban.

Duk Wani Yaron Dan Siyasa Burinsa Yaga Maigidansa Yatemak**asa Afannin Karatunsa Ko Basa Appointment Kokuma Basa Jari Dan yadogara da Kansa wanda shima sanadinsa wasuma sudogara dakansu Amma Yaran Yan Siyasa kalilan ne suke samun Tallafin daga iyayen gidansu.

Da yawan Yan Siyasar mu Basucika Temakon yaran dasuke Tare dasuba Musamman Wajen Biyamusu kudin Makaranta Basu appointment ko jari Saide Lokaci Bayan Lokaci Akebasu 5k 10k kokuma 20k Mai kokari shine yabasu 50k Amma banda haka babu wani Moran da yaran sukewa masu gidansu saide sune masu Gidan suke Moran Yaransu.

Gaskiya Ina Jan hankalin Yaran Dasuke tareda iyayen gidansu basu temakonsu Kuma basujansu ajiki Dasu tashi tsaye Sukoma Kan sana'o'insu na hanu sucigaba saboda iyayengidansu batemakonsu zasuyiba.

Yan Siyasa yak**ata kafin kutemaki Kowa kufara Temakon yaranku dakuke taredasu Dan sune suketaredaku dajimawa Kuma suke muku biyayya Dan kare martabanku Kutemakamusu da Biyan kudin Makaranta basu Appointment Dakuma basu Jari Dan sudogara dakansu.

Fatanmu Allah yasa a gyara Allah Yasa Mufahinci hakan Amin Yaa Hayyu Yaa Qayyum.

Yasir Alhassan Gombe

Da Naira Biyar (5) kacal zaka iya ceton rayuwar wannan Bawan Allan🥹Aikin alkhairi baya ƙarewa awurin musulmi. Wannan mut...
17/04/2025

Da Naira Biyar (5) kacal zaka iya ceton rayuwar wannan Bawan Allan🥹

Aikin alkhairi baya ƙarewa awurin musulmi.

Wannan mutumin sunan sa Muhammed Y Maliki dake zaune a Karamar hukumar Akko, Gombe State Allah ya jarrabeshi da ciwon cancer.
Ya sha fama tsawon shekaru amma yar yanzu baigama warkewa ba!

Yanzu haka ana neman kudi da za'a mai aiki (Theater) Asibitin (Federal Teaching Hospital Gombe) ana neman naira Dubu 114,700 amma bashida halin biya, ya neman don Allah a taimaka masa! 🥲

Ga numbers waya da za'a iya tuntu6a 07061490387 ko 09130503836 zaku iya kira domin neman ƙarin bayani.

Saboda haka bayin Allah yan uwa musulmi, aikin alkhairi irin wannan ba baƙo bane awurinku.

Fisabilillahi mutaimake wannan mutumin da gwargwadon abunda Allah yahore mana

Tun daga N5 N10 N20 N50 N100 N500 N1000 N10,000 N20,000 N50,000 ko N1 Allah yahorema katuro fisabilillah domin ceton rayuwar sa.

Ga account details k**ar haka:

5894076181
Mohammed Y Maliki
Moniepoint

Ku taimake wannan Bawan Allan da kudi, addu’a ko kuyi sharing post zai iya yuwa acikin followers ɗinku asamu wanda zai taimaka.

Allah yabata lafiya ameen
Allah yasa adace ameen.

✍️Basiru M Kawu

A ganinku Wane bayani ne za'ayi wa wannan bazawarar har ta amince ta koma Gidan Tsohon Mijìñta?
07/04/2025

A ganinku Wane bayani ne za'ayi wa wannan bazawarar har ta amince ta koma Gidan Tsohon Mijìñta?

Address


Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Kidaya posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Shortcuts

  • Address
  • Alerts
  • Claim ownership or report listing
  • Want your business to be the top-listed Media Company?

Share