AHMAD MEDIA

AHMAD MEDIA Labarai Nishadantarwa Ilimantarwa Wassani

Real Madrid ta kori Alanso bayan Rashin Nasara da s**ayi a hannun bacalona jiya 🤔🤔🤔
12/01/2026

Real Madrid ta kori Alanso bayan Rashin Nasara da s**ayi a hannun bacalona jiya 🤔🤔🤔

Allah yayiwa Malam Mansur Arzai Rasuwa Janaizarsa Karfe 2:00 a Arzai Allah ya jikansa ya yafemasa.
12/01/2026

Allah yayiwa Malam Mansur Arzai Rasuwa Janaizarsa Karfe 2:00 a Arzai Allah ya jikansa ya yafemasa.

Bacalona ta zura Kwallo 3 yayin da madari take 2 karshen wasa..
11/01/2026

Bacalona ta zura Kwallo 3 yayin da madari take 2

karshen wasa..

Labari Da Ɗumi-Ɗuminsa Mataimakin Shugaban Ƙasa Kashim Shettima ya gwangwaje jarumi Adam A. Zango da dalleliyar mota da ...
08/01/2026

Labari Da Ɗumi-Ɗuminsa

Mataimakin Shugaban Ƙasa Kashim Shettima ya gwangwaje jarumi Adam A. Zango da dalleliyar mota da kap Kannywood babu mai irinta domin ya ji daɗin zirga-zirga biyo bayan hatsarin da ya yi da matarsa a kwanakin baya.

Wani fata za ku yi masa?

Da ɗumi-ɗumi: Gwamnonin Bauchi da Oyo na shirin komawa jam’iyyar ADC. Akwai alamu mai karfi da ke nuna cewa Gwamnan Jiha...
06/01/2026

Da ɗumi-ɗumi: Gwamnonin Bauchi da Oyo na shirin komawa jam’iyyar ADC.

Akwai alamu mai karfi da ke nuna cewa Gwamnan Jihar Bauchi, Bala Abdulkadir Mohammed, da kuma Gwamnan Jihar Oyo, Seyi Makinde, na dab da komawa jam’iyyar African Democratic Congress (ADC).

Majiyoyi masu kusa da lamarin sun bayyana cewa, idan wannan mataki ya tabbata, zai iya girgiza taswirar siyasar Najeriya gabanin babban zaben 2027.

Rahotanni na nuni da cewa wannan sauyin sheka na daga cikin manyan shiryayyen sauye-sauye da wasu manyan ‘yan siyasa ke yi domin neman wata sabuwar kafa ta cimma manufofinsu da burinsu na siyasa.

Gwamna Bala Mohammed da Gwamna Seyi Makinde na daga cikin manyan jiga-jigan siyasa da ke da karfin tasiri da gindin magoya baya a jihohinsu.

Shigarsu jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) na iya kara wa jam’iyyar armashi da karfi a matakin kasa, musamman a yankin Arewa da Kudu maso Yamma.

Muna yiwa masu ziyartar wannan shafi namu me Albarka Barka da sabuwar shekara 2026 Allah ya hadamu da Alkhairin da yake ...
31/12/2025

Muna yiwa masu ziyartar wannan shafi namu me Albarka Barka da sabuwar shekara 2026 Allah ya hadamu da Alkhairin da yake cikin ta Ameen

Da ɗumi-ɗumi: Peter Obi ya fice daga LP, ya koma jam’iyyar ADC.Tsohon ɗan takarar shugaban ƙasa a zaɓen 2023, Peter Obi,...
31/12/2025

Da ɗumi-ɗumi: Peter Obi ya fice daga LP, ya koma jam’iyyar ADC.

Tsohon ɗan takarar shugaban ƙasa a zaɓen 2023, Peter Obi, ya sanar da ficewarsa daga jam’iyyar Labour Party (LP) tare da komawa jam’iyyar African Democratic Congress (ADC).

Peter Obi ya bayyana hakan ne yayin wani taron siyasa, inda ya ce wannan mataki wani ɓangare ne na sabon tsari da hangen nesa na ceto da gyara siyasar Najeriya, musamman yayin da ake tunkarar zaɓen shekarar 2027.

A cewar Obi, ya ɗauki wannan shawara ne bayan dogon nazari, yana mai jaddada cewa burinsa shi ne gina adalci, shugabanci nagari da tsarin siyasa mai amfani ga talakawan ƙasa.

Ƙetarewar Obi ta haifar da ce-ce-ku-ce a faɗin ƙasar nan, inda magoya bayansa ke kallon matakin a matsayin sabon babi na gwagwarmayar siyasa, yayin da wasu ke jiran ganin tasirin hakan a cikin jam’iyyun adawa.

Masu sharhi na siyasa na ganin wannan sauyi na iya girƙiza tsarin jam’iyyun Najeriya, tare da sake jefa haske kan yadda za a tunkari zaɓen 2027.

Da ɗumi-ɗumi: Kotu ta ba da umarnin tsare Malami, ɗansa da matarsa a gidan yari na Kuje.Wata babbar Kotun Tarayya da ke ...
30/12/2025

Da ɗumi-ɗumi: Kotu ta ba da umarnin tsare Malami, ɗansa da matarsa a gidan yari na Kuje.

Wata babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta bayar da umarnin a tsare tsohon Ministan Shari’a na Tarayya, Abubakar Malami, tare da ɗansa Abdulaziz da kuma matarsa, a gidan gyaran hali na Kuje, bisa zargin aikata manyan laifukan rashawa da s**a shafi biliyoyin naira.

Kotun ta ce an ɗauki matakin tsare su ne domin tabbatar da bin sahihin tsarin shari’a, bayan gabatar da tuhume-tuhumen da ke nuna zargin karkatar da kuɗaɗen gwamnati da kuma amfani da ofis ba bisa ƙa’ida ba.

A zaman kotun, lauyoyin gwamnati sun nemi a tsare waɗanda ake tuhuma domin kauce wa yiwuwar tserewa ko kuma katsalandan ga shaidu, yayin da ɓangaren tsaro ya tabbatar da cewa bincike kan lamarin na ci gaba da zurfi.

Ana sa ran kotun za ta ci gaba da sauraron shari’ar a kwanaki masu zuwa, yayin da al’umma ke bibiyar lamarin da hankali, ganin girman sunan waɗanda abin ya shafa da kuma nauyin zargin da ke kansu.

30/12/2025

Annabi Muhammad S.A.W 😍😍😍

30/12/2025

Allah ya mu dace 👌👌🤫

Bam ya tashi a babban asibitin KebbiRundunar ‘yansanda a jihar Kebbi ta tabbatar da afkuwar fashewar bam da sanyin safiy...
30/12/2025

Bam ya tashi a babban asibitin Kebbi

Rundunar ‘yansanda a jihar Kebbi ta tabbatar da afkuwar fashewar bam da sanyin safiyar Talata a babban asibitin Bagudo, da ke karamar hukumar Bagudo ta jihar.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da kakakin rundunar, SP Bashir Usman, ya fitar a Birnin Kebbi.

Usman ya ce: “Muna son tabbatar wa mazauna yankin cewa an shawo kan al’amuran tsaro gaba ɗaya bayan wata babbar kara ta fashewa da ta auku a babban asibitin Bagudo da sanyin safiyar Talata, 30 ga Disamba.

“Ƙungiyar tsaro ta haɗin gwiwa wadda ta ƙunshi ‘yansanda, sojoji da ‘yan sa-kai ta kulle tare da tabbatar da tsaron yankin cikin gaggawa. Ƙwararrun jami’an EOD-CBRN suna wurin suna gudanar da cikakken bincike.

“Muna farin cikin sanar da cewa babu wanda ya rasa ransa. Duk da cewa wani gini a bangaren ma’aikata ya lalace, mazauna wajen sun riga sun fice lafiya.

“Kwamishinan ‘yansanda na jihar ya ƙara tura jami’an tsaro na musamman domin tabbatar da zaman lafiya da doka.”

28/12/2025

Kwankwaso ko Abba Gida Gida ?

Address

Kano Outlying
700001

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when AHMAD MEDIA posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to AHMAD MEDIA:

Share